Search This Blog

Showing posts with label Saudiyya. Show all posts
Showing posts with label Saudiyya. Show all posts

Saturday, 13 May 2023

Yakin Sudan: Sojoji Da ’Yan Tawaye Za Su Koma Teburin Sulhu A Saudiyya


Sojoji da mayakan RSF da ke yakar juna a Sudan za su koma kan teburin sulhu ranar Lahadi bayan sun kwana suna ba-ta-kashi a Khartoum, babban birnin kasar.

Wani babban jami’in gwamnatin Sudan ya ce za su koma tattaunawar ne bayan barkewar yaki tsakaninsu duk da yarjejeniyar da suka sanya hannu na kare fararen hula da ayyukan jin kai.

Jami’in ya bayyana cewa kasar Saudiyya mai masaukin baki ta gayyaci Babban Hafsan Sojin Sudan, Janar Abdel Fattah al-Burhan zuwa babban taron kasashen Larabawa da zai gudana a birnin Jidda ranar Juma’a.

Sai dai wasu jakadun kasashen Larabawa sun bayyana cewa ba a tsammanin zuwan Janar Burhan zai halarci taron ba saboda dalilan tsaro.

An gayyaci Janar Burhan ne a matsayinsa na shugaban kwamitin rikon kasar, wanda aka dora wa alhakin tsara yadda za a mika mulki ga zababbiyar gwamnati anan gaba,

Abokin hamayyarsa kuma shugaban mayakan RSFk, Janar Mohamed Hamdan Dagalo kuma shi ne mataimakinsa a kwamitin.

Wani jakadan kasar Saudiyya ya bayyana cewa kawo yanzu dai ba a fitar da sunayen wadanda za su wakilci bangarorin a zaman ba.

Rikicin da ya barke bagatatan a watan Afrilu a Sudan ya yi ajalin kusan mutum 800, tare da tilasta wasu sama da 200,000 gudun hijira zuwa kasashe makwabta.

Majalisar Dinkin Duniya ta ce bayan haka wasu sama da 700,000 sun yi  gudun hijira zuwa wasu sassan kasar.

A ranar Alhamis Saudiyya da Amurka suka jagoranci sanya hannu kan yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin bangarorin da nufin kare fararen hula da bayar da damar ci gaba da ayyukan jin kai.

Sai dai kuma bangarorin sun ci gaba da luguden wuta a sassan birnin Khartoum, cibiyar rikicin, kafin wayewar garin Asabar.

Ana dai sa rai cewa a zaman ranar Lahadi bangarorin za su tatttauna matakan aiwatar da yarjejeniyarsu ta ranar Alhamis kan yadda za a kare fararen hula da ma’aikatan agaji da kuma janye sojoji daga yankunan fararen hula.

Za kuma a tattauna yadda za a kawo karshen rikicin, wanda zai kai ga kafa sabuwar gwamnatin farar hula a Sudan.

Bisa abin da aka saba gani, babu wani daga cikin bangarorin da ke nuna alamar sassauci, inda suke ta gwabza fada, duk da cewa sun yi yarjejeniyar tsagaita wuta.

Sai dai kawo yaznu, RSF ta yi alkawarin mutunta yarjeniyar ranar Alhamis, amma har yanzu bagaren sojojin kasar bai ce uffan ba.

AMINIYA

Thursday, 4 May 2023

Saudiyya Ta Yi Wa Messi Tayin Ninkin Albashin Ronaldo

 


Kungiyoyin kwallon kafa a kasar Saudiyya na zawarcin gwarzon dan wasan duniya, Lionel Messi, na kungiyar PSG, da tayin albashin da ya zarce na kowane dan wasa a duniya.

Rahotanni sun nuna cewa wata kungiya da ke zawarcin Messi a Saudiyya ta yi masa tayin albashin Naira biliyan 183.5 (Dala miliyan 400) a shekara, idan kwantaraginsa ya kare da PSG a wata mai zuwa.

