Search This Blog

Showing posts with label Fadar Shugaban kasa. Show all posts
Showing posts with label Fadar Shugaban kasa. Show all posts

Tuesday, 11 April 2023

Buhari Zai Bar Najeriya Fiye Da Yadda Ya Same Ta – Fadar Shugaban Kasa

 


Fadar Shugaban Kasa ta ce a fannin tsaro da habaka tattalin arziki, Shugaba Muhammadu Buhari zai bar Najeriya fiye da yadda ya same ta a 2015.

Kakakin Shugaban, Femi Adesina, ne ya bayyana hakan lokacin da yake tattaunawa da gidan talabijin na Channels ranar Talata.

Ya kuma ce karyata batun cewa a tsawon mulkin Buhari na shekara takwas, ya nuna kabilanci wajen nafin wadanda za su shugabanci hukumomin tsaron kasar nan.

A cewarsa, nadin nasu ba shi da wata alaka da addinin, yanki ko kabilar da mutum ya fito wajen nadinsu, an fi la’akari da cancanta tun da dai doka ta ba Shugaban ikon nada duk wanda ya ga dama.

Ya ce, “Ka san cewa akwai wani rahoto da ya ce an fi samun karancin mutanen da aka kashe a 2022 a cikin shekara 12 da suka gabata a sakamakon ayyukan ta’addanci? Mun fa sani a Najeriya cewa alkaluman sun ci gaba da sauka a tsawon shekaru.

“Babu wanda ke son a sami asarar rai, komai kankantarsa, amma idan aka ce an sami ragi a yawan mutanen da ake kashewa a kowacce shekara, ni ina ganin abin a yi farin ciki da shi ne.

“Buhari zai bar Najeriya fiye da yadda ya same ta a 2015, lokacin da Kananan Hukumomi 17 ke karkashin ’yan ta’adda. Hatta NYSC ba ta iya ba matasa masu yi wa kasa hidima horo a wadannan yankunan. Amma a yanzu fa?” in ji shi.

Wednesday, 1 February 2023

Akwai Makiyan Tinubu A Fadar Shugaban Kasa – El-Rufa’i

 


Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufa’i, ya yi zargin cewa akwai makiyan dan takarar Shugaban Kasa na jam’iyyar APC, Bola Tinubu a Fadar Shugaban da suke kokarin ganin sun kai shi kasa.

Ya bayyana haka ne yayin tattaunawarsa da gidan talabijin na Channels, a cikin shirinsu na Sunrise Daily da safiyar Laraba.

El-Rufa’i ya ce mutanen, wadanda bai bayyana sunansu ba, sun fusata ne tun lokacin da aka kayar da dan takararsu a zaben fid-da gwani na APC.

Ya kuma ce mutanen na fakewa da bukatar ganin Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya yi abin da ya dace.

“Wadannan mutanen na kokarin fakewa da bukatar Buhari ya yi abin da ya dace. Zan bayar da misalai biyu; wannan batun na biyan tallafin mai wanda ya ke sa Najeriya ta kashe makudan kudade abu ne da dukkanmu mun dade da amincewa a cire shi.

“Sai da ma na tattauna da Shugaban Kasa a kan haka, inda na nuna masa dalilin da zai sa dole a cire. Saboda ta yaya zaka ware biliyan 200 don manyan ayyuka sannan ka kashe tiriliyan biyu wajen biyan tallafi? Wannan maganar muka tattauna da shi a 2021, kuma aka amince za a cire saboda kudin sun tashi sosai

“Misali na biyu kuma shi ne canjin kudi. Ya kamata a fahimci Shugaban Kasa. Mutane na zargin Gwamnan CBN, amma ba haka batun yake ba. Idan muka koma tarihi, ko zamanin mulkin Buhari na soja, ya canza kudi saboda maganin barayi da masu jibge haramtattun kudade a gida.

Kalaman na El-Rufa’i dai na zuwa ne mako daya bayan Tinubu ya yi zargij akwai masu yi masa zagon kasa a cikin jam’iyyarsa, wadanda ya ce ba sa so ya lashe zaben.

Dan takarar ya yi zargin cewa da gangana aka kirkiro wahalar man fetur da canja fasalin kudi domin a yi masa zagon kasa.

(AMINIYA)

Monday, 2 January 2023

Obasanjo ya zama tamkar dan bakin ciki - Fadar Shugaban kasa

Fadar Shugaban Najeriya ta mayar da kakkausan martani kan kalaman da Tsohon Shugaban Najeriya Olusegun Obasanjo ya yi a saƙonsa na sabuwar shekara.

A wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban Najeriya Malam Garba Shehu ya fitar, sanarwar ta ce Obasanjo ba zai taɓa daina caccakar Shugaba Muhammadu Buhari ba sakamakon Obasanjon ba zai daina baƙin ciki kan duk wani wanda ya sha gabansa a ayyukan ci gaban ƙasa ba.

Fadar shugaban ƙasar ta buga misali da cewa Shugaba Buhari ya kammala gadar Neja ta biyu bayan an yi shekara 30 ana alƙawura a kanta.

Haka kuma fadar shugaban ƙasar ta ce Obasanjo ya yi wa kudu maso gabashin Najeriya ƙarya domin ya samu ƙuri'unsu, amma Shugaba Buhari bai samu ƙuri'unsu ba amma duk da haka sai da ya yi musu aikin gadar.

Fadar shugaban ƙasar ta kuma ce Obasanjo yana baƙin ciki ne sakamakon yana ganin yadda Buhari ke samun lambobin yabo da kuma yadda shugaban ke ci gaba da da'awar cewa zai tabbatar an gudanar da sahihin zaɓe fiye da wanda ya kawo sa kan karagar mulki.

Haka kuma fadar ta zargi Obasanjo da lalata dimokraɗiyya a Najeriya bayan kitsa tsige wasu gwamnoni a ƙasar da suka haɗa da Joshua Dariye da Rashidi Ladoja da Peter Obi da Chris Ngige da Ayo Fayose.

Wannan martanin na fadar shugaban Najeriya duk na zuwa ne bayan tsohon Shugaban Najeriyar Chief Olusegun Obasanjo ya ce Peter Obi ne zaɓinsa a zaɓen 2023 haka kuma Obasanjon ya caccaki gwamnatin Shugaba Buhari

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

FG Urges KOICA, FAO to Align Agricultural Intervention with Nigeria’s Development Priorities, Ward-Based Strategy

The Federal Government has called for stronger alignment between development partners’ interventions and Nigeria’s national deve...