Search This Blog

Friday, 31 March 2023

Gobara Ta Barke A Gidan PDP

 


Ga dukkan alamu gobara ta sake barkewa a gidan babbar jam’iyyar adawa ta kasar nan wato PDP, wadda ta sake shiga rudu, makonni kadan da faduwarta a zaben Shugaban Kasa.

A ranar Talata da ta gabata ce, Kwamitin Zartarwar Jam’iyyar na Kasa (NWC), ya ayyana Ambasada Iliya Umar Damagum a matsayin Shugaban Riko na jam’iyar ta kasa.

Kafin nadinsa, Alhaji Iliya Damagum shi ne Mataimakin Shugaban Jam’iyyar PDP na kasa Shiyyar Arewa.

Kakakin Jam’iyyar PDP, Debo Ologunagba ne ya bayyana nada Damagun a ranar Talata a wani taron manema labarai a Abuja.

A sanarwar da PDP ta fitar, ta ce ya zame mata dole ta yi biyayya ga umarnin wata kotu da ta bukaci Shugaban Jam’iyyar na Kasa Dokta Ayu Iyorchia ya daina bayyana kansa a matsayin shugaban jam’iyyar har zuwa lokacin da za ta yanke hukunci kan kararsa da aka kai gabanta.

Wata Babbar Kotu a Jihar Benuwai ce ta dakatar da Dokta Iyorchia Ayu daga shugabancin Jam’iyyar PDP ta Kasa.

Alkalin Kotun, Mai Shari’a W.I Kpochi ne ya bayar da umarnin a ranar Litinin bayan sauraron kunshin karar da aka shigar Mai lamba MHC/85/2023.

Tun a ranar Juma’ar da gabata Jam’iyyar PDP ta ce ta dakatar da Shugabanta na Kasa, Iyorchia Ayu bisa zarginsa da wasu ayyuka na cin amanar jam’iyyar.


Shugabannin jam’iyyar a matakin gundumarsa da ke Karamar Hukumar Gboko, a Jihar Benuwe ne suka dauki matakin.

Sun ce sun dakatar da shi ne bayan kada kuri’ar rashin kwarin gwiwa kan ayyukansa.

A lokacin da ya karanta matsayar da shugabannin suka cim ma, Sakataren Jam’iyyar a Gundumar Igyorob, Mista Banger Dooyum ya ce zagonkasa da Ayu da na kusa da shi suka yi wa PDP ne ya janyo mata shan kaye a gundumar da kuma jihar baki daya a zaben Gwamnan da aka yi a jihar.

Sun kuma zargi Ayu da rashin biyan kudaden da ake karba na shekara-shekara daga ’ya’yan jam’iyyar, kamar yadda dokokinta suka tanada.

hugaban Kungiyar, Terzungwe Atser ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar, inda a ciki ya ce ba zai taba yiwuwa jagororin jam’iyyar su dauki wannan mataki ba a yanzu ba tare da an tursasa su yin hakan ba.

Yanzu aka fara rigimar —Wike

A bangaren Gwamnan Jihar Ribas, Nyesome Wike ya ce yanzu aka fara rigimar siyasa a tsakaninsa da dakataccen shugaban na PDP, Dokta Ayu.

Ya ce hankali ba zai dauka ba a ce wanda ya kasa kawo mazabarsa a zabubbukan da suka gabata ya ci gaba da jagorantar PDP a matsayin Shugabanta na kasa.

Wike ya bayyana haka ne lokacin da yake kaddamar da makarantar Okoro-nu-Odo da ke Karamar Hukumar ObioAkpor da ya sabunta.

Ya ce, Allah ne kadai Ya san dalilin da Ayu ya kekeshe zuciyarsa ya ki sauka daga mukaminsa a lokacin da Gwamnoni 5 da ake kira G5 suka bukaci hakan bayan Atiku Abubakar ya zama dan takarar Shugaban Kasa a PDP.

Gwamna Wike ya ce da a ce lokacin da suka bukaci haka, Dokta Ayu ya amince ya sauka, da irin su da suka yi kokarin ganin an mayar da mulki Kudu sun yi amfani da wannan wajen samun sulhu, wanda a cewarsa watakila da hakan ya sa Jam’iyyar PDP ta samu nasara.

“Ku wadanda kuke cewa kun dakatar da Ayu, ba ku ma ga komai ba.

“Ayu, yanzu aka fara rigimar nan. Wadanda suke kusa da shi su fada masa cewa yanzu aka fara,” in ji Wike.

Duk da cewa ba yanzu aka fara yunkurin cire Ayu daga Shugaban PDP na Kasa ba, wannan karon lamarin ya yi karfi matuka domin a cikin shugabannin jam’iyyar da masu ruwa-da-tsaki an samu rabuwar kai kan cire shi.

Aminiya ta samu labarin cewa an fara yunkurin ganin bayansa ne kwanaki kadan bayan zaben Shugaban Kasa, inda Jam’iyyar PDP ta sha kaye a hannun Jam’iyyar APC, rashin nasarar da wasu suka alakanta da kin amincewa ya sauka daga mukaminsa.

Aminiya ta ruwaito yadda hayaki ya fara tashi a jam’iyyar bayan Atiku Abubakar ya doke Gwamna Wike na Ribas a zaben fid-da-gwan na takarar Shugaban Kasa.

Gwamna Wike da wasu gwamnoni hudu sun ware, inda suka kafa Kungiyar G5, wadda daga cikin bukatunta akwai batun cire Ayu a matsayin shugaban jam’iyyar.

A cewarsu, ba zai yiwu ba dan takarar Shugaban Kasa da Shugaban Jam’iyya su fito daga yanki daya, wanda hakan ya sa suka bukaci Ayu ya sauka, a musanya shi da wani daga Kudu.

Hakan ya sa PDP ta shiga zaben Shugaban Kasa ba tare da gwamnonin biyar tare da ita ba, ciki har da Wikem, Gwamnan Jihar Ribas wadda take kan gaba wajen ba PDP kuri’u a zabubbukan baya.

Aminiya ta samu labarin cewa wannan yunkurin ya kara zafi ne kasancewar shugaban ya kasa hada kan jam’iyyar kafin zabe da kuma gazawarsa wajen kawo wa PDP jiharsa a zaben Shugaban Kasa da na gwamnoni, duk da cewa ba sa ga maciji da Gwamnan jiharsa ta Binuwai daya daga cikin gwamnonin G5.

Wasu abubuwan da suka kara ta’azzara rikicin shi ne batun dakatar da wasu jiga-jigan Jam’iyyar PDP da suka hada da tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Anyim Pius Anyim da tsohon Gwamnan Jihar Ekiti, Ayo Fayose da tsohon Gwamnan Jihar Katsina, Ibrahim Shema kuma ta bukaci Kwamitin Ladabtarwa na Jam’iyyar da ya binciki Gwamna Ortom na Binuwai.

Jim kadan bayan dakatar da Shema ne ya fitar da sanarwa, inda a ciki ya bukaci ko dai a janye dakatarwa, ko ta zama takardar sallamarsa daga jam’iyyar, domin a cewarsa ba zai yiwu a dakatar da shi ba, inda kuma aka ce dole za a dakatar da shi, to zai bar jam’iyyar.

Daga cikin wadanda suke gaba-gaba wajen ganin an cire Ayu, akwai gwamnonin G5, wato Gwamna Nyesom Wike na Ribas da Samuel Ortom na Binuwei da Seyi Makinde na Oyo da Okezie Ikpeazu na Abiya da Ifeanyi Ugwuanyi na Enugu.

