Akwai Yiwuwar Matsalar Tsaro Ta Kawo Wa Zaben 2023 Tangarda – INEC



Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ta yi gargadin cewa matsalar tsaron da ake fama da ita a wasu sassan Najeriya za ta iya sa wa a soke babban zaben 2023 da za a fara a watan gobe.

Shugaban hukumar, Farfesa Mahmud Yakubu, wanda Shugaban Cibiyar Bincike Kan



Harkokin Zabe (BEI), Farfesa Abdullahi Abdu Zuru ya wakilta ne ya yi gargadin ranar Litinin a Abuja.

Ya bayyana hakan ne yayin wani taron ba da horo kan shirye-shiryen tsaro a lokacin zaben.

Hukumar ta ce matsalar na iya sa wa a gaza gudanar da zaben a mazabu da dama, ta yadda zai yi wahala a iya bayyana wanda ya lashe shi, wanda ta ce hakan zai haifar da rudani a tsarin mulkin Najeriya.

Popular posts from this blog

Yanzu - Yanzu: Bankuna Zasu Karbi Tsofaffin Kudi Ko da Bayan Karewar Wa'adi - Emefiele

Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki