Posts

Showing posts with the label Gwamnatin tarayya

Yanzu-Yanzu: Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Ranakun Hutu

Image
Gwamnatin tarayya ta ayyana ranakun Talata da Laraba 9 da 10 ga Afrilu, 2024 a matsayin ranakun hutu domin bukukuwan Sallah. Ministan harkokin cikin gida Olubunmi Tunji-Ojo ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da babban sakataren ma’aikatar, Aishetu Ndayako ya fitar ranar Lahadi. Ministan ya taya daukacin al’ummar musulmi murnar kammala azumin watan Ramadan mai alfarma. Tunji-Ojo ya yi kira gare su da su yi koyi da kyawawan dabi’u da suka hada da kyautatawa, soyayya, hakuri, zaman lafiya, makwabtaka, tausayi, kamar yadda Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya bayar da misali da shi. (SOLACEBASE)

Labari Da Dumiduminsa: Gwamnatin Tarayya Ta Amince Da Kamfanonin Jiragen Da Zasu Yi Jigilar Maniyyata Hajin 2024

Image
Gwamnatin tarayyar Najeriya karkashin jagorancin shugaba Bola Ahmed Tinubu ta amince da wasu manyan kamfanonin jiragen sama guda uku da za su yi jigilar maniyyata aikin hajjin 2024, wadanda suka hada da Air Peace., FlyNas da Max Air.  Har ila yau, an amince da wasu kamfanoni uku na jigilar kayayyaki da za su yi jigilar kayan alhazai WaÉ—annan su ne Cargo Zeal Technologies Ltd, Nahco Aviance da Qualla Investment Limited.   A sanarwar da mataimakiyar daraktar harkokin hulda da jama'a da dab'i ta hukumar, Fatima Sanda Usara ta sanyawa hannu, tace Yarjejeniyar ta karfafa yunÆ™urin gwamnati na tabbatar da ingantaccen aikin hajji ga maniyyatan Najeriya.  Don haka, a lokaci guda gwamnatin tarayya ta amince da rabon maniyyata daga jahohi daban-daban ga kowane kamfanonin jiragen sama da aka amince da su kamar haka:   i.Air Peace zai yi jigilar maniyyata daga: Abia, Akwa Ibom, Anambra, Bayelsa, Cross River, Delta, Ebonyi, Edo, Ekiti, Enugu, FCT, Imo, Kwara, Ondo da Ribas. ii.Fl

Gwamnatin Tarayya ta ce daga watan Satumbar wannan shekara za ta fara ba wa dalibai rance-Mashawarcin Shugaban

Image
Mashawarcin Shugaban Kasa kan Ayyuka na Musamman, Dele Alake, ya kara da cewa gwamnati za ta bullo da sabbin hanyoyin tallafa wa dalibai masu karamin karfi. “Daga cikin abubuwan da gwamnatin ta tsara na tabbatar da ganin kowane dalibi ya kammala karatunsa a kan lokaci, komai karamin karfin iyayensa, akwai daukar su aikin wucin gadi a makarantunsu, bayar da rance da kuma daukar nauyin wadanda suka cancanta a cikinsu,” a cewarsa. Alaka ya ce dokar bai wa dalibai rance da Shugaba Tinubu ya sanya wa hannu za ta fara aiki gabanin shiga sabuwar shekarar karatu mai kamawa a watan Satumba . Sai dai kuma bai ce uffan ba game da matakai ko shirye-shiryen da gwamnatin ta yi domin tabbatar da hakan. Ya kuma  nesanta Gwamnatin Tarayya da karin kudin rajista da sauransu da jami’o’inta suka yi, inda ya ce, har kwanan gobe ba a biyan kudin makaran a jami’o’in, don haka babu gaskiya a rahoton da wasu kafofin yada labarai suka wallafa cewa gwamnatin ta kara kudin makaranta a jami’o’inta. Ya

Labari Da Dumiduminsa : Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Shirinta Na Janye Tallafin Man Fetur

Image
Gwamnatin tarayya ta dakatar da shirin cire tallafin man fetur a karshen gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari. Wannan na daga cikin shawarar da majalisar tattalin arzikin kasa ta yanke a zamanta na ranar Alhamis. Ministar Kudi, Kasafin Kudi da Tsare-Tsare na Kasa, Misis Zainab Ahmed ce ta bayyana hakan a lokacin da take zantawa da manema labarai a fadar shugaban kasa a karshen taron hukumar zaben da mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo ya jagoranta a fadar shugaban kasa da ke Abuja. Zainab ta bayyana cewa akwai yiyuwar cire tallafin zai fara aiki a watan Yuni saboda dokar masana'antar man fetur, PIA da kuma kasafin kudin 2023 sun ba da tallafi har zuwa watan Yuni, don haka duk wani jinkiri na iya buƙatar gyara PIA da tanadin kasafin kuɗi. Ministan, ya ce babu wani wa'adi da aka bayar na cire tallafin, kuma gwamnati mai zuwa za ta yanke shawara a kan lokacin da za ta iya yin hakan. Cikakken labarin zai zo muku nan gaba kadan

Gwamnatin tarayya za ta dena biyan tallafin man Fetur

Image
  Gwamnatin tarayyar Najeriya ta ce daga Æ™arshen watan Yunin wannan shekara za ta daina biyan tallafin man fetur a Æ™asar. Ministar kuÉ—i, kasafi da tsare-tsare ta Æ™asar Zainab Ahmed ce ta bayyana haka a lokacin gabatar da kasasfin kuÉ—in shekarar 2023. BBC Hausa ta rawaito cewa Misis Zainab ta ce gwamnatin tarayya ta ware kimanin naira tiriliyan 3.36 domin biyan tallafin man fetur É—in a cikin wata shida na farkon shekarar 2023. Ministar ta Æ™ara da cewa hakan na daga cikin tsarin tsawaita cire tallafin zuwa wata 18 da gwamnatin ta bayyana a shekarar da ta gabata.