Kafar labarai ta Telegraph ta kasar Birtaniya ta ce dan wasan ya fara tunanin duba tayin kuma tuni kungiyar ta fara tattaunawa da Kyaftin din na kasar Argentina kan kwangilar da take masa tayi, bayan dakatarwar da PSG ta yi masa.

Idan hakan ta tabbata, Messi zai rika karbar kusan ninki biyun albashin babban abokin hamayarsa Cristiano Ronaldo, wanda a halin yanzu Al Nassr ta kasar Saudiyya ke biyan sa Naira biliyan 96.3 Dala miliyan 210 a shekara, zuwa 2025.

Wannan sabuwar ta taso ne bayan da kungiyar PSG ta dakatar da Messi na tsawon mako biyu ba tare da albashi ba, saboda wata ziyara da ya kai Saudiyya ba da izinin kungiyar ba.

A baya dai an yi ta rade-radin kungiyar Al Hilal ta Saudiyya ce ke neman daukar Messi, daga baya da PSG ta takatar da shi kuma maganar ta kara tasowa.

AMINIYA

Thursday, 27 April 2023

Saudiyya Ta Kwashe ’Yan Najeriya Da Suka Makale A Sudan Zuwa Kasarta


Gwamnatin kasar Saudiyya ta kwashe wasu daga cikin ’yan Najeriya da suka makale a yakin da ya barke a Sudan zuwa kasarta.

Minista a Ma’aikatar Harkokin Waje ta Najeriya, Zubairu Dada, ya ce Saudiyya ta tura jiragen ruwa da suka kwashe ’yan Najeriya zuwa birnin Jeddah na kasarta, bayan barkewar yaki a Sudan.

Ma’aikatar ta ce daga bisani za a maido da ’yan Najeriyan da aka kai Saudiyya gida, kuma gwamnatin Tarayya na kokarin ganin cewa babu dan Najeriya ko daya da ya rage a Sudan kafin cikar wa’adin awa 72 da bangarorin da ke yaki da juna suka bayar na tsagaita wuta.

Ta bayyana cewa a kokarinta na kwashe ’yan Najeriya da suka makale bayan barkewar yakin, Gwamnatin Tarayya ta kashe Naira miliya 552 kan daukar hayar motocin da za su fitar da su zuwa iyakar Sudan da kasar Masar.

Ministan Harkokin Waje na Najeriya, Geoffrey Onyema, ya ce an dauki hayar bas-bas 40 da za su kwashi ’yan Najeriya daga Khartoum, babban birnin Sudan zuwa iyakar kasar Masar da ke Aswan, inda za su hau jirgi zuwa gida.

“Dala miliyan 1.2 (Naira miliyan 552) aka caje mu kan bas 40 da muka nema; Mun samu bas guda 40 na alfarma da za su dauki ’yan Najeriya (daga Khartoum) zuwa iyakar kasar Masar.

“Sanin kowa ne cewa tabbas irin wannan yanayi akwai wadanda za su yi amfnai da rikicin Sudan wajen tatsar jama’a,” in ji Oyema.

Ya bayyana cewa Gwamnatin Tarayya na yin dukkan mai yiwuwa wajen ganin an gama kwashe ’yan Najeriya cikin sa’a 72 da gwamnatin Sudan ta bayar na tsagaita wuta.

“Ba mu da matsala da wa’adain awa 72 da gwamnatin ta bayar kuma mun tattauna da bangarorin da abin ya shafa, kuma sun ba mu hadin kai,” in ji shi.

Ya ci gaba da cewa “Za a kwashe ’yan Najeriya ne a rukuni-rukuni domin tabbatar da tsaron lafiyarsu; kuma Alhamdulillah babu dan Najeriya ko daya da ya rasa ransa.

AMINIYA

Thursday, 20 April 2023

Labari Da Dumiduminsa: An Wa Watan Sallah A Saudiyya

 


Hukumomin Saudiyya sun sanar da ganin watan Shawwal na sallah a ranar Alhamis 20 ga watan Afrilun 2023.