Akwai kuma wasu jigajigan jam’iyyar, ciki har da tsofaffin gwamnoni da suka hada da Ibrahim Shema da Cif Bode George da Ayo Fayose da sauransu.

Haka a cikin jagororin jam’iyyar, Aminiya ta samu labarin cewa an samu rarrabuwar kai a tsakaninsu, inda wasu suka amince a cire shi, wasu kuma suke tare da shi.

Akwai bayanan da suke cewa mai yiwuwa Dokta Ayu ya kalubalanci dakatar da shi da Kwamitin NWC ya yi a kotu, lamarin da ake jin zai kara rura wutar rikicin da ke cin jam’iyyar.

AMINIYA

Gwamnatin Kano Ta Yi Kira Ga Abba Kabir Yusuf Da Ya Jira A Rantsar Da Shi Sannan Ya Fara Bayar Da Umarni

Gwamnatin jihar Kano ta yi kira ga Injiniya Abba Kabir Yusuf da Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta ayyana a matsayin zababben gwamna da ya yi hakuri tare da daina fitar da sanarwa a hukumance ta hanyar ba da shawara ga jama’a domin kada a haifar da rudani da bai kamata ba a jihar.
 
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida, Malam Muhammad Garba ya fitar a ranar Juma’a a matsayin martani ga umurnin da ofishin zababben gwamnan ya fitar, inda ya gargadi mutane, kungiyoyi da kungiyoyi da suke gudanar da gine-gine a wuraren taruwar jama’a da su kiyaye. .

Ya ce matakin da zababben gwamnan ya dauka ya kai ga yin tsalle-tsalle ta hanyar bayar da umarni kan lamarin da ya shafi manufofin gwamnati yayin da mai ci bai cika cika wa'adinsa ba.

Malam Garba ya kuma bayyana cewa, dangane da batun rabon mukamai kamar yadda kundin tsarin mulkin tarayyar Najeriya ya tanada, Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya ci gaba da zama gwamna mai ikon zartarwa har zuwa ranar 29 ga watan Mayu kuma yana da hakkin gudanar da ayyukansa a maslahar jama'a ko a jajibirin fitowar sa.

“Har sai ya zama gwamna a ranar 29 ga Mayu, ya ci gaba da zama zababben gwamna kuma ba shi da ikon gwamna. Abin da kawai zai iya yi shi ne ya mayar da wasu ayyukan da magabata ya yi a lokacin da ya hau kan karagar mulki idan akwai kwararan dalilai na yin hakan. Sanarwar ta kara da cewa, babu wani zababben gwamnan da yake da ikon da kundin tsarin mulki ko doka ya ba shi na sanin alkiblar jihar har sai an rantsar da shi.

Kwamishinan ya bayyana cewa gwamnonin jihohi suna da iko da yawa wajen rabon filayen don haka kowace gwamnati ta yi irin wannan aiki ciki har da gwamnatin da ta shude wacce zababben gwamnan ya yi aiki.

Ya kuma bayyana cewa bisa ga bayanan da ake da su, gwamnatin da ta shude ta yi rabon filayen a wasu wuraren taruwar jama’a da zababben gwamnan ya ambata da suka hada da katangar birnin, tare da raba fili daga Kofar Nassarawa zuwa Kofar Mata; shaguna a filin Sallar Idi na kofar Mata da ke fuskantar gidan sinimar Orion da kuma daga Kofar Mata zuwa ‘Yan yashi daura da filin Idi da kuma daga Kofar Kabuga zuwa Kofar Famfo da ke fuskantar tsohon Campus na Jami’ar Bayero.

Malam Garba ya bayyana cewa shawarwarin da zababben gwamnan ya bayar ya haifar da tashin hankali a jihar inda ya shawarce shi da ya hakura da hakan domin gudun kawo rudani.

Ya kuma yi kira ga daidaikun mutane da kungiyoyi da suka mallaki fili bayan bin ka’idoji da tsare-tsare da kada a yi barazana da umarnin.


Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki

Zababben Gwamnan Jihar Kano Ya Sanar Da Kwamitin Karbar Mulki

…… Dr. Baffa Bichi, Abdullahi Musa ya nada a matsayin Shugaba da Sakatare

Bayan gabatar da takardar shaidar cin zabe da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC ta gabatar, zababben gwamnan jihar Kano Engr. Abba Kabir Yusuf (Abba Gida Gida) ya kaddamar da kwamitin sa na mika mulki a shekarar 2023.

A wata sanarwa da Sanusi Bature Dawakin Tofa, babban sakataren yada labarai na zababben gwamnan ya fitar, tsohon babban sakataren hukumar kula da manyan makarantu (TETFUND)  dan takarar Sanatan Kano ta Arewa a NNPP Dr. Abdullahi Baffa Bichi ya bayyana a matsayin shugaba na kwamitin mika mulki na Gwamna (GTC), yayin da babban sakataren dindindin, Abdullahi Musa mai ritaya a matsayin sakatare.

Kwamitin rikon kwarya zai gudanar da ayyukan mika mulki cikin tsari daga gwamnatin Ganduje mai barin gado zuwa gwamnatin Abba Gida Gida mai jiran gado.

Mai girma Gwamnan Jihar Kano mai jiran gado zai kaddamar da kwamitin a ranar Asabar 1 ga Afrilu, 2023 da karfe 2:00 na rana. Jadawalin Da ke ƙasa akwai cikakken jerin membobin Babban Kwamiti, yayin da za a sanar da ƙananan kwamitoci a sassa daban-daban da ƙananan sassa nan gaba.

Thursday, 30 March 2023

Zababben Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf, Ya Yi Kira Da A Dakatar Da Duk Wasu Gine-gine Da Ake Yi A Marantu, Makabarta da Kasuwanni

Zababben Gwamnan Jihar Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya bayar da umarnin a bayar da wannan Shawara ga Jama’a da duk daidaikun mutane, kungiyoyi da sauran kungiyoyi da suke ci gaba da gine-gine a wuraren taruwar jama’a cikin wata sanarwa da babban daraktan yada labaransa, Sunusi Bature Dawakin Tofa ya sanyawa hannu kamar kamar:

a. Ana shawartar ku da ku daina aikin gine-gine a filayen jama'a a ciki da kewaye: Dukkanin Makarantu na Jiha, duk wuraren addini da al'adu na jihar, duk asibitocin jihar, duk makabarta a cikin jihar, da kuma jikin Badalar Kano;

b. Ana kuma shawarce ku da ku daina rushewa, da kuma gina duk wasu gine-ginen gwamnati na gwamnati da jama'ar jihar Kano;

c. An bayar da wannan Shawarar ne domin amfanin jama'a, daga yau Alhamis 30 ga Maris, 2023 har zuwa sanarwa ta gaba. Duk wani wanda ya sabawa haka  yana yin haka duk abun da ya faru shi ya jawo



Bashin Da Ake Bin Najeriya Ya Karu Zuwa Naira Tiriliyan 46.25 - DMO

Ofishin Kula da Basussuka na Kasa (DMO) ya ce bashin da ake bin Najeriya ya karu zuwa Naira tiriliyan 46.25 a watan Disamban 2022.

A wata sanarwa a ranar Alhamis, DMO ya ce an samu karin sama da Naira tiriliyan bakwai daga abin da kasar ta mallaka a shekarar 2021.

