Search This Blog

Tuesday, 28 February 2023

Nasarar Tinubu Ta Yi Nuni Da Yadda Dimokwaradiyya Ta Yi Aikinta - Ganduje

Gwamna Ganduje ya bayyana Nasarar dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a zaben 2023, a matsayin shugaban kasa a Najeriya, ta nuna yadda aka yi dimokaradiyya ta gaskiya. 

A wani martani ga nasarar da Tinubu ya samu, Gwamna Ganduje ya yaba da gwagwarmayar siyasa da jajircewar daular siyasar Tinubu, wadda ta samar da wasu abubuwa daga ko’ina a fadin kasar nan, wajen tabbatar da cewa dan takarar shugaban kasa ya yi nasara baki daya.

“Sahihancin jarin Asiwaju Bola Ahmed Tinubu a kan ɗan adam, ci gaban ƙasa da haɗin kan ƙasa ya taka muhimmiyar rawa wajen fifita shi ga dukkan sassan ƙasar,” in ji shi.

Ya kara da cewa, “Yakin da Tinubu ya kwashe shekaru da dama yana yi na maido da mulkin dimokuradiyya a kasar nan, ‘yan Najeriya sun fahimta sosai. Don haka, muna ganin hikima da kuma dalili mai kyau na jinginar da makomarmu gare shi.”

Yayin da yake tabbatar da cewa, zababben shugaban kasar zai bullo da dabarun tunkarar matsalolin da suka addabi al’ummar kasar nan, Gwamna Ganduje ya yabawa shugabannin jam’iyyar da mambobin jam’iyyar da suka tsaya tsayin daka har zuwa wannan lokaci.

Tinubu, a cewar Ganduje, “Mai ƙwazo ne mai dabara, maginin mutum da sararin samaniya, ƙwararren shugaba na siyasa, shugaba mai yada al’umma, mai jurewa da tabbatar da dimokuradiyya mai dorewa da ci gaba kuma ƙwararren mai motsawa.”

Da wadannan abubuwan da suka gabata da ma wasu da dama da suka yi tasiri wajen ganin wanda ya lashe zaben shugaban kasa, Gwamna Ganduje ya kara bayyana cewa, “Tare da zababben shugaban kasarmu, Tinubu, ya jagoranci dimokuradiyya mafi girma a Afirka, tabbas nahiyarmu za ta ci gajiyar dimbin kwarewa. domin ci gaban nahiyar.

"Nasarar da Tinubu ya samu ba wai kawai kasarmu ta uwa ta Najeriya za ta amfana ba, zai kuma zama wani kwarin gwiwa ga Afirka, a matsayinta na nahiya da kuma aiwatar da tsarin dimokuradiyya a duniya," in ji shi.

Labari da dumiduminsa : INEC Ta Bayyana Bola Tinubu A Matsayin Wanda Ya Lashe Zaben Shugaban Kasa

An ayyana Bola Tinubu, dan takarar jam’iyyar All Progressives Congress (APC), a matsayin wanda ya lashe zaben shugaban kasa.

Shugaban Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), Mahmood Yakubu ne ya sanar da sakamakon zaben a safiyar yau Laraba.


Yakubu ya ce Tinubu ya samu kuri’u 8,794,726.


Atiku Abubakar na jam’iyyar PDP ne ya samu kuri’u 6,984,520, yayin da Peter Obi na jam’iyyar Labour Party (LP) ya zo na biyu da kuri’u 6,101,533.

"Yanzu na sauke nauyin da ya rataya a wuyana a matsayina na babban jami'in dawo da na kasa," in ji shugaban INEC.


“Ni, Farfesa Mahmood Yakubu, a nan na tabbatar da cewa ni ne jami’in da zai dawo takara a zaben 2023. An fafata zaben.

“Wannan Tinubu Bola Ahmed na jam’iyyar APC, bayan ya tabbatar da ka’idojin doka, an bayyana shi a matsayin wanda ya yi nasara kuma an dawo da shi.

Yakubu ya kara da cewa za a bayar da takardar shaidar komawa ga Tinubu da karfe 3 na yammacin Laraba.

Hukumar DSS Ta Kama Alasan Ado Doguwa

Hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) ta kama shugaban masu rinjaye na majalisar wakilai Alhassan Dogowa, saboda zargin kisan wasu magoya bayan jam’iyyar adawa a yankin.

 Majiyarmu ta rawaito cewa an kama Doguwa ne a filin jirgin sama na Malam Aminu Kano , a kan hanyarsa ta zuwa kasar Saudiyya domin gudanar da aikin umarah a ranar talata.

 Kamen ba zai rasa nasaba da kisan da aka yi wa magoya bayan ‘yan adawa kusan 15 a karamar hukumar Tudunwada a lokacin zaben da aka kammala ba .

 Rahotanni sun ce an kulle wasu daga cikin mutane a wani gini inda aka kona su kurmus, lamarin da ya sa aka gagara kubutar
Kadaura24 

Friday, 24 February 2023

APC Ta Bukaci A Gudanar Da Bincike Kan Rikicin Siyasa Da Ya Barke A Kano

Kwamitin yakin neman zaben dan takarar gwamnan Jihar Kano a jam’iyyar APC, ya bukaci ‘yan sanda da su binciki fadan bangar siyasa da barnar da aka yi a Karamar Hukumar Kumbosto a ranar Alhamis.

Mataimakin kakakin kwamitin, Alhaji Garba Yusuf ne ya yi wannan kiran a wani taron manema labarai ranar Alhamis a Kano.


Kwamitin ya yi watsi da zargin cewa akwai hannun magoya bayan jam’iyyar APC a rikicin, inda ya ce ya kamata ‘yan sanda su binciki lamarin tare da gurfanar da masu hannu a tashin-tashinar.

“Duk wadanda ke da hannu aa harin da aka kai wa mazauna yankin za a gurfanar da su gaban kotu



A ranar Alhamis dai Hukumar Tsaron Farin Kaya (NSCDC), ta tabbatar da cafke mutum 55 da ake zargi biyo bayan harin da wasu ‘yan daba suka kai kan wasu mutane tare da lalata motoci a kan hanyar Zariya.
Ana zargin magoya bayan APC da na NNPP sun yi arangama da juna, lamarin da ya yi sanadin jikkatar wasu tare da salwantar dukiyoyi.

Thursday, 23 February 2023

Yau Ake Rufe Yakin Neman Zaben Shugaban Kasa

 


Daga karfe 12 na daren yau Alhamis 23 ga Fabrairu, 2023, za a fure yakin neman zaben ’yan takarar shugaban kasa da Majalisun Tarayya da za a gudanar ranar Asabar.

Dokar Zaben Najeriya ta haramta yin duk wani nau’in yakin neman zabe ko tallata dan takara daga sa’a 24 kafin ranar zabe.

