Search This Blog

Showing posts with label Ronaldo. Show all posts
Showing posts with label Ronaldo. Show all posts

Thursday, 4 May 2023

Saudiyya Ta Yi Wa Messi Tayin Ninkin Albashin Ronaldo

 


Kungiyoyin kwallon kafa a kasar Saudiyya na zawarcin gwarzon dan wasan duniya, Lionel Messi, na kungiyar PSG, da tayin albashin da ya zarce na kowane dan wasa a duniya.

Rahotanni sun nuna cewa wata kungiya da ke zawarcin Messi a Saudiyya ta yi masa tayin albashin Naira biliyan 183.5 (Dala miliyan 400) a shekara, idan kwantaraginsa ya kare da PSG a wata mai zuwa.

Kafar labarai ta Telegraph ta kasar Birtaniya ta ce dan wasan ya fara tunanin duba tayin kuma tuni kungiyar ta fara tattaunawa da Kyaftin din na kasar Argentina kan kwangilar da take masa tayi, bayan dakatarwar da PSG ta yi masa.

Idan hakan ta tabbata, Messi zai rika karbar kusan ninki biyun albashin babban abokin hamayarsa Cristiano Ronaldo, wanda a halin yanzu Al Nassr ta kasar Saudiyya ke biyan sa Naira biliyan 96.3 Dala miliyan 210 a shekara, zuwa 2025.

Wannan sabuwar ta taso ne bayan da kungiyar PSG ta dakatar da Messi na tsawon mako biyu ba tare da albashi ba, saboda wata ziyara da ya kai Saudiyya ba da izinin kungiyar ba.

A baya dai an yi ta rade-radin kungiyar Al Hilal ta Saudiyya ce ke neman daukar Messi, daga baya da PSG ta takatar da shi kuma maganar ta kara tasowa.

AMINIYA

Friday, 6 January 2023

Al Nassr za ta mutunta hukuncin dakatarwar wasanni 2 kan Ronaldo

 


Kungiyar kwallon kafa ta Al Nassr a Saudi Arabia ta tabbatar da shirin mutunta hukuncin hukumar kwallon kafar Ingila kan sabon dan wasan da kungiyar ta saya Cristiano Ronaldo game da haramcin wasanni biyu da ke kansa

Wani jigo a Al Nassr ya shaidawa AFP yau juma’a cewa tauraron na Portugal mai shekaru 38 ba zai taka leda a wasanni biyu da kungiyar za ta doka nan gaba ba, domin mutunta hukuncin.  

Tun a watan Nuwamba ne dai, hukumar FA ta dakatar da Ronaldo a wasanni biyu saboda samunsa da laifin jifan wani magoyin bayan Everton da wayar salula lokacin da ya ke shirin daukar hotonsa bayan rashin nasarar Manchester United hannun Everton a Goodison Park.

Har zuwa yanzu dai Al Nassr ba ta yiwa Ronaldo rijista ba, kasancewar kungiyar ta zarta adadin ‘yan wasa 8 sa hukumar kwallon kafar Saudiya ta sahale mata saye daga ketare duk kaka.

Zuwa yanzu dai Al Nassr ta sayi ‘yan wasan da yawansu ya kai 9 daga ketare ciki har da Ronaldo da ta sayo kan yuro miliyan 200 bayan dan wasan gaban na Portugal ya raga gari da Manchester United ana tsaka da gasar cin kofin Duniya

Kwantiragin dan wasan mai shekaru 38 zai kaishi har zuwa watan Yunin 2025.

Yanzu haka dai Al Nassr na bukatar raba gari da dan wasa guda gabanin baiwa Ronaldo damar samun gurbi a Club din yayinda ake jita-jitar yiwuwar kungiyar za ta rabu ne da Jaloliddin Masharipov don samun gurbin yiwa tauraron na Portugal da ya lashe Ballon d’Or sau 5 rijista.

Tuesday, 3 January 2023

Brentford Ta Casa Liverpool A Firimiyar Ingila

 


Liverpool ta barar da damar matse hudun farko a gasar Firimiyar Ingila, bayan da ta sha kashi 3-1 hannun Brentford a filin wasa na Community da ke Landan.

Masu tsaron bayan Liverpool sun yi sakaci musamman Konate, da hakan ya bai wa Brentford damar dawowa mataki na bakwai, maki biyu tsakaninsu da kungiyar ta Anfield.

Tun a minti na 19 da fara wasa ne Ibrahima Konate ya ci gida bayan an yi bugun kusurwa.

Sai kuma a minti na 42 Wissa ya ci ta biyu aka tafi hutun rabin lokaci 2-0.

Kuma yayin da Liverpool ta matsa don ganin ta farke ne, dan wasan gaban Brentford Mbeumo ya kwaci kwallo hannun Konate ya ci wa kungiyarsa kwallo ta uku a minti na 84.

A yanzu Brentford ta yi wasa shida ba a doke ta ba, a karon farko da ta yi irin haka a sama da shekaru 80, kuma sun koma na bakwai a teburin Firimiyar Ingila.

(AMINIYA)

Yayin da Liverpool ta barar da damar matse hudun farko da tazarar maki daya, kuma ta cigaba da zama na shida maki biyu kacal tsakaninta da Brentford.

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

FG Urges KOICA, FAO to Align Agricultural Intervention with Nigeria’s Development Priorities, Ward-Based Strategy

The Federal Government has called for stronger alignment between development partners’ interventions and Nigeria’s national deve...