Posts

Showing posts with the label Tallafi

Shugaban NAHCON Ya Yabawa Gwamnan Imo Bisa Tallafawa Maniyyatan Jahar

Image
Hukumar alhazai ta kasa NAHCON a yau ta karbi bakuncin gwamnan jihar Imo, Hope Uzodinma, wanda ya kai ziyarar ban girma a gidan alhazai dake Abuja. A sanarwar da mataimakin daraktan yada labarai na hukumar, Mousa Ubandawaki ya sanyawa hannu, yace A jawabinsa na maraba, Malam Jalal Ahmad Arabi ya bayyana jin dadinsa da karbar bakuncin Gwamnan Jihar Imo a gidan Hajji. Arabi ya bayyana Gwamna Uzodinma a matsayin wani ginshikin tallafi ga Hukumar tare da bayyana yadda ya yi kokarin ganin alhazan jihar sa da ke da niyyar shiga aikin Hajjin bana. A cewarsa, “Kun kasance ginshikin goyon bayanmu a Hukumar ta hanyar goyon bayanku na ganin cewa Musulmin Jihar Imo sun samu damar shiga aikin Hajji. Kun tallafa mana a 2023 da ma bana duk da kasancewar kiristanci ne kuma jihar Imo jihar ce mafi rinjayen Kirista. A gare mu ku alama ce ta zaman lafiya tare da addini da hadin kai a kasar." Ya kuma baiwa Gwamna Hope Uzodinma takardar yabo da lambar yabo ta 🥈 f nagari bisa goyon bayansa

Shugaban Majalisar Dokoki Ta Katsina Ya Raba Tallafin Naira Miliyan 35

Image
Kakakin Majalissar Dokoki ta Jihar Katsina, Nasir Yahaya, ya bayar da tallafin Naira Million Talatin da HuÉ—u da Dubu ÆŠari Tara da Hamsin. (34,950,000) ga Mutum Dubu Ukku (3000) a filin wasan Ƙwallon Kafa dake Daura Hadimin tsohon Shugaban Najeriya, Buhari Sallau, ya rawaito a shafinsa na Facebook cewa, an bayar da Tallafin ga Marayu, Limamai, Zawarawa, Masu Ƙananan Sana'oi, Exco, Mata, Matasa, Students, yan Media, Dagattai, MabuÆ™ata, yan siyasa, Ƙungiyar Teloli, Ƙungiyar Masu Shayi da Masu chajin waya, da sauran su. Inda ko wanne daga cikinsu zai amfana da Tallafin, Naira Dubu Goma (10,000) Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Radda PhD, yayi Jin-Jina gami da fatan Alkhairi ga Kakakin Majalissar akan wannan abin Alkhairi da yayi, sannan yayi roÆ™o gami da Jan hankali ga wanda suka amfana da wannan Tallafin da suyi amfani dashi ta hanyar daya dace, domin su bunÆ™asa Kasuwar su.  Haka kuma Mataimakin Shugaban Jam'iyyar APC na Jihar, Alh. Bala Abu Musawa, ya taya mutanen D

Gwamnan Kano Zai Kaddamar da Kashi Na Biyu Na Tallafin Abinci

Image
Gwamnatin jihar Kano karkashin jagorancin gwamna Abba Kabir Yusuf na shirin raba buhunan hatsi da kuma baiwa matasa da mata da nakasassu tallafin kudi. A sanarwar da babban sakataren yada labaran Gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya sanyawa hannu, ya ce, a ci gaba da kokarin gwamnatinsa na bayar da tallafi ga al’ummar jihar domin rage radadin tallafin man fetur, an kammala shirye-shiryen rabon hatsin da suka hada da shinkafa da masara a yankuna 484 dake cikin kananan hukumomi 44 na jihar. Gwamna Alh Abba Kabir Yusuf ya bayyana haka a yau a wajen wani taro da shugabannin kananan hukumomin jiha da na kananan hukumomi/Secretries na hudu grassroot Mobilisation platforms (Community Re-Orientation Committee (CRC), Lafiya Jari, Kano PRO-PA da kuma Kwankwasiyya) taron da ya gudana. wanda aka gudanar a dakin taro na Coronation, gidan gwamnatin Kano. Gwamnan ya ce rabon kaso na biyu ya zama wajibi duba da irin matsalolin da mutane ke ciki sannan ya yi kira ga ayyukan rabar a mataki