A yayin rubuta wannan rahoton, kusan awa 12 ya rage wa daukacin jam’iyyu da ’yan takara su yi duk abin da za su iya, su kuma rufe yakin neman zabensu, sannan a fafata a akwatunan zabe a ranar Asabar.

Jam’iyyu 18 ne ke zawarcin kujerar shugaban kasa bayan kammala wa’adin Shugaba Muhammadu Buhari na biyu a ranar 29 ga watan Mayu.

Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ta bayyana cewa za a gudanar da zabukan ne a mazabu 1,491 da ke kananan hukumomi 774 da ke jimillar rumufunan zabe 176, 846.

’Yan Najeriya ne za su yi alkalanci a zaben mai mutum miliyan 95.5 da suka yanki katin zabe, wadanda akasarinsu matasa ne, masu shekara 18 zuwa 35, ko da yake kawo yanzu babu alkaluman adadin wadanda suka karbi katin zabensu.

Manyan jam’iyyu

Jam’iyyar APC mai mulki kasar tun 2015 na neman ci gaba da jan ragamar kasar na karin shekara hudu, a yayin da babbar jam’iyyar adawa ta PDP wadda ta mulki kasar na tsawon shekara 16, bayan dawowar tsarin dimokuradiyya daga 1999 zuwa 2015 na neman sake dawowa.

Bugu da kari, zaben na bana ya zo da sabon abu, inda ake da wasu kananan jam’iyyu biyu, LP da kuma NNPP da suke tashe da kuma samun magoya baya a wannan karon.

Batun shekarun ’yan takara dai ya dade yana tayar da kura a zabukan Najeriya, inda gabanin zaben 2019 Gwamnatin Tarayya ta yi dokar rage yawan shekarun tsayawa takara domin a dama da matasan kasa.

APC ta tsayar da tsohon Gwamnan Jihar Legas (1999-2007) kuma Uban Jam’iyyar na kasa, Asiwaju Bol Ahmed Tinubu, a yayin da PDP ta tsayar da Fsohon Mataimkin Shugaban Kasa Atiku Abubakar (1999-2007).

Karo na biyar ke nan Atiku yake neman zama shugaban kasa a yayin da Tinubu ke tutiyar cewa shi ya fi kowa dacewa ya mulki kasar a wannan karon bayan Buhari.

A nasa bangaren, yana takama da matasa, kasancewarsa mai karancin shekaru a cikin manyan ’yan takara.

Hakazalika, dan takarar NNPP, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso yana takama da kasancewa mai jini a jika yana kuma bugun gaba da irin ayyukan da ya yi a lokacin da yake Gwamnan Jihar Kano, ministan tsaro.

Yana kuma takama da farin jininsa, inda a 2015 ya zama na biyu a zaben dan takarar shugaban kasa na APC, wanda Buhari ya lashe.

Zaben na zuwa ne a yayin da Najeriya ke tsaka da fama da matsalar tattalin arziki bayan Gwamnatin APC ta yi sauyin takardun Naira 200, N500 da kuma N1,000.

Sauran abubuwan da ke ci wa kasar tuwo a kwarya sun hada da sha’anin tsaro, tsadar man fetur da rashin ingantattun ababen more rayuwa da suka hada da bangaren ilimi, lafiya, sufuri, da kuma uwa uba makamshi da wutar lantarki.

Tuesday, 21 February 2023

INEC Ta Gargadi Masu Sanya Idanu Kan Zaben Najeriya

Hukumar Zaɓen Najeriya, INEC, ta gargaɗi masu aikin sa ido kan yadda zaɓukan ƙasar za su gudana su kiyaye da dokoki da ƙa'idojin ƙasar sannan su guji katsa-landan a abin da ba su da hurumi a kai.

INEC ta yi gargaɗin ne a lokacin da ta gudanar da taron ƙarin haske game da dokokin aikin sa idon da bayar da bayanai ga masu aikin na cikin gida da kuma na waje a Abuja, ranar Talatar nan.

Tuni dubban masu sa idon suka hallara a ƙasar domin duba yadda zaɓukan - da za a fara ranar Asabar 25 ga watan nan na Fabarairu - za su gudana, inda za a fara da na shugaban ƙasa da na 'yan majalisun dokoki na tarayya.

Sai kuma ranar 11 ga watan Maris inda za a yi zaɓukan gwamnoni da 'yan majalisun dokoki na jihohi

Dubban masu sanya idanu daga ƙungoyoyi daban-daban na ciki da wajen Najeriya ne suka saurari bayanai daga manyan jami'ai na hukumar zaɓen da suka haɗa da shugaban hukumar Farfesa Mahmood Yakubu da sauran muƙarraban hukumar game da yadda kowa zai taka rawar da ta dace ba tare da wuce gona da iri ba a kan zaɓukan.

Farfesa Sani Adam wanda kwamishina ne a hukumar zaɓen ta Najeriya ya yi wa BBC ƙarin bayani a kan gargaɗin da suka yi wa masu aikin sa idon, inda ya ce suna so jami'an su kasance mutane masu adalci ba kuma 'yan leƙen asiri ƙasa ba.

Farfesan ya ce suna son su kasance sun dubi abin da ake yi kuma su tabbatar duk ƙa'idojin da aka gindaya musu sun kiyaye da su, sannan a bi zaɓen kamar yadda ake ba tare da an samu tashin hankali ba

Kwamishinan ya ce suna so masu sa idon, su kasance sun bayar da bayani kan abubuwan da suka gani na gaskiya sannan su kasance masu bin dokokin Najeriya da kuma zaɓen.

Bayan wannan kuma kar su yi katsa-landan a ciki, kar su shiga harkar da ba ta shafe su ba.

Jami'in ya ce, ''masu aikin suna da damar bayar da bayanin duk abin da suka gani su tabbatar haka ne.''

Ya ce, ''akwai dokoki waɗanda suka ba masu aikin sa idon, '' mun ƙarfafa gaya masu cewa Najeriya ƙasa ce mai zaman kanta ba ƙasa ba ce da za su zo su yi mata katsa-landan,'' in ji shi.

''Amma su yi aikinsu yadda ake so kuma su yi aiki ne don su taimaka mana wajen ƙara gyara yadda ake zaɓe a Najeriya,'' a cewarsa.

Shi kuwa Salisu Musa mai sa ido daga ƙungiyar 'Country International Human Right Movement', ya gaya wa BBC cewa a matsayinsu na masu sa ido na waje ''dole mu ɗauki ƙa'idojin da suka bayar.

''Amma akwai abubuwan da INEC suka faɗa kusan za mu saurare su mu ji'', in shi ji.

''Amma za mu saka ido duk abin da muka ga ya yi ba daidai ba za mu sa shi a cikin rahoto don kowa ya same shi,'' in ji shi.

