Posts

Showing posts with the label 'Yan Kasuwa

Tsadar Kayan Abinci: Hukumar Yaki Da Cin Hanci Ta Kano Za Ta Fara Kama Dukkanin Wadanda Ta Samu Suna Boye Kayan Abinci

Image
Shugaban Hukumar, Barrister Muhuyi Magaji Rimin Gado, ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis, yayin da yake yi wa manema labarai jawabi a ofishinsa Muhuyi Magaji ya ce " ..a dokar jahar Kano, boye kayan abinci haramun ne" don haka zamu dauki matakin da ya dace kan masu aikata hakan. Shugaban Hukumar ya ci gaba da cewa duk da cewar Gwamna Abba Kabir Yusuf ya gudanar da zama na musammam tare da manyan 'yan kasuwa, Amma yace hakan na zai hana ofishinsa nasa yin abun da ya dace ba, kasancewar daman hukumar na karkashin Ofishin Gwamnan ne. "Mun yi wani aiki a baya wanda al'uma suka ji dadin shi, don haka mun karbi kiraye - kiraye ta hanyoyin sadarwa, wasu sun tako kafa da kafa su kira su ce wai abubuwan da muka yi a baya me yasa yanzu ba ma yi, to shi ne na ja hankali cewa kowanne abu ya na zuwa ne da nasa matsalar, wancan lokacin matsalar ta faru ne lokacin zaman gida sanadiyyar cutar Coronation.." Batista Muhuyi ya kara da cewa wancan yanayi ya haifar

Tsadar Rayuwa: Gwamna Abba Kabir Yusuf Ya Gana Da 'Yan Kasuwar Kano

Image
Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya roki ‘yan kasuwa da su nuna tausayi da jin kai ga al’ummar jihar. Gwamnan ya yi wannan roko ne a wata tattaunawa da ‘yan kasuwar jihar, da nufin samar da hanyoyin magance hauhawar farashin kayayyaki. A cikin sanarwar da Darakta yada labarai da hulda da jama'a na Gwamna, Sunusi Bature Dawakin Tofa ya sanyawa hannu, yace Yusuf ya nuna matukar damuwarsa kan halin da al’ummar kasar ke ciki sakamakon hauhawar farashin kayayyaki da ake ci gaba da yi, inda ya ce da yawa ba sa iya cin abinci sau uku a rana. Ya koka da cewa za a iya rage tsadar kayan masarufi, da tsarin tsarin mulki ya yi tasiri, idan har ’yan kasuwa suka kiyaye dabi’u da dabi’u, yana mai jaddada bukatar hada karfi da karfe don shawo kan lamarin. Duk da hauhawar farashin Dala, gwamnan ya yi imanin cewa matakan gyara za su iya saukaka lamarin sosai. Gwamna Yusuf ya jaddada alhakin da ya rataya a wuyan jihar na ganin jama’a sun ji dadin zama tare da bayyana

Muna Asarar N13bn Duk Mako Saboda Rufe Iyakar Najeriya Da Nijar – ’Yan Kasuwa

Image
’Yan kasuwar Arewacin Najeriya sun koka da cewa suna tafka asarar sama da Naira biliyan 13 duk mako saboda rufe iyakokin Najeriya da Nijar sanadiyyar rikicin kasar. A ranar 4 ga watan Agusta, Shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya ba hukumar Kwastam umarnin rufe dukkan iyakokin kasar da Jamhuriyar Nijar. Iyakokin sun hada da ta Jibiya da ke Jihar Katsina da ta Illelah a Jihar Sakkwato da kuma ta Maigatari a Jihar Jigawa. Da yake jawabi ga manema labarai a Abuja ranar Lahadi, Shugaban kungiyar ’yan kasuwa na Arewacin Najeriya, Ibrahim Yahaya Dandakata, ya ce matakan da aka dauka sun jefa su cikin tsaka mai wuya. Sai dai ya yi kira ga Gwamnatin Najeriya da ta taimaka ta bude iyakar Maje-Illo da ke Jihar Kebbi, domin ta ba su damar shigo da kayayyaki cikin kasa. A cewarsa, “Tun bayan umarni Shugaban Kasa kan rufe dukkan iyakokin Najeriya da Nijar sakamakon juyin mulkin da aka yi a can, muke cikin tsaka mai wuya. ’Yan kasuwar Arewa na tafka asar Naira biliyan 13 kowanne mako. “Galib

Buhari Ya Je Maiduguri Domin Jajantawa 'Yan Kasuwar Monday Market

Image
Shugaban Kasa Muhamamdu Buhari ya isa Jihar Borno, domin jajanta wa ’yan kasuwar da iftila’in gobora ta shafa a Kasuwar Monday da ke Maiduguri. An wayi gari ranar Lahadi a Maiduguri da gobarar, wadda ta lakume dubban shaguna a kasuwar, wadda ita ce mafi girma a Jihar Borno da ma yankin Arewa maso Gabashin Najeriya. ’Yan sanda na ci gaba da tsare Ali Madaki kan daukar bindiga a yakin neman zabe Ana sa ran a yayin ziyarar ta ranar Alhamis, Buhari zai je Fadar Shehun Borno, inda zai jajanta wa ’yan kasuwar da suka yi asarar dukiyoyinsu a gobarar ta ranar Lahadi. Shugaban kasar zai kuma kaddamar wa wasu ayyuka da suka hada da rukunin gidajen da Gwamna Babagana Zulum ya gina da wasu tituna a garin Maiduguri. Sauran su ne Cibiyar Kula da Masu Cutar Kansa a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Maiduguri da kuma Tashar Iskar Gas ta kamfanin NNPC.