An ga watan ne a yankin Tumair na Saudiyya kamar yadda kwamitin duban wata na yankin ya bayyana, hakan na nufin Saudiyya ta kammala azumin Ramadan 29.

Gobe Juma'a 21 ga watan Afrilu zai zama 1 ga watan Shawwal.

Friday, 13 January 2023

Najeriya Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Gudanar Da Aikin Hajjin Bana Da Saudiyya



 Najeriya ta samu nasarar yin taro da hukumomin aikin hajji na Saudiyya, inda aka sanya hannu kan yarjejeniyar gudanar da aikin hajjin bana.

Karamin ministan wajen Najeriya Ambasada Zubairu Dada ne ya jagoranci tawagar Najeriya wajen kulla wannan yarjejeniya da ke zama ka’idar amincewa kowace kasa ta kawo alhazai.

Rattaba hannu kan yarjejeniyar ya biyo bayan wata ganawa ta yanar gizo tsakanin shugaban hukumar Alhazan Zikrullah Kunle Hassan da hukumomin aikin hajji na Saudiyya a watan Disambar bara.

Kwamishinan ma’aikata da tsara manufofi na hukumar Alhazan Nura Hassan Yakasai wanda ke cikin tawagar ya bayyana cewa Saudiyya ta amince da dawowa da Najeriya yawan kujeru na asali da ta ke samu mutum dubu 95.




Hakanan Yakasai ya ce a yanzu ba dogon bincike kan cutar korona bairos matukar maniyyaci ya na da shaidar gwajin cutar.

Malamai sun shiga fadakar da maniyyata don kara fahimtar dokokin aikin da zummar samun ladan wankuwa daga zanubai.

Shugaban JIBWIS Sheikh Abdullahi Bala Lau ya bukaci kara karfafa koyar da maniyyatan aikin daga Najeriya har zuwa Makkah da Madina.


A shekarun baya ‘yan Najeriya kan saye dukkan kujerun aikin hajji har ma a saura da bukatar masu son zuwa, amma gabanin bullar annoba an samu kujerun da su ka yi kwantai don rashin karfin arzikin jama’a ko wadatar abun hannu da ya kara ta’azzara daga rage daukar nauyin lamuran hajji da gwamnatoci su ka yi.

Thursday, 5 January 2023

Mutum miliyan bakwai ne suka yi aikin Umarah a shekarar 2022- Saudia

Ma’aikatar Aikin Hajji da Umarah ta kasar Saudiyya ta ce kimanin mutum miliyan bakwai ne suka yi aikin Umarah a shekarar 2022.

Jaridar Aminiya ta rawaito cewa wannan adadin a cewar ma’aikatar ya hada da baki su miliyan hudun da suka samu izinin shiga kasar domin Hajjin Umarah.

Kamfanin dillancin labarai na SPA ya rawaito a ranar Alhamis cewar, Ma’aikatar ta yi amfani da harsuna 14 wajen isar da muhiman bayanai da suka shafi addini da kiwon lafiya da sauransu ga maniyyatan yayin zamansu a kasar.

Kazalika, ta ce ta tabbatar da maniyyatan sun samu kulawar da ta dace wajen gudanar da harkokinsu da suka hada yanka da ziyartar wurare da sauransu.

Ta kara da cewa, ta sahale wa masu rike da biza daban-daban ibadar Umarah a wannan shekarar.

Ta ce a 2022 ne ta kyale masu bizar yawon shakatawa suka yi Umarah yayin zamansu a kasar, wanda hakan shi ne karon farko da irin hakan ta faru.


Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

SAPZ Kano partners ABCOAD to organize FFS Training for Youth and Women.

The Special Agro-Industrial Processing Zones (SAPZ) Programme, Kano State, in collaboration with Audu Bako College of Agricultur...