Musa ya ce, ''ka san daman kusan ita wannan observers kamar ba ta shiri da INEC saboda abin da ake gani sun zo don su bi ƙwaƙwaf kan me ke faruwa,''

''Ka san ba za ka so ya zamanto ya yi maka babakere a gida ba,'' in ji mai sa idon.

''Ita maganar wannan katsa-landan suna nufin dole mu bi a hankali tun da dukkanmu ƙungiyar da ta zo wajen aikin nan dole muna da tsare-tsarenmu, kuma za mu tabbatar namu bai ƙetare na hukumar zaɓen ba,'' in ji shi.

Shugaban hukumar zaɓen ta Najeriya Farfesa Mahmood Yakubu ya ce wannan zaɓe shi ne wanda ya fi samun masu sa ido na ciki da na waje a tarihin zaɓen Najeriya.
BBC 

Bankin CBN Ya ce Har Yau Yana Nan Kan Bin Umarnin Shugaba Buhari Na Ci Gaba Da Amafani Da Tsofaffin Kudi Na 200 Kadai

Monday, 20 February 2023

APC Ta Bukaci Buhari Ya Mutunta Umarnin Kotun Koli Kan Wa’adin Tsofaffin Kudi


Kwamitin Gudanarwar APC na kasa ya bukaci Shugaba Muhammadu Buhari da ya martaba hukuncin da Kotun Koli ta yanke kan batun daina amfani da tsofaffin takardun kudi.

Wannan kira dai na zuwa ne yayin wani taro da gwamnonin jam’iyyar da shugabanta na kasa, Sanata Abdullahi Adamu suka gudanar ranar Lahadi a Abuja.

NAJERIYA A YAU: Shin don talakawa gwamnoni ke adawa da canjin kudi?
Tsohon Shugaban PDP a Kano ya sauya sheka zuwa NNPP
A taron wanda aka shafe tsawon sa’a biya ana tattaunawa, ya kara nuna yadda APC ta tsunduma cikin rudani da rabuwar kawuna, inda shugabancin jam’iyyar ya bi sahun wasu gwamnonin kasar da ke fito-na-fito da manufar daina karbar tsoffin kudi ta Shugaba Buhari.

A cewar Kwamitin, “Muna kira ga Babban Ministan Shari’a na Tarayya da Gwamnan Babban Bankin Najeriya da su mutunta umarnin Kotun Koli na wucin gadi wanda har yanzu ke gabanta.


“Taron yana kira ga Shugaba Buhari da ya sa baki wajen warware matsalolin da canjin kudin ya haifar wa ‘yan Najeriya.”

A hukuncin da Kotun Koli ta zartar, ta dakatar da wa’adin da CBN ya bayar na daina amfani da tsofaffin takardun kudi na 200, 500 da 1000 daga ranar 10 ga watan Fabrairu.

Sai dai duk da wancan hukunci na Kotun Koli, Gwamnan CBN, Godwin Emefiele ya tabbatar da cewar wancan hukunci na daina amfani da kudin yana nan daram.

Kazalika, a ranar Alhamis din da ta gabata ne, Shugaba Buhari ya kara wa’adin ci gaba da amfani tsohuwar takardar Naira 200 har na tsawon wata biyu.


Kazalika, a ranar Alhamis din da ta gabata ne, Shugaba Buhari ya kara wa’adin ci gaba da amfani tsohuwar takardar Naira 200 har na tsawon wata biyu.


Sai dai wasu daga cikin gwamnonin APC da suka hada da Nasir El-Rufai na Jihar Kaduna da Yahaya Bello na Kogi da Bello Matawalle na Zamfara da Abdullahi Umar Ganduje na Kano da kuma takwaransu na Ogun, Dapo Abiodun, sun kalubalanci umarnin na Shugaban Kasa.

Yayin gana wa gwamnonin jam’iyyar, shugaban na APC ya goyi bayansu inda ya koka kan irin wahalar da canjin kudin ya haifar.

Canjin kudin dai da CBN ya yi, ya bar baya da kura inda wasu ‘yan siyasa ke ganin da gan-gan aka fito da shi don kawo musu zagon-kasa a zaben 2023 da ke tafe.

Yayin da a gefe guda kuma, tsarin ya haifar da tashin-tashina a wasu jihohin da zanga-zanga ta barke, tare da kai hare-hare kan bankuna da masu sana’ar PoS.

Tuni dai miliyoyin mutane suka koka tare da yin kira ga Gwamnatin Tarayya da ta duba halin da suke ciki, yayin da wasu kuma ke zargin tsarin na barazana da durkushewar kasuwancinsu.

Friday, 17 February 2023

Yadda CBN Ya Lashe Amansa Kan Karbar Tsoffin N500 Da N1,000

 


Babban Bankin Najeriya (CBN) ya jefa ’yan Najeriya cikin rudani bayan ya fitar da sanarwa masu cin karo da juna kan ci gaba a karbar tsoffin takardun N500 da N1,000 cikin dan kankanin lokaci.

CBN ya lashe amansa ne bayan manyan bankunan kasuwanci irinsu UBA da First Bank sun tura wa abokan huldarsu sakonni cewa za su ci gaba da karbar tsoffin takardun N500 da N1,000.

Bankunan sun yi haka ne bayan wata sanarwar da kakakin CBN, Osita Nwanisobi, da ke umartar su da karbar kudin matukar ba su wuce N500,000 ba.

Sakonsa ga  bankunan ya ce,

“Kwastoma zai iya kai har N500,000 bankin kasuwanci, amma abin da ya haura hakan sai dai ya kai ofishin CBN.

“Don haka ana bukatar ku bi wannan umarnin,” in ji wasikar farko da babban bankin ya aike wa manajojin reshe da ayyukan bankunan kasuwancin.

Bayan fitowar wasikar, ’yan jarida sun tuntubi Mista Nwanisobi, game da ita, wanda ya tabbatar musu da sahihancinta.

“Duk wanda ke da tsoffin takardun kudin da suka haura N500,000 ya kai ofishin CBN mafi kusa

“Muna kuma sanar da ku cewa za mu bude rassanmu gobe Asabar 18 ga Fabrairu, 2023.”

Shi ma bankin UBA ya tura irin wannan sako ga kwastomominsa kamar haka: “Ba mu daina amsar tsoffin takardun N500 da N1,000 ba, matukar ba su haura N500,000 ba.

Bankunan sun tura sakonnin ne a ranar Juma’a.

Amma kafin a jima, bayan kafofin watsa labarai su wallafa labarin, sai CBN ya fitar da wata sabuwar sanarwa, yana karyata umarninsa na farko da ya baiwa bankuna su ci gaba da karbar tsofaffin N500 da N1000.