Kano: Ba zan rika yi wa gwamnatin Abba katsa-landan ba – Kwankwaso
Masari: Tinubu na bukatar addu’a
“Jimillar Bashin Jama’a wanda ya kunshi bashin cikin gida da na kasashen waje na Gwamnatin Tarayya da kananan hukumomi daga (Gwamnatin Jihohi 36 da Babban Birnin Tarayya), ya kai Naira Tiriliyan 46.25 ko kuma dala biliyan $103.1, kwatankwacin adadin ranar 31 ga watan Disamba, 2021, na Naira tiriliyan 39.5 wanda ya yi daidai dad ala biliyan $95.77.

“Ta fuskar hada-hadakuwa, jimillar bashin cikin gida ya kai Naira tiriliyan 27.55 daidai da dala biliyan $61.42, yayin da jimillar bashin waje ya kai Naira tiriliyan 18.7t daidai da dala biliyan $41.6.


Ofishin ya bayyana cewa dalilan da suka sa aka kara samun yawan bashin gwamnati; su ne sabbin rancen da Gwamnatin Tarayya da na kananan hukumomi suka yi, na farko, don samar da gibin kasafin kudi da aiwatar da ayyuka.

“Bayar da bayanan lamuni da gwamnati ta yi don daidaita wasu lamura shi ma ya ba da gudunmawa wajen karuwa bashin.”

Sai dai ta ce kokarin da gwamnati ke ci gaba da yi na kara samun kudaden shiga daga albarkatun mai da wadanda ba na mai ba ta hanyar tsare-tsare irin su Dokar Kudi da kuma dabarun tattara kudaden shiga na iya tallafawa dorewar bashi.
AMINIYA 

Zababben Gwamnan Kano Ya Nada Tsohon Dan Jarida, Sanusi BatureBabban Sakataren Yada Labaransa

Zababben Gwamnan Jihar Kano H.E. Engr. Abba Kabir Yusuf ya bayyana Sunusi Bature Dawakin Tofa a matsayin babban sakataren yada labaran sa na lokacin mika mulki.

A cikin wata takarda mai dauke da sa hannun shugaban kwamitin mika mulki na gwamna a madadin gwamnan jihar, mai girma gwamna ya bayyana nadin na Bature a matsayin wanda ya dace da shi a bisa cancantarsa ​​da rikon amana da jajircewarsa da kwazonsa da ya nuna tun 2019.

Sunusi kwararre ne a fannin yada labarai da hulda da jama’a sadarwar ci gaba da ƙwararrun masu ruwa da tsaki tare da gogewar shekaru 19 na aiki a cikin ci gaban ƙasa da ƙasa, kamfanoni masu zaman kansu da kuma Media a Najeriya.

Shi ne wanda ya lashe lambar yabo ta ilimi ta Cambridge kan aikin jarida a 2008, Bature ya yi aiki a wurare daban-daban a kungiyoyi daban-daban na kasa da kasa da na kasashen biyu kamar Ofishin Harkokin Waje da Kasuwanci na Burtaniya (FCDO), Hukumar Ci Gaban Cikin Gida ta Amurka (FCDO). USAID), Bill da Melinda Gates Foundation, Save the Children International, Discovery Learning Alliance da kuma Gidauniyar Rockefeller.

Ya rike mukamai da dama wadanda suka hada da General Manager Corporate Services a Dantata Foods and Allied Products Limited (DFAP), Director Stakeholder Engagement at YieldWise Project, Country Program Manager at Girl Rising (ENGAGE) Project wanda Gwamnatin Amurka ta ba da tallafi, Mai Gudanar da Ayyukan Jiha na MNCH Campaign. Ayyukan BMGF, Mataimakin Darakta Ayyuka a Ƙwararrun Ƙwararrun Ƙwararru, Jami'in Shirye-shiryen Jiha, Ƙwararrun Siyasa da Ci Gaban Watsa Labarai, Sadarwa da Ƙwararrun Gudanar da Ilimi a tsakanin sauran mukamai.

Sanusi ya kammala digirinsa na farko (B.A. Hons.) a Mass Communication a Jami’ar Maiduguri, ya yi Diploma na kasa kan Mass Communication a Kaduna Polytechnic, Diploma Higher National Diploma (HND) da Difloma a fannin Ilimin Kiwon Lafiyar Jama’a da Ci gaba.

Ya kuma yi digiri na biyu . a cikin Ayyukan zamantakewa tare da ƙwarewa a Ci gaban Al'umma daga Jami'ar Fasaha ta Ladoke Akintola, (LAUTECH) Ogbomosho, Jihar Oyo da kuma wani digiri na biyu a Harkokin Jama'a (MPR) daga Jami'ar Bayero mai daraja, Kano, Nigeria. Ya shiga cikin shirin MSc akan Gudanar da Ayyuka a Kwalejin Robert Kennedy, Zurich, Switzerland.

Har zuwa lokacin da aka nada shi, Sunusi Bature ya rike mukamin mataimakin shugaban kasa a Najeriya a wani kamfani mai suna Kingston Organic PLC da ke Burtaniya.

Wednesday, 29 March 2023

Yanzu-Yanzu: Nasiru Gawuna Ya Taya Abba Gida-gida Murnar Lashe zaɓen Gwamnan Kano

Mataimakin Gwamnan Jihar Kano Kuma wanda ya yiwa jam’iyyar APC takarar gwamnan jihar kano a jam’iyyar APC Dr. Nasiru Yusuf Gawuna ya ce ya karɓi Kaddarar faɗuwa zaɓe tare da taya Abba Kabiru Yusuf Murnar lashe zaɓen gwamnan Kano.

Nasiru Gawuna ya bayyana hakan ne cikin wani sakon murya da yayi bayani na tsawon mintuna biyu, wanda Sakataren yada labaran sa Hassan Musa Fagge ya aikowa kadaura24.


” Mun tsammaci Hukumar Zabe INEC zata duba koken da mukai mata na samun kura-kurai a sakamakon zaben da ya gudana, amma a yau 29 ga watan maris ta sake tabbatar da matsayar ta ta hanyar mikawa Abba Kabiru Yusuf Shaidar lashe zabe , don haka mun dauki wannan a matsayin kaddara”. Inji Gawuna


 
Yace dama ya fada a baya cewa zai karɓi Kaddara idan ya fadi zaben don haka yayi kira ga magoya bayan sa da dukkanin al’ummar jihar kano da zu baiwa sabon zaɓaɓɓen gwamnan hadin kai don ya gudanar da mulkin sa cikin kwanciyar hankali da lumana.

 
Mataimakin Gwamnan ya kuma yi addu’ar Allah ya kamawa Sabon zababben gwamnan, sannan yayin addu’ar Allah ya bashi ikon yiwa al’ummar jihar kano adalci a Shugabanci sa.
KADAURA24 


Tuesday, 28 March 2023

Zababben Gwamnan Jihar Kano Abba Kabir Yusuf na ya al'ummar Kano domin su Karbar Shaidar Cin Zabensa

Zababben Gwamnan Jihar Kano, Engr. Abba Kabir Yusuf, wanda aka fi sani da Abba Gida Gida yana gayyatar dumbin magoya bayansa, mambobin jam'iyyar NNPP da kuma manyan masu ruwa da tsaki, zuwa gabatar da takardar shaidar cin zabe ga dukkan 'yan takarar da suka ci zabe a ranar Asabar 18 ga wata.