Tinubu Ya Ba Da Umarnin Bai Wa ’Yan Najeriya Tallafi

Image
  Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya ba da umarnin bayar da tallafi domin rage wa ’yan Najeriya domin rage musu radadin cire tallafin mai da Gwamnatin Tarayya ta yi. Shugaban Kamfanin Mai na Kasa (NNPCL) Mele Kyari ne ya sanar da haka, yana mai cewa biyan tallafin mai da gwamnati ke yi ya zama tarihi, hasali ma ba a ware masa ko sisi ba a kasafin kudi. Da yake bayani bayan ganawarsa da jagororin jam’iyyar APC mai mulki, Kyari ya ce a halin yanzu ma NNPC na bin gwamnati bashin Naira tiriliyan 2.8 da ya kashe wajen biyan tallafin man, don haka kamfanin ba zai iya ci gaba da biya ba. “Har yanzu gwamnati ta kasa biyan Naira 2.8 da muke bin ta, wanda ya isa hujja cewa gwamnati ba za ta iya ci gaba da biyan tallafin man ba,” in ji Kyari. Ya bayyana cewa babu wanda zai ba da bashi ga wanda ake bi bashin Naira tiriliyyan 2.8, don haka, kamfanin NNPCL ba zai iya kara biyan tallafin a madadin gwamnati ba. Hasali ma kudin da NNPC ke kashewa wajen biyan tallafin na hana shi sauke nauyin da ya rata

Akwai yiwuwar a soma cire tallafin fetur a watan Afrilu - Gwamnatin Najeriya

Image
  Akwai yiwuwar gwamnatin tarayyar Najeriya ta soma cire tallafin man fetur daga Afrilun 2023, wato watanni uku kafin yadda ainahin lokacin da aka yi niyyar cire tallafin a baya. Ministar kuÉ—i da kasafi Zainab Ahmed ce ta bayyana haka a wata hira ta musamman da ta yi da gidan talabijin na Arise a yayin wani taro na tattalin arzikin duniya a Switzerland. "Abin da ya fi shi ne wannan gwamnatin watakila ta soma cire tallafi a farkon zango na biyu na wannan shekara saboda zai fi nagarta idan aka cire a hankali a maimakon a jira a cire shi baki É—aya," in ji ministar. Ta bayyana cewa duka Æ´an takarar shugaban Æ™asar Najeriya a lokutan yaÆ™in neman zaÉ“ensu duk suna da ra'ayin cire wannan tallafin Bayan Æ™ara wa'adin watanni 18, gwamnatin tarayya ta shirya kashe naira tiriliyan 3.35 kan tallafin mai daga Janairu zuwa Yunin 2023. Wannan Æ™arin wa'adin da aka yi ya janyo muhawara matuÆ™a kan irin kuÉ—in da za a kashe sakamakon ana ganin cewa zai Æ™ara giÉ“i a kasafin kuÉ—i wanda kum

Abdulmumin Jibrin Kofa ya raba tallafin naira miliyan hamsin ga al'umar Kiru da Bebeji

Image
  A ranar lahadi ne dan takarar majalissar tarayya a kananan hukumomin Kiru/Bebeji a jam'iyyarNNPPHon Abdulmumin Jibrin Kofa PhD,(Jarman Bebeji) ya gwanjage mutanen yankinsa da jari/tallafin kudade inda wasu suka rabauta da Dubu dari biyu(#200,000), Dubu dari daya(#100,000), Dubu Hamsin(#50,000), Dubu Ashirin(#20,000), Dubu Goma(#10,000) da kuma Dubu Biyar(#5,000). Mutanen da suka amfana da wannan jari/tallafi sun hada da wakilan akwatuna, Exco na karamar hukuma da mazabu na Jam'iyyar NNPP da PDP na Kiru/Bebeji, KOKAS na Kiru/Bebeji, Wasu kungiyoyi masu karfi na mata da matasa a Kiru/Bebeji, Dagatan Kiru/Bebeji, Limaman Juma'a Kiru/Bebeji, Malaman Kwankwasiyya Kiru/Bebeji, Dalibai, Yan Social Media, Mafarauta, Yan Achaba, Mahauta da kuma mutane masu bukata ta musamman. Wannan taro ya sami halartar yan takarkaru na Kiru/Bebeji, manyan jagorori tare da  shuwagabannin jam'iyyar NNPP/PDP na Kiru/Bebeji.