A sabuwar sanarwar, kakakin na CBN ya zargi kafofin watsa labarai da yada labarin karya — wato sanarwarsa ta farko wadda shi da kansa ya tabbatar musu da sahihancinta.

“ To a sani cewa, kamar yadda Shugaban Kasa ya ba da umarni, tsoffin takardun kudi da za a ci gaba da amfani da su, su ne N200 na tsawon kwana 60 zuwa ranar 10 ga watan Afrilu.”

A kan haka ne First Bank ya goge sakon da ya wallafa a shafinsa na Twitter.

Wannan dambarwar ta zo ne washegarin jawabin Shugaban Kasa Muhammadu Buhari, inda ya ba da umarnin a ci gaba da amfani da tsoffin takardun Naira 200 tare da sabbin takardun Naira 200, 500 da kuma 1,000 har zuwa 10 ga watan Afrilu, ranar da tsohuwar 200 za ta daina aiki.

Buhari ya sanar da haka ne a jawabinsa ga ’yan Najeriya da ke ci gaba da surutu kan sauyin takardun kudin da CBN ya yi, da kuma karancin sabbin da ya jefa su cikin damuwa.

Hannu guda kuma gwamnatocin was jihohi sun maka Gwamnatin Tarayya a Kotun Koli suna neman ta soke dokar haramta amfani da tsoffin kudin.

Batun karancin sabbin takardun kudin dai ya jefa ’yan Najeriya cikin kunci, har da asarar rayuka.

A wasu jihohin Kudu abin ya kai ga tarzoma da kona bankuna.

AMINIYA

Babban bankin Najeriya (CBN) ya musanta rahotannin da ake ta yadawa cewa ya ba bankunan ajiya izinin karbar tsoffin takardun kudi na N500 da N1,000.

A wata sanarwa da Osita Nwanisobi, Daraktan Sadarwa na Babban Bankin na CBN ya fitar a ranar Juma’a, babban bankin ya ce don kaucewa shakku ne kawai CBN ke sake fitar da wasu tsofaffin takardun kudi na Naira 200 kuma ana sa ran za a rika yawo a matsayin takardar kudi na tsawon kwanaki 60 har zuwa watan Afrilu. 10, 2023, daidai da shirin shugaban kasa Muhammadu Buhari na kasa ranar Alhamis.


Babban bankin na CBN ya shawarci jama’a da su yi watsi da duk wani sako da/ko bayanan da bankin bai fitar a hukumance ba kan wannan batu.

Ta kuma shawarci masu aikin yada labarai da su yi kokarin tabbatar da duk wani bayani daga majiya mai kyau kafin a buga su.

Sanarwar ta kara da cewa;

An jawo hankalin babban bankin Najeriya kan wasu sakonni na bogi da ba da izini ba da ke ambato babban bankin na CBN na cewa ya ba bankunan ajiya izinin karbar tsoffin takardun kudi na N500 da N1,000.

Domin kaucewa shakku, kuma bisa tsarin yada labarai na shugaban kasa na ranar 16 ga Fabrairu, 2023, an umurci CBN da sake fitar da tsoffin takardun kudi na N200 KAWAI kuma ana sa ran za a yi ta yawo a matsayin takardar kudi na tsawon kwanaki 60 har zuwa 10 ga Afrilu. , 2023.


Don haka ya kamata jama’a su yi watsi da duk wani sako da/ko bayanan da babban bankin Najeriya bai fito a hukumance ba kan wannan batu.
DN24

LABARI DA DUMI-DUMI: Emiefele ya umurci bankunan da su karbi tsofaffin takardun kudi na N500, N1,000

Babban bankin Najeriya (CBN) ya bukaci bankuna da su fara karbar tsofaffin takardun kudi na N500 da N1,000 daga hannun kwastomomi.

Osita Nwanisobi, kakakin babban bankin ne ya bayyana hakan a ranar Juma’a, inda ya bayyana cewa ba za a iya ajiye duk wani kudi da ya haura N500,000 ba kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.


Wannan ci gaban dai na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da nuna bacin ran da aka yi a fadin kasar dangane da kin amincewa da takardun kudi da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya ayyana a matsayin ba na doka ba.

A cikin shirinsa na yada labarai na kasa, Buhari ya bukaci ‘yan Najeriya da su karbo tsofaffin takardun kudi na N500 da N1000 ga CBN.

'Yan Najeriya sun yi dafifi zuwa manyan bankunan banki don ajiye tsoffin takardunsu.

Yayin da jami’an bankin ke kokarin shawo kan jama’a, sai suka tura su bankunan kasuwanci amma mutanen suka ki amincewa.

Cikakken labarin zai zo muku nan gaba 

Thursday, 16 February 2023

Buhari Ya Ce A Ci Gaba Da Amfani Da Tsoffin Takardun N200

 


Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya ba da umarni a ci gaba da amfani da tsoffin takardun Naira 200.

Buhari ya ba da umarnin a ci gaba da amfani da tsoffin N200 ne ga Babban Bankin Najeriya (CBN) a yayin jawabinsa ga ‘yan Najeriya a safiyar Alhamis.

Ya kara wa’adin amfani da tsoffin takardun N200 ne da kwana 60 zuwa ranar 20 ga watan Afrilu, 2023.

Hakan na zuwa ne washegarin da Kotun Koli ta dage sauraron karar da wasu gwamnatocin  jihohi suka shigar na kalubalantar dokar haramta amfani da tsoffin N1,000 da N500 da kuna N200 da CBN ta canja.

