Posts

Showing posts with the label DSS

DSS ta kama mutum biyu a Kano kan zargin tayar da rikici

Image
  Hukumar tsaro ta farin kaya DSS ta ce ta kama wasu mutane biyu da take zargi da tunzura mutane domin tayar da hankali a jihar Kano gabanin zaÉ“en gwamna da na ‘yan majalisun jiha da za a yi a ranar Asabar.   Cikin wata sanarwa da ta wallafa a shafinta na Twitter hukumar ta DSS ta ce mutanen sun naÉ—i hoton bidiyo ne da suke bayanan tunzura jama’a a cikinsu, sannan suka riÆ™a wallafa shi a shafukan sada zumunta.   Ta kuma wallafa sunayen Sharu Abubakar TaÉ“ule mai shekara 37 a duniya, da kuma Isma’il Iliyasu Mnagu mai shekara 51 a matsayin waÉ—anda ta kama.   “Cikin waÉ—annan saÆ™onnin masu haÉ—ari, sun nuna jam’iyyar siyasar da suke goyon baya kuma suka yi kira ga magoya bayansu su kai wa abokan hamayyarsu hari duk inda suka gansu.   “WaÉ—anda ake zargin sun yi kira da a kai wa jami’an tsaro hari yayin zaÉ“en gwamnoni da na ‘yan majalisar jihohi da za a yi a ranar Asabar. “Wata jam’iyyar siyasa a Kano na barazanar shirya zanga-zanga a sakamakon shirin kai hare-haren,” in ji hukum

Hukumar DSS Ta Kama Alasan Ado Doguwa

Image
Hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) ta kama shugaban masu rinjaye na majalisar wakilai Alhassan Dogowa, saboda zargin kisan wasu magoya bayan jam’iyyar adawa a yankin.  Majiyarmu ta rawaito cewa an kama Doguwa ne a filin jirgin sama na Malam Aminu Kano , a kan hanyarsa ta zuwa kasar Saudiyya domin gudanar da aikin umarah a ranar talata.  Kamen ba zai rasa nasaba da kisan da aka yi wa magoya bayan ‘yan adawa kusan 15 a karamar hukumar Tudunwada a lokacin zaben da aka kammala ba .  Rahotanni sun ce an kulle wasu daga cikin mutane a wani gini inda aka kona su kurmus, lamarin da ya sa aka gagara kubutar Kadaura24 

Hukumar DSS Ta Musunta Mamaye ofishin Gwaman Babban Bankin Najeriya

Image
Hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) ta musanta mamaye harabar babban bankin Najeriya, a ranar Litinin, kamar yadda ake yada labarin a yanar gizo. Rundunar ‘yan sandan sirrin a cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na hukumar tsaron ta farin kaya, Peter Afunanya ya fitar ta ce labarin karya ne. Idan dai za a iya tunawa a ranar Litinin din da ta gabata ne aka ga motocin a harabar babban bankin da ke Abuja. Hukumar ta DSS a cikin sanarwar ta ce jami’anta ba su yi yunkurin kama gwamnan na CBN ba.

LABARI DA DUMIDUMINSA! Jami’an Hukumar I DSS Sun Mamaye ofishin Gwaman Babban Bankin Najeriya

Image
Jami’an hukumar tsaro ta farin kaya, SSS, sun mamaye hedikwatar babban bankin Najeriya CBN, inda suka karbe ofishin gwamnan babban bankin, Godwin Emefiele. Jaridar DAILY NIGERIAN ta rawaito cewa an yi artabu tsakanin jami’an SSS da Mista Emefiele kan zargin bada tallafin yaki da ta’addanci. A baya dai hukumar leken asirin ta nemi kotu ta kama Mista Emefiele amma ya fita kasar domin hutun shekara da zai kare a gobe 17 ga watan Janairu. Sai dai a watan Disamba ne babbar kotun birnin tarayya ta haramtawa SSS kama, gayyata, ko kuma tsare Mista Emefiele. Jami’an SSS da suka isa hedikwatar CBN a ranar Litinin da ta gabata, sun shigo da motoci kusan 20 dauke da jami’an tsaro. Jami’an sun kuma hana duk ma’aikatan bankin shiga ofishin Mista Emefiele. Peter Afunanya, mai magana da yawun SSS, har yanzu bai amsa tambayar da dan jaridan ya aike masa ba. Cikakkun bayanai daga baya…

Hukumar DSS ta kama tsohon Shugaban Kungiyar Yakin Neman Zaben dan takarar Shugaban Kasa na jam’iyyar LP, Doyin Okupe

Image
Hukumar Tsaro ta Farin Kaya (DSS) ta kama tsohon Shugaban Kungiyar Yakin Neman Zaben dan takarar Shugaban Kasa na jam’iyyar LP, Doyin Okupe. A cewar Tolu Babaleye, lauyan Okupe, an kama dan siyasar ne a filin jirgin saman Murtala Muhammed da ke Ikeja a Jihar Legas, a lokacin da yake kan hanyarsa ta zuwa Landan. Wata Babbar Kotun Tarayya da ke zamanta a Abuja, ta samu Okupe, mai bai wa tsohon Shugaban Kasa Goodluck Jonathan shawara kan Harkokin Jama’a, da laifin karkatar da kudaden makamai daga Ofishin mai bai wa Shugaban Kasa Shawara kan Harkokin Tsaro. Mai shari’a Ijeoma Ojukwu ta bayyana cewa, masu tuhuma sun gabatar da karar satar kudi a kan Okupe wanda aka ci shi tarar Naira miliyan 13. Jaridar Aminiya ta rawaito cewa, A shekarar 2019, Hukumar Yaki da Yi Wa Tattalin Arziki Zangon Kasa, ta tuhumi Okupe da laifuka 59 ciki har da wadanda suka shafi karkatar da kudi har Naira miliyan 240 daga hannun Sambo Dasuki. An gurfanar tare da shi tare da wasu kamfanoni biyu – Value T