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) a Kano ta shirya ranar Laraba 29 ga Maris, 2023 da karfe 10 na safe a sakatariyar INEC don bayar da shaidar cin zabe ga zababben gwamna da mataimakinsa da ‘yan majalisar jiha.

Kakakin zababben gwamnan jihar Kano, Sanusi Bature Dawakin-Tofa, a wata sanarwa a ranar Talata ya ce za a gudanar da taron ne a dakin taro na INEC da karfe 10:00 na safe.

Ya kuma bukaci magoya bayan jam’iyyar NNPP da duk wadanda aka gayyata, wadanda suka shahara da son zaman lafiya da bin doka da oda, da su rika gudanar da harkokinsu cikin tsari a lokacin bikin da kuma bayan bikin, tare da yi wa kowa fatan alheri.

SABATURE

Monday, 27 March 2023

Hajj 2023: NAHCON, Hukumar Alhazai Na Jihohi Zasu Hada Gwiwa Don Zabar Masauki Masu Inganci

Gabanin bayyana kudin aikin Hajjin shekarar 2023, Hukumar Alhazai ta Najeriya (NAHCON) ta dorawa Hukumomin Alhazai na Jihohi (SMPB) damar samun matsuguni masu inganci kawai domin rage kudin Hajjin 2023.

NAHCON ta bayyana haka ne a yayin wani taro tsakanin shugabannin hukumomin Alhazai na jahohi da masu samar da masauki da kuma masu aikin hajjin 2023 da aka zabo masu ba da abinci a karo na biyu kafin aikin hajji a ranar Lahadi a birnin Makkah na kasar Saudiyya.

“Eh, kwamishinan kudi na NAHCON wanda ya jagoranci taron ya roke mu da mu nemo masaukai masu inganci da ba shi da nisa da babban masallacin Makkah amma ya kamata a rage farashi.

‘’Farashin masauki a Makkah ya tashi saboda dalilai kamar haka: Masarautar Saudiyya ta fara rusa wasu gidaje da alhazan Najeriya ke amfani da su a baya don share fagen sabon shirinsu na ci gaba.

“Ba kamar a shekarar 2022 da mahajjata miliyan daya kacal suka yi aikin hajji ba, sama da mahajjata miliyan 3 ne ake sa ran za su yi aikin hajji a bana – wanda ke nufin karin yawan mahajjata da karancin masauki. Haƙiƙa, yana da ƙalubale a gare mu jahohi amma za mu yi aiki tuƙuru don ganin yadda za mu iya tafiya,” wata majiya mai ƙarfi ta shaida wa manema labarai na Hajji a Makkah.

Binciken da masu aiko da rahotannin alhazai suka yi ya nuna cewa a yanzu haka an ruguje akasarin  otal-otal da ke kan titin Hijra a Misfala yayin da wasu kuma hukumar masarautar Makkah da wuraren tsarki ta Saudiyya ta ruguza su.

Mahajjata daga jihohin Sokoto, Katsina, Kaduna, Bauchi, Kano, Kwara, Plateau da Niger suna karbar maniyyatan su ne a cikin garin Misfala ta hanyar Hijira da Ibrahim Khalil Road a Makkah.

An dage aikin duba masauki da kicin da aka shirya tun karfe 10:30 na rana zuwa karfe 5 na yamma agogon Saudiyya a yau.

Lokaci na duba ya canza saboda yawan zirga-zirga a kewayen Harami musamman bayan sallar tarawihi.
IHR

Saturday, 25 March 2023

Hajj2023: Tawagar Hukumar NAHCON Sun Gudanar Da Taron Cikin Gida A Yayin Ziyararsu Zuwa Makka

Tawagar Hukumar Alhazai ta Najeriya (NAHCON) a yayin da suke kasar Saudiyya sun gudanar da taronsu na farko na cikin gida don a yayin ziyara kafin aikin Hajji karo na biyu a shirye-shiryen gudanar da aikin Hajjin shekarar 2023 a ofishin NAHCON dake Ummuljud Makka 

Tawagar tana da alhakin ayyuka kamar haka:

1) Duba dakunan dafa abinci na Makkah da Madina.
2) Tattaunawar kwangila tare da masu gudanar da ayyuka 
3) Don gudanar da tarurruka tare da AHOUN, Jihohi, Muassasah, masu ba da masu bayar da  masauki,
4) Horon E-track da 5) Rahoton ƙarshe ..

Taron ya gudana karkashin jagorancin Kwamishinan kudi Alhaji Nura Hassan Yakasai wanda shi ma ya jagoranci tawagar da ta samu rakiyar wakilan CBN da Jama’atu Nasril Islam da kwamishinan yankin Kudu
Daga cikin yan tawagar a taron: Sun hada da Daraktan Gudanarwa da HR, Darakta harkokin shari'a, Mataimakin Darakta PEO, sauran Daraktoci da manyan ma'aikatan gudanarwa.
NAHCON 

Monday, 20 March 2023

Sanata Uba Sani Ya Samu Nasarar Zama Gwamnan Kaduna

An bayyana dan takarar jam’iyyar All Progressives Congress (APC) Sanata Uba Sani a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan jihar Kaduna a shekarar 2023.



Jami’in kula da masu kada kuri’a na jihar Kaduna kuma mataimakin shugaban jami’ar Usman Dan Fodio Sokoto, Farfesa Lawal Suleiman Bilbis ne ya bayyana shi a matsayin wanda ya lashe zaben.



Sani ya samu kuri'u 730,002 inda ya kayar da babban abokin hamayyarsa Isa Ashiru na jam'iyyar PDP wanda ya samu kuri'u 719,196.


Dan takarar jam’iyyar Labour Party (LP), Jonathan Asake ya zo na uku mai nisa bayan ya samu kuri’u 58,283 yayin da dan takarar jam’iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP), Suleiman Hunkuyi ya samu kuri’u 21,405.

Sunday, 19 March 2023

Hukumar Zabe Ta Sanar Da Abba K Yusuf A Matsayin Wanda Ya Lashe Zaben Gwamnan Kano

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa INEC ta bayyana Abba Kabir Yusuf na jam'iyar NNPP  a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan Kano da aka kammala kwanan nan da kuri'u 1,019,602.

Thursday, 16 March 2023

Za Mu Kama Duk Wanda Ya Dauki Makami Ranar Zabe A Kano —’Yan Sanda

 


Mataimakin babban sufeto-Janar na ’yan sanda DIG Hafiz Muhammad Inuwa da ke kula da harkokin zaben shekarar 2023 a yankin jahohin Arewa maso Yammacin Najeriya, ya gargadi ’yan siyasa da magoya bayansu, da su kauce wa yin wani abu da zai tada hankulan masu zabe. 

DIG Hafiz M. Inuwa ya bayyana cewa shugaban ’yan sanda Usman Alkali Baba ya umarce su, da su gargadi ’yan siyasa da masu ruwa da tsaki da su ja wa magoya bayansu kunne gabanin zaben da ke tafe a ranar Asabar 18 ga watan Maris 2023.

Ya bayyana hakan ne a Jihar Kano, a ci gaba da shirye-shirye da rundunar ke yi na tabbatar da tsaro da kare rayukan al’umma da kuma dukiyoyinsu.

Ya kara da cewa fatansu, shi ne a yi zabe lafiya a kammala lafiya, ba tare da nuna siyasa da gaba ba.“Duk wani dan siyasa in dai yana son ci gaban Kano, to zaman lafiya shi ne ci gaban, so ake a zauna lafiya.