Wednesday, 15 February 2023

Yanzu-Yanzu! Buhari Ya Gana Da Bola Tinubu A Fadar Shugaban Kasa

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya gana da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC mai mulki, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu a fadar shugaban kasa da ke Abuja.
Taron wanda rahotanni suka ce an yi shi ne a Gidan da ke cikin Villa, kamar yadda majiya mai tushe ta bayyana, wanda aka yi gabanin taron Majalisar Zartaswa na Tarayya (FEC) na mako-mako.
Ko da yake ba a iya gano dalilin taron ba, domin a lokacin da ake gabatar da wannan rahoto, ana kyautata zaton na da alaka da batutuwan yakin neman zabe da sauran batutuwan da suka shafi kasa baki daya.
Daga nan ne Buhari ya shiga taron FEC na mako-mako, don jagorantar taron, da misalin karfe 10:40 na safe, bayan mintuna 40 kamar yadda aka saba, kamar yadda aka saba shirya taron ne daga karfe 10 na safe.
Wata majiyar kuma ta bayyana cewa rashin jinkirin da shugaban kasar ya yi da Tinubu, tabbas ya biyo bayan matakin da ya dauka na komawa baya ne don sa ido kan sakamakon shari’ar da kotun koli ta yi wa gwamnatin tarayya da babban bankin Najeriya CBN. ) akan manufofin sake fasalin naira, wanda daga karshe aka daga ci gaba da zama ranar Laraba 22 ga watan Fabrairu.
Taron na majalisar zartarwa ta kasa ya samu halartar Sakataren Gwamnatin Tarayya (SGF), Mista Boss Mustapha, da Shugabar Ma’aikata ta Tarayya, Dr Folasade Yemi-Esan.
Haka kuma akwai Ministocin Watsa Labarai da Al’adu, Lai Mohammed, Mai Shari’a, Abubakar Malami, Sadarwa da Tattalin Arziki na Dijital, Isa Pantami, kasafin kudi da tsare-tsare na kasa, Zainab Ahmed, Babban Birnin Tarayya, Mohammed Bello da Ilimi, Adamu Adamu.
Sauran sun hada da Ministocin Lafiya, Dokta Osagie Ehanire, Harkokin jin kai, Gudanar da Bala'i da Ci gaban Jama'a, Sadiya Farouq, da kuma Ministocin Ma'aikatar Gona, Mustapha Shehuri, Kasafi da Tsare-tsare na Kasa Clement Agba da dai sauransu.

DA DUMI-DUMI: Sake fasalin Naira: Kotun Koli ta Dage Sauraron karar da Kaduna, Kogi da Zamfara suka shigar


Kotun kolin Najeriya ta dage ci gaba da shari’ar kan manufar musanya naira na babban bankin Najeriya CBN zuwa ranar Laraba 22 ga watan Fabrairu domin sauraron kararrakin da jihohi 10 suka hada.

 

Kotun kolin da ta saurari karar a ranar Larabar da ta gabata ta cika makil da wasu manyan lauyoyi da sauran gwamnonin jihohin Kaduna da Kogi, Nasir El-Rufai da Yahaya Bello, bi da bi.

 

A zaman da ya gabata, Kotun ta dakatar da aiwatar da wa'adin ranar 10 ga watan Fabrairu na CBN daga yin kwangilar tsohuwar takardar kudi ta N200, N500 da N1,000.

 

Jihohin Zamfara da Kogi da kuma Kaduna ne suka shigar da karar gwamnatin tarayya da kuma babban bankin kasa CBN.

 

Sauran jihohin da suka hada da Neja, Kano, Ondo, Ekiti, su ma sun nemi a shigar da su gaban CBN da gwamnatin tarayya.

 

 

An fara zaman kotun inda mai shari’a John Okoro ya jagoranci kwamitin mutum bakwai.

 

Ya ce bai kamata kotu ta yi watsi da shari’ar da kuma manufarta ba domin ya shafi ’yan Najeriya da ke addabar jama’a.

 

Jihar Legas, ta hannun babban mai shari’a, Moyosore Onigbanjo, ita ma ta nemi a shigar da ita kara.

 

Jihar Bayelsa, karkashin jagorancin Damian Dodo, ita ma ta nemi a shigar da ita kara a matsayin wanda ake kara. Hakazalika, Jihar Edo ta nemi a shigar da ita a matsayin wanda ake kara.

 



Community Verified icon

Tuesday, 14 February 2023

Wa'adin Dena Karbar Tsofaffin Kudi Ya Cika - CBN

Gwamnan Babban Bankin Najeriya (CBN), Godwin Emefiele, ya jadadda cewar ranar 10 ga watan Fabrairu ne wa’adin amfani tsofaffin takardun Naira ya cika.

Emefiele ya bayyana hakan ne a lokacin da yake zantawa da jami’an diflomasiyya a Ma’aikatar Harkokin Waje da ke Abuja a ranar Talata.

“Lamarin ya lafa sosai tun bayan lokacin da aka fara biyan kudi a kan kanta wanda hakan ya rage dogayen layuka a ATM.

“Don haka babu bukatar la’akari da wani sauyi daga wa’adin ranar 10 ga Fabrairu,” in ji shi.

‘Yan Najeriya sun shiga rudani yayin da bankunan kasuwanci suka daina karbar tsoffin takardun tun daga ranar Litinin.

Da yake karin haske, Emefiele ya ce, “Wasu daga cikin shugabanninmu suna siyan sabbin takardun kudi suna ajiyewa saboda wata manufa saboda haka ba zan iya yin karin haske kan hakan ba.”

Emefiele ya ce babban bankin ya san irin wahalhalun da ‘yan Najeriya ke sha sakamakon canjin kudin, amma ya ce tsarin zai iya kawar da kashi 4 cikin 100 na hauhawar farashin kayayyaki.

Ya kuma yi bayanin cewa kamata ya yi a ce adadin kudin da ke zagawa a hannun al’umma ya kai kusan Naira biliyan 700.


Ana iya tuna cewa, a bayan nan ne dai gwamnatocin jihohin Kaduna, Zamfara da Kogi suka maka CBN da Gwamnatin Tarayya a gaban Kotun Koli suna kalubalantar sabon tsarin amfani da sabbin takardun kudi. 

AMINIYA 


Monday, 13 February 2023

Kotun 'Ma'aikata Ta Umarci Ganduje Da Ya Amince Da Muhuyi A Matsayin Shugaban Hukumar Karbar Korafi Ta Kano


A ranar Litinin din da ta gabata ne Kotun ma’aikata ta kasa da ke zamanta a Kano, ta umarci gwamnatin jihar Kano da ta ci gaba da kasancewa a kan “status quo ante bellum” a karar da korarren shugaban hukumar korafe-korafe da yaki da cin hanci da rashawa ta Kano PCAC, Muhuyi Magaji Rimingado ya shigar, har sai an ci gaba da sauraron karar.

Status quo ante bellum yana nufin halin da ake ciki kamar yadda ya kasance kafin jayayya.

 

An shigar da karar  gwamnatin jihar Kano da majalisar dokokin jihar da kuma babban lauyan jihar Kano a matsayin wadanda ake tuhuma na 1 da na 2 da na 3.

gaban mai shari’a E.D. Esele,

 

Mista Rimingado yana kalubalantar sahihancin matakin da gwamnati ta dauka na korar shi ba tare da bin ka'ida ba.

 

A bisa wannan umarnin, wasikar korar da aka mika wa Mista Rimingado ba ta da wani tasiri kuma hukuncin da kotun masana’antu ta kasa, Abuja ta yanke a baya yana nan daram sai dai idan kotu ta yanke hukunci bayan yanke hukunci.

 

A ranar 14 ga Disamba, 2022, kotun ma’aikata ta kasa ta ayyana Mista Rimingado a matsayin shugaban hukumar, sannan ta kuma umarci Ganduje ya biya shi bashin albashin N5,791, 891.22.


Sai dai a wata takardar sallamar mai dauke da kwanan watan 24 ga watan Janairu mai dauke da sa hannun sakataren gwamnatin jihar Usman Alhaji, gwamnatin jihar ta kori Mista Rimingado a matsayin shugaban hukumar, saboda kudirin majalisar dokokin jihar a ranar 26 ga watan Yuli.

DAILY NIGERIAN

Duk wanda ya kwarmata masu ɓoye sabbin kuɗaɗe zai samu tukuici – EFCC

Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta EFCC a Najeriya ta ce bankunan kasuwanci ne suka janyo tarnaƙi wajen ganin sabbin kuɗi sun wadata a hannun jama'a.

EFCC ta ce bayanai daga Babban Bankin Najeriya sun nuna cewa zuwa yanzu, CBN ya buga sabbin takardun kuɗi sama da naira biliyan 400, amma bankuna sun ƙi fitarwa su bai wa jama'ar ƙasar.

Shugaban hukumar EFCC, Abdurrasheed Bawa a wata tattaunawa da BBC, ya buƙaci 'yan Najeriya su tona asirin masu ɓoye sabbin kuɗi, don ganin hukumar ta je ta ƙwace su.

Abdurrashe Bawa ya ce wannan ita ce mataki na gaba da suke ganin zai taimaka wajen kawo wa talakan Najeriya waraka.

Sannan ya tunasar da cewa akwai tukuici mai gwabi ga duk mutumin da ya taimaka aka gano wurare ko mutumin da ke rike da sabbin kudade.

'Ma’aikatan banki ne matsalar mu’
Shugaban na EFCC ya ce babu shaka sun yi na'am da wannan sauyi kuɗi, saboda bayanan sirri ya nuna musu cewa akwai mutane da dama da suka boye kuɗaɗe, suna cinikayya a boye.

Sai dai ya ce babbar matsalarsu ita ce ma'aikatan banki, saboda duk da cewa kuɗaɗen da aka buga ba su wadatu ba, ma'aikatan na bai wa wasu mutane kuɗaɗen a ɓoye.

"Su na hana talakawa kudaden a banki da na’urar ATM".

"Shiyasa mu ka tura jami'ansu jihohi domin sa ido kan bankunan da mutanen da ke yiwa harkar zangon kasa".

Zargin bai wa gwamnoni kuɗaɗe
Ya ce akwai zargin dagaske ana bai wa gwamnoni sabbin kuɗaden, kuma akwai wadanda suka boye tsoffi kuɗaɗe, shiyasa aka ba wa 'yan Najeriya damar kwarmata duk wani mutum da suka fuskaci na ɓoye kuɗaɗe.

EFCC ta tunasar da cewa duk mutum da ya tona asiri zai samu kasonsa mai gwaɓi, don haka kada mutane su yi kasa a gwiwa.
(BBC) 

Sunday, 12 February 2023

Yanzu-Yanzu : Dan Takarar Gwamnan Kano Na Jam'iyyar LP, Bashir I Bashir Ya Koma APC

Dan takarar gwamna na jam’iyyar Labour Party, LP, a jihar Kano, Bashir Bashir, ya fice daga jam’iyyarsa zuwa jam’iyyar All Progressives Congress, APC.

A ranar 21 ga watan Janairu, dan takarar gwamnan ya kaurace wa taron gangamin jam’iyyar a Kano tare da shugaban kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa, Mohammed Zarewa; kodinetan yakin neman zaben Peter Obi na jiha, Balarabe Wakili da; dan kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa, Idris Dambazau.

Wata majiya da ke kusa da dan takarar ta tabbatar da sauya shekar Mista Bashir da wasu jiga-jigan jam’iyyar LP zuwa APC a ranar Lahadin da ta gabata, inda ta ce babban dalilin da ya sa suka sauya sheka shi ne na ware manyan masu ruwa da tsaki a Arewa wajen yanke shawara da kuma rashin samun cikakkiyar alkibla kan maslahar Arewacin Najeriya. .

Saturday, 11 February 2023

Canjin Kudi Ya Rage Satar Mutane Da Karbar Rashawa —Malami

Ministan Shari’a kuma Antoni-Janar na Tarayya, Abubakar Malami (SAN), ya bayyana cewa canjin kudi ta Babban Bankin Najeriya (CBN) ya yi ya taimaka wajen rage aikata ayyukan garkuwa da mutane.

Malami, ya bayyana haka ne cikin wata hira da ya yi da Gidan Rediyon Tarayya da ke Kaduna, inda ya ce jama’a ba sa ganin nasara da tsarin ya haifar.

Da yake bayyana hakan a ranar Juma’a, Malami ya ce: “Na fada muku maganar tana gaban kotu, ba za mu bijire wa kotu ba, za mu bi umarnin kotu amma muna da ’yancin fada wa kotu alfanun da tsarin ya haifar.

“Idan ba ku ga amfanin tsarin ba, ya kamata kuma a gefe daya ku ga alfanunsa.

“Idan wadancan gwamnonin sun bayyana wa kotu wahalar da ake sha saboda tsarin, ya kamata kuma a fahimci cewa tsarin a gefe daya yana warware wasu matsalolin.

“Na ba ku misali da matsalar tsaro; Tun bayan da aka kaddamar da wannan tsarin garkuwa da mutane ya ragu.

“Sannan ya rage yawan cin hanci da rashawa, don haka muna da ’yancin zuwa mu bayyana wa kotu amfanin da tsarin ya haifar.

“Kotun ta yanke hukunci ba tare da sauraron bangaren gwamnati ba, amma ta sanya 15 ga Fabrairu a matsayin ranar da za ta saurari tsagin gwamnati.


Kowa ya san dalilin da aka zabi Shugaban Kasa Muhammadu Buhari, saboda ya yaki cin hanci da matsalar tsaro ya kuma bunkasa tattalin arziki. Don haka za mu bukaci kotu ta kalli kowane bangare.”


Idan ba a manta ba a satin da ya wuce ne gwamnatocin jihohin Kaduna, Zamfara da Kogi suka maka Gwamnatin Tarayya a Kotun Koli inda suka bukaci kotun da dakatar da hana amfani da tsofaffin takardun kudi.


Wannan dai na zuwa ne bayan wahala da talakawa suka shiga sakamakon canjin kudi da CBN ya yi, wanda hakan ya sa kasuwancin wasu ke neman durkushewa.

Friday, 10 February 2023

Labari da dumiduminsa : Kotun Daukaka Kara Ta Tabbatar Da Sadiq Wali A Matsayin Dan Takarar Gwamnan Kano Na PDP

A ranar Juma’a ne wata kotun daukaka kara ta jihar Kano ta tabbatar da Sadiq Aminu Wali a matsayin dan takarar gwamna na jam’iyyar PDP a Kano.