“Kuma na zo da jawabi, in gargade su, Wallahi ba za mu yi kasa a gwiwa ba wajen maganin duk wani da ya nemi ya tada fitina,

“Saboda haka ina tabbatar muku da cewa duk wanda ya nemi ya dau makami ko don ya hana wani fitowa zabe, ko don ya jikkata wani, to Wallahi Tallahi fushin hukuma ne a tattare da shi” in ji shi.Ya ce ba zu raga wa kowa ba duk girmansa kowaye , domin ci gaban Nijeriya da ci gaban Kano da kuma zaman lafiya shi ne agaban mu.

Tun kafin wannan lokacin ne Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya bayyana cewa sun tanadi ’yan sanda masu yawa don tabbatar da tsaro a zaben ranar 18 ga watan Maris 2023.

Sai Buhari Ya Yi Magana Za Mu Karbi Tsohon Kudi —’Yan Kasuwa


 ’Yan kasuwa a wasu yankunan Najeriya sun bayyana cewa ba za su fara karbar tsoffin takardun N5oo da N1,000 har sai sun ji Shugaban Kasa Muhamamdu da bakinsa ya ce su fara karba.

’Yan kasuwa da kwastomominsu jihohin Kaduna da Legas da kananan hukumomin Abaji da Kwali a Yakin Babban Birnin Tarayya na kin karbar tsoffin kudin ne, a washgarin da bankunan kasuwanci suka fara bayar da su, bisa umarnin Babban Bankin Najeriya (CBN).

Sai dai a Jihar Kano, harkokin kasuwanci sun fara komawa yadda aka saba, tun bayan da bankuna suka fara bayar da tsoffin kudi, kuma mutane suka ci gaba da amfani da su a harkokin kasuwanci.

Harkoki sun fara kankama a Kano

Wani tan kasuwa a Kasuwar Kantin Kwari da ke Kano, Adamu Hamza, ya ce sun fara samun karuwar ciniki,  “tsakanin jiya (Talata) da yau (Laraba), kudi ya fara yawo a hannun jama’a, suna kawowa kuma muna karba.”

Aminiya ta ruwaito cewa tun ranar Talata injinan ATM a birnin Kano suka fara bayar da tsoffin kudin, sai dai yawanci N500 ne.

Haka kuma an samu raguwa mutane da ke neman cirar kudi, dai dai wasu bankunan sun bayyana cewa tsabar kudin da ke hannunsu  ya kare, shi ya sa ba a ganin layin mutane a ATM dinsu domin cirar kudi.

‘Sai mun ji daga bakin Buhari’

Aminiya ta zaiyarci yankin Abaji a ranar Laraba, inda ta iske mutane na ta gunaguni cewa bankuna sun koma ba wa mutane tsoffin takardun kudin.

Wani dan kasuwa, Bashir Aliyu, ya yi mana korafin cewa ya ce cikin banki cirar kudi , amma aka ba shi tsoffin takardun N1,000 da aka sauya, amma ya ki karba, sabo ba zai iya kashe su cikin sauki ba, idan ya je kasuwannin kauye.

A cewarsa, duk da cewa CBN ya ba umarnin bankuna su ci gaba da harkokinsu da tsoffin kudin, shi ba zai samu natsuwa ba sai sai ya ji Shugaba Buhari da kansa ya yi wa ’yan kasa magana cewa su ci gaba da amfani da tsoffin kudin.

Wani jami’in banki da ya nemi mu boye sunansa ya shaida mana cewa bankin ya fito da Naira dubu 500 na tsoffin takardun kudi da yake da su domin ba wa mutanen da suka zo cirar kudi, amma yawancin mutanen sun ki karba.

“A takaice, daga cikin N500,000 da bankin ya fitar domin ba wa kwastomomi N150,000 kadai aka samu wadanda karba,” in ji jami’in bankin.

Hakazalika wasu ’yan kasuwa a yankin Kwali na kin karbar tsoffin kudin, saboda har yanzu ba su ji Shugaba Buhari ya yi magana a kai ba.

Wata ’yar kasuwa mai suna Misis Laraba Gwatana ta ce, “Ni ba zan karbi tsohon kudi ba, saboda har yanzu rade-radi muke ji cewa CBN ya umarci bankuna su koma bayar da tsoffin kudaden.

“Amma ni dai ba zan karbe su ba, sai lokacin da na ji Buhari ya fito ya yi wa ’yan Najeriya jawabi cewa su rika karbar tsoffin kudin; gaskiya ba wanda ke so ya kara yin asara.”

’Yan kasuwa kaduna ma haka

Zuwa ranar Laraba, ’yan kasuwa da dama a Jihar Kaduna na kin karbar tsoffin takardun N500 da N1,000 a Kasuwar Sheikh Gumi, inda suke bayyana fargaba kan batun amfani da tsoffin kudaden.

Wakilinmu ya lura cewa maimakon karbar tsoffin kudaden, ’yan kasuwa da dama sun tanadi na’uarar tura kudi ta PoS ga kwastomominsu.

Wani dan kasuwa mai sayar da kayan gwari, Malam Lawal Ibrahim, ya shaida wa Aminiya cewa, “ban fara karbar tsoffin takardun N500 da N1,000 tukuna; amma ina karbar tsohuwar N200.”

Ya ce dalilinsa shi ne, “Gwamnati na ta kumbiya-kumbiya, don haka ina tsoron in karba, daga baya CBN ya ce ya canza shawara a bar ne da asarar biyan kudin kaya, shi ya sa ba na karba.”

Mohammed Isa mai kayan gwari shi ma ya ce, gara ya ki karbar tsoffin kudaden da ya bari su ja masa asara.

“Lokacin da aka fara cewa mu kai tsoffin kudin CBN, sai da na yi kwanaki a kofar CBN don in ajiye N100,000. Shi ya sa na yi wa kaina riga-kafi, da in yi asara gara kaya na sun yi kwantai.”

Yankin Kudu

Wannan yanayi haka yake a wasu sassa na Jihar Legas, inda bakuna suka fara bayar da tsoffin kudin, amma na dar-dar wajen yin cinikayya da su, duk kuwa da umarnin CBN na ci gaba da amfani da su zuwa ranar 31 ga watan Disamba.

A Jihar Ribas kumma, manyan shaguna da gidajen mai da wasu wuraren kasuwanci na ci gaba da harkokinsu da tsoffin kudin.

Sai dai an korafi cewa duk da cewa bankuna na bayar da tsofifn kudaden, amma idan aka kai musu ba sa amsa.

Wata mazauniyar garin Fatakwal, Amaka Ike, wadda wakilinmu ya zanta da shi ya ce, ta ce da kyar ta iya yin sayayya da tsofifn kudaden.

Amaka ta ce, “wasu masu shaguna, gidajen mai da wasu ’yan kasuwa ba sa karbar tsoffin kudaden saboda a cewarsu, har yanzu ba su natsu ba, gwamnati za ta iya sauya shawara a kowane lokaci, kan batun.”

AMINIYA

DSS ta kama mutum biyu a Kano kan zargin tayar da rikici

 


Hukumar tsaro ta farin kaya DSS ta ce ta kama wasu mutane biyu da take zargi da tunzura mutane domin tayar da hankali a jihar Kano gabanin zaɓen gwamna da na ‘yan majalisun jiha da za a yi a ranar Asabar.