A wani hukunci na bai daya da ta yanke a ranar Juma’a, kotun daukaka kara ta yi watsi da hukuncin da karamar kotun ta yanke na tabbatar da Muhammad Abacha a matsayin dan takarar gwamnan jihar Kano na PDP.

Cikakkun labarin zai zo muku nan ba da jimawa ba…

Thursday, 9 February 2023

Hukumar NAHCON Ta Bude Cibiyar Bayar Da Horo Kan Ayyukan Hajji

Hukumar alhazai ta kasa NAHCON ta kaddamar da cibiyar bayar horo kan ayyukan Hajji da alhazai

Cibiyar za ta horas da duk ma’aikatan da ke aikin Hajji da Umrah ta Najeriya tare da ba su takardar shaida. Haka kuma za ta samar da hanyoyin koyon sana'o'i, bunkasa sana'o'in Matasa da kuma zama wurin tuntuba a duk duniya wajen horar da aikin Hajji da Umrah.

An kuma gabatar da kason farko na daliban cibiyar. Daliban sun hada da Shugaban Hukumar, da daukacin kwamishinonin zartaswa na Hukumar, mambobin hukumar da zababbun Sakatarorin gudanarwa na hukumar jin dadin Alhazai na Jahohi. 

Manyan baki da dama ne suka halarci bikin, ciki har da Ministan babban birnin tarayya Abuja, Malam Muhammad Musa Bello CON; Sakataren Gwamnatin Tarayya, Boss Mustapha CFR; Jakadan Saudiyya a Najeriya,  Faisal Ibn Ibrahim Al-Ghamdy; Shugaban NAHCON, Alh. Zikrullah Kunle Hassan da Babban Sakataren Hukumar NBTE, Farfesa Idris Bugaje.
(Nura Hassan Yakasai) 

Wednesday, 8 February 2023

Kotun Ƙolin Ta Dakatar Da Gwamnatin Najeriya Dga Aiwatar Da Wa'adin Amfani Da Tsofaffin Kudi

Kotun Ƙolin Najeriya ta dakatar da gwamnatin tarayya daga aiwatar da wa'adin amfani da tsofaffin takardun kuɗin kasar.

A baya dai CBN ya saka 10 ga watan Fabrairu a matsayin ranar da za a daina amfani da tsofaffin takardun naira 1,000 da 500 da kuma 200 da aka sauya wa fasali.

Jihohin arewacin ƙasar uku, waɗanda suka haɗa da Kaduna da Kogi da kuma Zamfara suka shigar da ƙarar a gaban Kotun Ƙolin ƙasar suna buƙatar kotun da ta hana Babban Bankin ƙasar aiwatar da wa'adin.

A hukuncin wucin-gadin da suka yanke, alƙalan kotun bakwai ƙarƙashin jagorancin mai shari'a John Okoro, sun dakatar da gwamnatin tarayya da Babban bankin ƙasar da sauran bankunan kasuwanci na ƙasar daga aiwatar da wa'adin 10 ga watan Fabrairu na amfani da tsofaffin takardun kuɗin ƙasar.

Kotun ta kuma ce dole ne gwamnatin tarayya da CBN da kuma sauran bankunan ƙasar su jingine batun aiwatar da wa'adin har zuwa lokacin da kotun za ta yanke hukunci game da lamarin a ranar 15 ga watan Fabrairu.

Wannan hukunci na nufin a halin yanzu al'ummar Najeriya za su ci gaba da amfani da tsofaffin takardun kudin ƙasar har zuwa lokacin da kotun za ta yanke hukuncin ƙarshe.

Batun wa'adin amfani da tsofaffin kuɗin ƙasar dai ya zama wani batu da ya ɗauki hankula a 'yan kwanakin nan.

Tuesday, 7 February 2023

Buhari ya gana da Emefiele da EFCC kan karancin Naira

 


Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya yi ganawar sirri  da Gwamnan Babban Bankin Kasar, CBN, Godwin Emefiele da shugaban Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa , EFCC, AbdulRasheed Bawa da Sakataren Gwamnatin Tarayya, Boss Mustapha da kuma shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, Farfesa Ibrahim Gambari  game da halin da kasar ke cikin na karancin takardar kudin Naira

Kazalika gwamnan Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal da takwaransa na Kebbi, Atiku Bagudu, su ma sun halarci zaman na yau Talata.

An gudanar da wannan zaman ne a daidai lokacin da  ake fama fa matsanancin karancin takardar kudin Naira wanda ya haddasa zanga-zanga a wasu sassan Najeriya tare da kaddamar da hari kan wasu bankuna da jami’an tsaro.

A Juma’ar da ta gabata  ne, shugaba Buhari ya roki ‘yan kasarr da su ba shi wa’adin kwanaki bakwai domin magance matsalar karancin takadar Nairar wadda ta samo asali sakamakon shirin Babban Bankin CBN na sauya fasalin Naira 1000 da 500 da kuma 200.

Nan da ranar 10 ga wannan wata ne, wa’adin da shugaban ya nema zai cika, yayin da ‘yan kasar suka zura idanu domin ganin yadda za ta kaya.

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da ake shirin gudanar da zaben shugaban kasa nan da ‘yan kwanaki kalilan, yayin da batun karancin Nairar ya yamutsa hazon siyasar kasar, inda har dan takarar shugaban kasa na Jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu ke zargin cewa, zagon-kasa ake yi masa, shi ya sa aka bullo da shirin sauya Nairar gami da kirkirar matsalar karancin man fetur a cewarsa.

 (RFI)

Dillalan Man Fetur Sun Lashe Amansu Kan Shiga Yajin Aiki

Yan sa’o’i bayan umartar mambobinta su rufe ilahirin gidajen man fetur a Najeriya, Kungiyar Dillalan Man Fetur ta Kasa (IPMAN) ta bukaci a bude gidajen a ci gaba da sayarwa.

Aminiya ta rawaito yadda a ranar Talata kungiyar ta bukaci a rufe ilahirin gidajen man da ke kasar nan take sannan a fara yajin aiki, kamar yadda wata sanarwa da Shugaban kungiyar na kasa, Mohammed Kuluwa, ya fitar ranar Talata.


IPMAN ta ce, “Sakamakon mawuyacin halin da muka tsinci kanmu a ciki wajen samo man da kuma sayar da shi da tsada, da kuma yadda hukumomi ke tilasta mana sayar da shi a kan farashin da muke faduwa.

“Muna umartar ilahirin mambobinmu da su dakatar da sayar da mai, sannan su dakatar da biyan kudin duk wani man da suka riga suke kokarin sarowa daga yanzu har sai abin da hali ya yi.”


To sai dai ’yan sa’o’i bayan waccan sanarwar, IPMAN ta yi mi’ara koma baya.