 

Cikin wata sanarwa da ta wallafa a shafinta na Twitter hukumar ta DSS ta ce mutanen sun naɗi hoton bidiyo ne da suke bayanan tunzura jama’a a cikinsu, sannan suka riƙa wallafa shi a shafukan sada zumunta.

 

Ta kuma wallafa sunayen Sharu Abubakar Taɓule mai shekara 37 a duniya, da kuma Isma’il Iliyasu Mnagu mai shekara 51 a matsayin waɗanda ta kama.

 

“Cikin waɗannan saƙonnin masu haɗari, sun nuna jam’iyyar siyasar da suke goyon baya kuma suka yi kira ga magoya bayansu su kai wa abokan hamayyarsu hari duk inda suka gansu.

 “Waɗanda ake zargin sun yi kira da a kai wa jami’an tsaro hari yayin zaɓen gwamnoni da na ‘yan majalisar jihohi da za a yi a ranar Asabar.


“Wata jam’iyyar siyasa a Kano na barazanar shirya zanga-zanga a sakamakon shirin kai hare-haren,” in ji hukumar ta DSS.


Sanarwar ta ƙara da cewa jam’iyyar siyasar ta shirya kutsawa ofisoshin wasu hukumomin tsaro a ranar 16 ga watan Maris a matsayin nuna goyon baya ga waɗanda ake zargin.“Yayin da hukumar ke sanar da mutane kan wannan haramtaccen mataki, ta kuma yi kira ga jam’iyyar da ta dakatar da wannan lamari, ko kuma ta shirya yaba wa aya zaƙinta.


“DSS ba za ta zuba ido tana kallon mutane suna tunzura al’umma ba su tayar da hankali da rashin tsaro a jiha ba.”


Sanarwar DSS ta ce za ta haɗa hannu da sauran hukumomin tsaro domin tabbatar da an samar da cikakken tsaron da zai bayar da damar da gudanar da zaɓe mai inganci a jihar.


Baya ga Kano hukumar tsaron ta kama wasu mutane da ke irin wannan kiraye-kiraye a wasu jihohi a faɗin ƙasar.


Hukumar ta shawarci jam’iyyun siyasa a fadin Najeriya da su gargadi mabiyansu su zama masu bin doka da oda, domin tabbatar da dimokuraɗiyya ta samu wurin zama yadda ya kamata


BBC

Tuesday, 14 March 2023

‘Kusan Sau Miliyan 13 Aka Yi Yunkurin Yi Wa Najeriya Kutse Yayin Zaben Shugaban Kasa’


 Gwamnatin Tarayya ta ce akalla sau 12,988,978 aka yi yunkurin yin kutse a shafukan intanet na Najeriya yayin zaben Shugaban Kasa da na ’yan Majalisun Tarayya da aka yi a ranar 25 ga watan da ya gabata.

Hare-haren, a cewar gwamnatin an kai su ne daga ciki da wajen kasar, kuma an yi su ne kan shafukan gwamnati, kusan sau 1,550,000 a kullum.

Ministan Sadarwa, Isah Ali Pantami ne ya sanar da hakan a cikin wata sanarwa ranar Talata.

To sai dai ya ce yunkurin kutsen ya yi tashin gwauron zabo zuwa sau 6,997,277, a ranar zaben Shugaban Kasa ta Asabar.

Ministan ya kuma ce ma’aikatarsa ta kafa wani kwamitin yaki da irin wadannan hare-haren, kuma ya fara aiki ne ranar 24 ga watan na Fabrairu, sannan ya kammala ranar 28.

AMINIYA

Sufeto Janar Ya Sake Turo Usaini Gumel A Matsayin Sabon Kwamishinan 'Yan Sanda Na Kano


Sufeto Janar na ‘yan sanda, Usman Alkali, ya sake soke turo kwamishinan ‘yan sandan Kano.

A wata sanarwa da aka fitar a ranar Litinin, Sufeto Janar din ya soke aika Feleye Olaleye a matsayin kwamishinan ‘yan sandan Kano tare da sanya CP Ahmed Kontagora a matsayin wanda zai maye gurbinsa.

Sai dai a wata siginar da aka sake fitarwa a daren jiya, sufeto janar din ya nada CP Usaini Gumel a matsayin wanda zai jagoranci rundunar 'yan sanda ta Kano lokacin zabukan gwamnoni da na ‘yan majalisar jiha a jihar.

A ranar 8 ga Maris, bayan zanga-zangar da ‘yan adawa suka yi, IGP ya sauya matakin da aka tura CP Balarabe Sule, tsohon babban jami’in tsaro ga gwamnan jihar Kano, Abdullahi Ganduje, a matsayin wanda zai maye gurbin CP Mohammed Yakubu

A cikin sabuwar takardar da aka fitar mai dauke lamba TH.5361/FS/FHQ/AB3/SUB.6/146, Mista Alkali kuma ya sake yin wasu ƙananan canje-canje a cikin umarnin.

IGP ya umurci DCP Auwal Musa da ya karbi DCP Nuhu Darma a matsayin mataimakan kwamishinan ‘yan sanda mai kula da ayyuka da binciken manyan laifuka (CID)

Daily Nigerian 

Dokar Zabe Ta Inganta Zabukan Najeriya —Fadar Shugaban Kasa

 


Fadar Shugaban Kasa ta ce zabukan da aka yi na Shugaban Kasa da ’yan Majalisar Dokokin Tarayya a ranar 25 ga watan Fabarairu, sun inganta ne albarkacin Dokar Zabe ta 2022.

Mai magana da yawun Shugaban Kasa, Malam Garba Shehu, ya ce albarkacin Dokar Zabe, an samu gagarumin ci gaba idan aka kwatanta da zabukan da aka yi a kasar a baya.

A sanarwa da kakakin shugaba Buhari ya fitar, fadar ta ce duk da cewa an samu wasu matsaloli nan da can, wannan ba zai sa a ce zaben ya gaza ba.

Fadar shugaban ta nuna godiya kan damuwar da manyan jagororin masu sanya ido na kasashen waje musamman tsoffin jakadu; Mark Green da Johnnie Carson suka nuna a kanmatsalolin da aka samu kan kayan aiki a lokacin zabukan.Sanarwar ta ce duk da ’yan matsalolin da aka samu ba za a ce zaben ya gaza ba, illa dai wadanda suka fadi ne suke nuna gazawarsa.

Kakakin ya ce zaben na Najeriya ba shi kadai ba ne ake samun ire-iren wadannan matsaloli abu ne da kusan a kowa ce kasa ake iya samu a zabe.

Malam Garba ya ci gaba da cewa “ko ba komai, yadda Ma’aikatar Harkokin Waje ta Amurka da Firaministan Birtaniya, Rishi Sunak da sauran shugabannin Afirka ta Yamma da na Tarayyar Afirka suka taya murna ga dan takarar APC Bola Ahmed Tinubu, wanda ya yi nasara a wannan zabe da ya kasance wanda aka fi fafatawa a tarihin Najeriya, hakan ya nuna cewa abin a yaba ne“Tabbas Dokar Zabe ta 2022 ta inganta zaben, la’akari da yadda na’urar tantance masu zabe BVAS ta kawo karshen aringizon kuri’u da duk wata cuwa-cuwa wajen kada kuri’a.”