“Bayan tattaunawa da hukumomi masu ruwa da tsaki, muna umartar gidajen mai da su bude su ci gaba da sayarwa, yayin da uwar kungiya za ta ci gaba da tattaunawa,” kamar yadda sabuwar sanarwar ta IPMAN, wacce ita ma Shugaban nata ya sanya wa hannu ta fada.

Sanarwar ta dillalan man na zuwa ne a daidai lokacin da ’yan Najeriya ke ci gaba da kokawa da dogayen layuka da wahalar man ta haifar a fadin kasar.

Kazalika, ana fama da tsadar man a kusan duk fadin kasar, inda a wasu wuraren ya haura N370 a kan kowacce lita, yayin da a wasu Jihohin kuma rahotanni suka ce har ma ya haura N400

Hakan kuma na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da fama da karancin takardun kudi sakamakon canjin da Babban Bankin Najeriya (CBN) ya yi.

(AMINIYA) 

Monday, 6 February 2023

Kotu Ta Hana Buhari Da CBN Kara Wa’adin Karbar Tsoffin Takardun Kudi


 Babbar Kotun Birnin Tarayya ta hana Shugaba Buhari da Gwamnan Babban Bankin Najeriya (CBN), Godwin Emefiele, kara wa’adin amfani da tsoffin takardun Naira da aka sauya fasalinsu.

Alkalin kotun, Mai Shari’a Eleoje Enenche ya kuma hana daukacin bankuna da ke Najeriya yin duk wata hulda da ta danganci tsoffin takardun kudin ko neman kara wa’adin amfani da su daga ranar 10 ga watan 10 ga watan Fabrairu da muke ciki.

Da yake sauraron ƙarar da wasu biyar daga cikin jam’iyyun siyasa 18 da ke Najeriya suka shigar, alkalin ya bukaci shugabannin bankuna da jami’ansu su kawo dalilan da za su hana a kama su da kuma gurfanar da su a gaban kotu kan zargin su da yin zagon kasa ga tattalin arziki, bisa yadda suke boye sabbin takardun Naira 1,000 da N500 da kuma N200 da CBN ya sauya wa fasali ya kuma ba su, amma suke kin ba wa mutane.

(AMINIYA)

Kotun Koli Ta Tabbatar Da Ahmed Lawan A Matsayin Dan Takarar Sanata Na Yobe Ta Arewa

Kotun koli a ranar Litinin ta tabbatar da Ahmed Lawan, shugaban majalisar dattawa a matsayin dan takarar sanata na jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a jihar Yobe ta arewa.


A wani hukunci mafi rinjaye da mai shari’a Centus Nweze ya yanke, kotun kolin ta amince da daukaka karar da jam’iyyar APC ta shigar kan takarar Bashir Machina.

Hukuncin da mafi rinjayen alkalai uku suka yanke wa 2, ya yi watsi da hukuncin da kotun daukaka kara ta Abuja ta yanke a ranar 28 ga watan Nuwamba, 2022, ta tabbatar da Bashir Sherrif Machina a matsayin dan takarar sanata na jam’iyyar APC na jihar Yobe ta Arewa a zabe mai zuwa.


Sai dai mai shari’a Adamu Jauro da Emma Agim sun nuna rashin amincewa da hukuncin da aka yanke, wanda hakan ya sanya suka yanke hukuncin watsi da karar da jam’iyyar APC ta shigar tare da tabbatar da sakamakon binciken da kotunan da ta shigar da kara suka yi.


Kamfanin dillancin labaran Najeriya ya ruwaito cewa Mai shari’a Monica Dongban-Mensen, wacce ta jagoranci kwamitin mutane uku na kotun daukaka kara, ta bayyana hakan ne a wata daukaka kara da jam’iyyar APC (mai daukaka kara) ta shigar inda take kalubalantar hukuncin da mai shari’a Fadimatu Aminu ta babbar kotun tarayya da ke Damaturu, ta yanke. a ranar 28 ga Satumba, 2022, ta ayyana Machina a matsayin wanda ya lashe zaben fidda gwani da jam’iyyar ta shirya a ranar 28 ga Mayu, 2022.


Sai dai tun bayan da Bola Tinubu ya lashe zaben fidda gwanin takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, jam’iyyar ta zabi Lawan ne domin maye gurbin Machina.

Amma Machina ya dage cewa ba zai janye wa Shugaban Majalisar Dattawa ba.

A yayin da ake fuskantar cece-kuce, jam’iyyar APC ta mika sunan shugaban majalisar dattawa ga hukumar zabe mai zaman kanta a matsayin dan takararta na Sanata mai wakiltar Yobe ta Arewa.

Sakamakon rashin gamsuwa da hukuncin da jam'iyyarsa ta yanke ba, Machina ya garzaya kotu domin neman hakkinsa.

Machina a cikin karar sa, ya bukaci kotu da ta bayyana shi a matsayin zababben dan takarar sanata na jam’iyyar APC mai wakiltar Yobe ta Arewa.

Mai shari’a Aminu ya soke zaben fidda gwanin da aka yi wanda ya samar da Lawan a ranar 9 ga watan Yuni, 2022, inda ya dage cewa kwamitin gudanarwa na jam’iyyar APC ya gudanar da sahihin zaben fidda gwani a ranar 28 ga watan Mayu, wanda Bashir Sheriff Machina ya lashe.

Don haka ne alkalin kotun ya umarci APC da ta mika sunan Machina ga INEC a matsayin wanda ya lashe zaben fidda gwani na jihar Yobe ta Arewa.

Sunday, 5 February 2023

Yanzu-Yanzu: Gwamnan Jigawa ya amince da nadin Sabon Sarkin Dutse

Gwamnan jihar Jigawa Muhammad Badaru Abubakar ya amince da nadin Muhammad Hameem Nuhu Sanusi a matsayin sabon sarkin Dutse.

Kadaura24 ta rawaito Sanarwar amincewa da nadin na dauke da sa hannun kwamishinan aiyukan na musamman na jihar Jigawa Auwalu D Sankara,wadda kuma aka rabawa manema labarai.


Nadin ya biyo bayan zaben Masu Zaben Sarki na Masarautar Dutse su bakwai suka yi wa Hameem daga cikin masu neman kujerar sarautar har su su uku.

 Majalisar Sarakunan Jihar Jigawa ta amince da zaben, sannan kuma nadin sa ya fara aiki daga ranar 5 ga Fabrairu, 2023.

 Sabon Sarkin dai ya gaji Mahaifinsa ne Alhaji Nuhu Muhd Sanusi II wanda Allah ya yiwa rasuwa a makon daya

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

FG Urges KOICA, FAO to Align Agricultural Intervention with Nigeria’s Development Priorities, Ward-Based Strategy

The Federal Government has called for stronger alignment between development partners’ interventions and Nigeria’s national deve...