AMINIYA

Monday, 13 March 2023

Labari da dumiduminsa : Bankin CBN Ya Ce Za A Ci Gaba Da Amafani Da Tsofaffin Kudi Na Har Zuwa 31 Ga Disamba


Babban Bankin Najeriya (CBN) ya ce tsofaffin takardun kudi na N200, N500 da N1000 suna nan a kan doka har zuwa ranar 31 ga Disamba, 2023.

Kakakin CBN, Isa Abdulmumin ne ya sanar da hakan a wata sanarwa da ya fitar a yammacin ranar Litinin.

“A bisa bin ka’idar da aka kafa ta bin umarnin kotu da kuma biyan ka’idar bin doka da oda da gwamnatin shugaban kasa Muhammadu Buhari ta yi, da kuma karawa ayyukan Babban Bankin Najeriya (CBN), a matsayin mai kula da Deposit. An umurci bankunan kudi da ke aiki a Najeriya da su bi hukuncin da kotun koli ta yanke na ranar 3 ga Maris, 2023,” in ji sanarwar.


“A bisa haka, CBN ya gana da kwamitin ma’aikatan banki inda ya ba da umarnin cewa tsofaffin takardun banki na N200, N500 da N1000 su ci gaba da zama a kan takardar kudi tare da sake fasalin kudin har zuwa ranar 31 ga Disamba, 2023.

Shugaba Buhari Yace, Bai Umarci Atoni Janar Da Gwamnan CBN Kan Kin Bin Umarnin Kotu Ba Dangane Batun Tsofaffin Kudi

 
Fadar shugaban kasa na son mayar da martani kan wasu damuwar da jama’a ke ciki na cewa shugaban kasa Muhammadu Buhari bai mayar da martani ga hukuncin da kotun koli ta yanke kan batun kudin tsohon naira 500 da naira 1,000 ba, kuma ta bayyana a nan karara da cewa babu wani lokaci da ya umurci Babban Lauyan gwamnati da Gwamnan CBN su bijirewa duk wani umarnin kotu da ya shafi gwamnati da sauran bangarorin.

A sanarwar da babban mataimaki na musamman ga shugaban kasa kan harkokin yada labarai, Malam Garba Shehu ya fitar, ta ce, tunda aka rantsar da shugaban kasa a shekarar 2015, bai taba umurtar kowa da ya bijirewa umarnin kotu ba, bisa akidar cewa ba za mu iya gudanar da mulkin dimokuradiyya ba tare da bin doka da oda ba, kuma jajircewar gwamnatinsa kan wannan ka’ida ba ta canja ba.

Bayan zazzafar muhawarar da ake ta yi game da bin doka da oda dangane da halaccin tsohon takardun kudin, don haka fadar shugaban kasar na son bayyana karara cewa Shugaba Buhari bai yi wani abu da gangan ba na tsoma baki ko kawo cikas ga gudanar da shari'a.

Shugaban kasa ba karamin Shugaba ba ne, don haka ba zai hana babban lauyan gwamnati da gwamnan babban bankin kasar CBN yin cikakken bayanin ayyukansu kamar yadda doka ta tanada ba. A kowane hali. ana tafka muhawara a wannan lokaci idan aka samu hujjar kin amincewa da gangan da su biyun suka yi bisa umarnin kotun koli.

Umarnin shugaban kasa, bayan taron majalisar jiha. shi ne dole ne Bankin ya samar da duk kudaden da ake buƙata don rarrabawa kuma babu abin da ya faru da ya canza matsayi.

Tabbatacciyar hujja ce cewa
 Shugaban kasa cikakken mai mutunta tsarin shari'a ne da ikon kotuna. Babu wani abu da ya yi a cikin shekaru takwas ko fiye da suka gabata don yin ta kowace hanya don kawo cikas ga gudanar da shari'a, haifar da rashin amincewa da gudanar da shari'a, ko yin katsalandan ko lalata kotuna kuma babu wani dalilin da zai sa ya yi. don haka yanzu lokacin yana shirin barin ofis.

Mummunan yakin neman zabe da hare-haren da ‘yan adawa ke kaiwa shugaban kasa da duk wani nau’in masu sharhi ba daidai ba ne da kuma rashin adalci, domin babu wani umarnin kotu a kowane mataki da aka ba shi ko kuma aka ba shi umarni.

Dangane da tsarin rashin kudi da CBN ya kuduri aniyar samar da shi, sanannen abu ne cewa da yawa daga cikin ‘yan kasar da ke fama da wahalhalun da ake fama da su, abin mamaki suna goyon bayan manufar ganin cewa matakin zai dakile cin hanci da rashawa, da yaki da ta’addanci. gina yanayi na gaskiya da kuma karfafa jagoranci marar lalacewa na shugaban kasa.

Don haka ya dace a dora wa Shugaban kasa alhakin cece-kucen da ake fama da shi a halin yanzu kan karancin kudi, duk kuwa da hukuncin da Kotun Koli ta yanke. CBN ba ta da dalilin kin bin umarnin kotu bisa uzurin jiran umarni daga shugaban kasa.

Shugaba Buhari ya kuma yi watsi da ra'ayin cewa ba shi da tausayi, yana mai cewa "babu wata gwamnati a tarihinmu na baya-bayan nan da ta bullo da tsare-tsare don taimakawa masu rajin tattalin arziki da marasa galihu kamar wannan gwamnati mai ci."
 

Saturday, 11 March 2023

Dan Jarida Ya Mutu Yana Tattakin Zuwa Wurin Aiki Saboda Karancin Takardun Kudi

 


Wani fitaccen dan jarida da ke aiki a gidan rediyon Ibadan, ya riga mu gidan gaskiya a kan hanyarsa ta zuwa wurin aiki a safiyar wannan Asabar din.

Ma’aikacin jaridar wanda aka fi sani da Baba Bintin, ya yanke jiki ne ya fadi matacce kamar yadda wakilinmu ya ruwaito.

Bayanai sun ce lamarin ya faru ne yayin da Baba Bintin ke hanyarsa ta zuwa gidan rediyon Fresh FM, inda zai gabatar da wani shiri tare da wasu takwarorinsa, Komolafe Olaiya da Olalomi Amole a yankin Challenge da ke Ibadan, babban birnin Jihar Oyo.

Baba Bintin dai ya shahara wajen gabatar da shirin bayyana farashin kayayyaki da ranakun cin kasuwannin yau da kullum a fadin jihar da kewaye.

Jama’a a Najeriya na ci gaba da babatu kan halin kunci da suka shiga tun bayan sauya fasalin takardun kudi da Babban Bankin Kasar CBN ya yi.

CBN dai ya sauya fasalin takardun kudi na N200, da N500 da kuma N1,000 tare da dakatar da amfani da tsofaffin takardun kudin, lamarin da wasu gwamnoni suka kalubalanta a Kotun Koli 

A kan hakan ne Kotun Kolin a farkon wannan wata na Maris ta ba da umarnin ci gaba da amfani da tsoffin takardun kudin har zuwa ranar 31 ga watan Disamba, 2023.

Sai dai har yanzu Gwamnatin Tarayya ta shafa wa idonta kwalli a kan hukuncin, amma dai an samu wasu bankuna da suka soma bai wa abokanan huldarsu tsofaffin takardun kudin kamar yadda Kotun Kolin ta yanke.

AMINIYA

Friday, 10 March 2023

An Sace Wayar Sanata A Taron Karbar Shaidar Cin Zabe

 


Sanata Orji Uzor Kalu ya ce an sace masa wayar hannu a lokacin taron mika takardar shaidar cin zabe ga zababbun ’yan majalisar dokoki ta tarayya.

Orji Kalu wanda shi ne tsohon Gwamnan Jihar Abiya, ya sanar da haka ne tare da jan hankalin mutane cewa su yi hattara da duk wanda zai yi magana da su ta lambobin wayarsa.

Ya ce, “An sace wayata mai dauke da lambobina na MTN da Glo  a lokacin taron mika takardar shaidar cin zabe da ya gudana a Cibiyar Taro ta Ƙasa da Kasa da ke Abuja

“Na sanar da kamfanonin sadarwa amma duk wanda ke da bayanin da zai taimaka, muna bukata,” in ji shi kamar yadda ya wallafa a shafinsa na Facebook.

Uzor Kalu ya lashe zaben Sanatan Abia ta Arewa da aka gudanar a ranar 25 ga watan Fabrairu, 2023, karkashin inuwar jam’iyyar APC.

A ranar Talata, 7 ga watan Fabrairu, Hukumar Zabe ta Kasa ta mika wa ’yan majalisar da suka ci zaben takardar shaidar nasara a zaben.

Kotun Koli Ta Ba Wa Rufai Hanga Na NNPP Kujerar Sanatan Kano Ta Tsakiya

 


Kotun Koli ta umarci Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ta cire sunan tsohon Gwamnan Kano, Sanata Ibrahim Shekarau, a matsayin wanda ya ci zaben Sanatan Kano ta Tsakiya.

Kotun ta umarci INEC ta maye gurbin Shekarau da sunan Rufai Hanga a matsayin halastaccen wanda ya ci zaben kujerar a karkashin Jam’iyyar NNPP.

Ta kuma tabbatar da hukuncin Kotun Daukaka Kara da ta tabbatar da Rufai Hanga a matsayin halastaccen dan takarar NNPP a zaben da aka gudanar ranar 25 ga watan Maris.

INEC dai ta bayyana Shekarau a matsayin wanda ya ci zaben duk kuwa da cewa ya sauya sheka daga NNPP zuwa PDP kuma ya sanar da cewa ya janye daga takarar.

AMINIYA

Thursday, 9 March 2023

Hajjin Bana: Hukumar Alhazai Ta Kano Za Ta Ci Da Yin Bita A Wannan Makon Sakamakon Dage Ranar Zabe

Sakamakon dage zabe da hukumar zabe ta kasa ta yi, hukumar Jin dadin alhazai ta Jihar Kano na sanar da Malaman Bita da Kuma Maniyyatan Jihar Kano cewa za'a ci gaba da yin Bitar mako mako a wannan satin wato Asabar da Lahadi 11 da 12 GA watan Maris ,2023 a Cibiyoyin Bita 16 da ke fadin Jihar Kano

Sanarwar wacce Mataimakiyar Daraktar Ilmantarwa da wayar da kan Alhazai ta Hukumar Hadiza Abbas Sanusi ta fitar, ta yi kira ga dukkanin maniyyatan su halarci Cibiyoyin nasu domin akwai fa'ida mai yawa ga yin hakan 

2023: Idan Na Zama Gwamna Zan Bawa Kananan Hukumomin 'Yancinsu - Gawuna

Mataimakin gwamnan jihar Kano kuma dan takarar gwamna na jam’iyyar  APC, Dr. Nasiru Yusuf Gawuna ya yi alkawarin baiwa kananan hukumomin jihar ‘yancin cin gashin kansu idan aka zabe shi a matsayin gwamna.

Ya bayyana hakan ne a lokacin da yake gabatar da shirin gidan talabijin na NTA cikin shirin "The Balot".

"Ƙananan Hukumomin wani bangare ne na gwamnati kuma su ne matakin kusa da jama'a wanda ke taimakawa hatta ci gaba da rarraba albarkatu da ayyuka".

"A matsayina na tsohon shugaban karamar hukumar na san abin da ya shafi gudanar da mulkinta".

Lokacin da nake shugaban karamar hukuma, an ba ni cikakkiyar dama nayi  aiki. Hakan ya sa muka samu nasarori da dama don haka idan aka zabe mu a matsayin Gwamna zan mayar da martani kamar yadda Gawuna ya bayyana”.

A sanarwar da babban sakataren yada labaransa, Hassan Musa Fagge ya fitar, Gawuna Ya kara da cewa shi ne wanda ya fi cancanta kuma a shirye ya ke ya zama Gwamnan Jihar Kano bayan ya yi aiki da gwamnatocin da suka gabata kuma ya samu kwarewa da dama, duk da haka ya ba da tabbacin karfafa nasarorin da suka samu a wani bangare na manufofin ci gaba.

Gawuna ya kuma bukaci masu kada kuri’a da su guji tashin hankali su gudanar da rayuwarsu cikin kwanciyar hankali da lumana a lokacin zaben.


Wednesday, 8 March 2023

INEC ta ɗage zaɓen gwamnoni da mako ɗaya

 


Hukumar Zaɓe ta Najeriya INEC ta ɗage zaɓen gwamnoni da na 'yan majalisar dokokin jihohi da mako guda, wato zuwa 18 ga watan Maris

 

INEC ta tabbatar wa da BBC ɗage zaɓen, bayan wani taron sirri da manyan jami'an hukumar suka yi a Abuja.

 

Kafofin yaɗa labarai na Najeriya sun ambato cewa INEC ba ta kammala saita na’urar tantance masu zaɓe ba ta BVAS wadda aka yi amfani da ita a zaɓen shugaban ƙasa a ranar 25 ga watan Fabirairu.

 

Sun ƙara da cewa hukumar ta ce sai ta samu damar kwashe bayananta da ta tattara na a yayin zaɓen shugaban ƙasar zuwa wani rumbunta na daban kafin ta sake saita na’urar ta yadda za a yi zaɓen gwamnoni da na ‘yan majalisar jihohi ba tare da wata damuwa ba.

 

Tun da farko, an tsara gudanar da zaɓen ne a ranar asabar 11 ga watan Maris.

 

Wannan na zuwa ne sa'o'i kaɗan bayan wata kotun ɗaukaka ƙara a Najeriya ta amince da buƙatar hukumar zaɓe ta ƙasar ta sake saita na’urar tantance masu zaɓe ta BVAS wadda aka yi amfani da ita a zaɓen shugaban ƙasar.

 

Tawagar alƙalan kotun mai mutum uku ƙarƙashin jagorancin Joseph Ikyegh ta yanke hukuncin cewa an bai wa INEC damar ne domin gudanar da zaɓen gwamnoni wanda aka tsara gudanarwa a ranar Asabar 11 ga watan Maris tun da fari.

 

Hukuncin na nufin kotun ta ƙi amincewa da buƙatar da ɗan takarar shugaban ƙasa a jam’iyyar LP Peter Obi ya shigar ta neman hana INEC goge bayanan masu zaɓen da aka naɗa a zaɓen shugaban ƙasar.

 

Tawagar alƙalan ta ce INEC ta bayyana cewa tana da shirin kwashe bayannan da ke cikin na'urar 176,000 da aka yi amfani da su a zaɓen ta wallafa su a wani rumbun bayananta na daban, ko da yake Obi da LP ba su nuna ƙin amincewa da wannan shiri ba.

BBC

 

 

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

FG Urges KOICA, FAO to Align Agricultural Intervention with Nigeria’s Development Priorities, Ward-Based Strategy

The Federal Government has called for stronger alignment between development partners’ interventions and Nigeria’s national deve...