Search This Blog

Showing posts with label Garkuwa da mutane. Show all posts
Showing posts with label Garkuwa da mutane. Show all posts

Thursday, 16 May 2024

Karin Dalibai 7 Na Jami'ar Kogi Sun Shaki Iskar 'Yanci

Rundunar ‘yan sandan Jihar Kogi ta ce an kuɓutar da ƙarin wasu ɗalibai bakwai da aka sace a Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Confluence da ke yankin Osara a jihar


Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, SP Williams Aya, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Alhamis.

Aminiya ta ruwaito kamar yadda hukumar ‘yan sandan ta tabbatar cewa an sace ɗalibai 24 a jami’ar kuma zuwa yanzu an ceto 21 daga ciki.

Ya ce Sufeto-Janar na ‘yan sandan Nijeriya, IGP Kayode Egbetokun, ya tura ƙwararru domin ci gaba da aikin ceto ragowar ɗaliban da ke hannun masu garkuwa da su.


“An tura sashen tsaro na rundunar ‘yan sanda na sama, wanda ya ƙunshi jami’an rundunar masu amfani da jirgi masu saukar ungulu da aka horar da su kan binciken ta sama da jami’an sa ido da kuma sashen leƙen asiri na fasaha (TIU) don ci gaba da aikin ceton da kuma kai farmaki kan masu aikata laifuka a jihar.


“Ƙwararru jami’an tsaro tare da haɗin gwiwa ne suka kai ga ceto ƙarin mutane bakwai (7) da aka sace wanda ya kawo adadin zuwa 21.

“Muna nan akan bakarmu wajen ci gaba da duk mai yiwuwa domin tabbatar da cewa an kuɓutar da dukkan ɗaliban cikin aminci tare da gurfanar da waɗanda suka aikata laifin domin a hukunta su,” in ji shi.


Ya ƙara da cewa gwamnatin jihar Kogi da ma al’ummar jami’ar sun gamsu da aikin ceton da ake yi kawo yanzu.


Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Benthrad Onuoha, ya yabawa Sufeta Janar ɗin bisa goyon baya kan aikin da suke gudanarwa.
(AMINIYA)


Saturday, 23 March 2024

Rashin tsaro: Gwamnatin Kano Tayi Alkawarin Taimakawa Gwamnatin Tarayya Akan Yaki Da Masu Ta'addanci da Satar Mutane

Gwamnatin jihar Kano ta lashi takobin marawa shirin shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu baya na dakile illolin rashin tsaro da ke dagula zaman lafiya a kasar nan.

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya yi wannan alkawarin ne a ranar Juma’a a lokacin da ya karbi bakuncin ministan yada labarai da wayar da kan jama’a na kasa, Alhaji Muhammad Idris a ziyarar ban girma da ya kai gidan gwamnati.

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar, gwamnan ya ce ya dace a hada kai da gwamnatin tsakiya domin dakile wuce gona da iri domin dawo da ci gaban kasa.

Alhaji Yusuf ya yabawa shugaba Tinubu bisa yadda ya yi biyayya ga kiran da ya yi na sake bude iyakokin Najeriya da wasu kasashe, matakin da zai taimaka wajen rage wahalhalun tattalin arzikin kasar.

Ya kuma bayyana ziyarar a matsayin wacce ta dace da la’akari da yadda ta ke gudanar da harkokinta da masu ruwa da tsaki ciki har da ‘yan kasuwa da suka yi alkawarin yin duk abin da ya kamata na marawa gwamnatin tarayya baya a kokarin da take yi na inganta kasar nan.

Tun da farko, Ministan, Alhaji Muhammad Idris Malagi ya ce shi ne ya jagoranci tawagar manema labarai na fadar shugaban kasa zuwa Kano, kuma ya gana da ‘yan Najeriya daga sassa daban-daban, inda ya bayyana irin abubuwan da gwamnatin shugaba Tinubu ke yi domin kyautata rayuwa ga ‘yan Nijeriya.

A cewar ministan, "Mun zo ne domin neman hakuri da fahimtar juna a lokacin wasu kalubalen tattalin arziki da muke fama da su. Hakika wasu kalubalen na bukatar dukkan 'yan Najeriya su jure domin mu samu ci gaba a wajenmu baki daya." ministan

Ya kuma bayyana fatansa na cewa, wannan ikirari na Gwamna Abba Kabir Yusuf da kotun koli ta yi zai kara wa gwamnan kwarin gwuiwa wajen kara zage damtse wajen ganin an samar da ribar dimokuradiyya ga al’ummar Kano.

Ministan ya ci gaba da cewa, hadakarsa da ‘yan kasuwa za ta samar da sakamako mai kyau bisa la’akari da yadda Kano ta kasance cibiyar kasuwanci ba kawai a yankin Arewa ba har ma da fadin kasar baki daya.

Daga baya ya mika takardar shedar tutar kasa ga gwamnan tare da ba da shawarar a sayo tutoci masu yawa don amfani da su a gine-ginen gwamnati da sauran ayyukan hukuma a jihar.


Sunday, 4 February 2024

An Sako Daliban Da Aka Yi Garkuwa Da Su Ekiti

An sako daliban da malaman nasu ne kimanin mako guda bayan an yi garkuwa da su 



Dalibai tara da malamansu da aka yi garkuwa da su a Jihar Ekiti sun kubuta daga hannun ’yan bindiga.

Da misalin karfe 2 na dare, kafin wayewar garin yau Lahadi ne masu garkuwa da su suka sako su.

Hukumomi a jihar sun tabbatar da sako daliban su tara tare da malamansu.

An sako daliban da malaman nasu ne kimanin mako guda bayan an yi garkuwa da su a makarantar Apostolic Faith Group of Schools da ke yankin Emure-Ekiti.

Kawo yanzu dai babu bayanin ko an biya kudin fansa.

An yi garkuwa da su ne a makarantar Apostolic Faith Group of Schools da ke yankin Emure-Ekiti.

(AMINIYA)

Sunday, 21 January 2024

An Sako Kannen Nabeehah Da Ke Hannun ’Yan Bindiga

 Da misalin kare 12:30 na daren Asabar ne kannen na Nabeeh suka isa gidansu da ke Abuja, da rakiyar jami'an tsaro.



Masu garkuwa da mutane sun sako ’yan uwan marigayiya Nabeeha Al-Kadriyah hudu da suka sace a Abuja bayan sun shafe kwanaki 19 a hannunsu.

Da misalin kare 12:30 na daren Asabar ne kannen na Nabeeh suka isa gidansu da ke Abuja, da rakiyar jami’an tsaro.

Kawunsu  Sherifdeen, ya shaida wa wakilinmu ta wayar tarho da safiyar Lahadi, “An sako ’yan matan ne da yammacin ranar Asabar kuma tuni sun nufi gida”.

Su hudun su ne Najeeba ’ya aji 500 a Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya da kanwartar da ke aji 300 a jami’ar Nadherah, tare da tagwayen kannensu, Habeeba da Haneesa.

Dawowarsu bayan sun shafe kwanaki 19 a hannunsu ’yan bindigar da suka sace su a ranar 2 ga Janairu, 2024 ta sanya murna tskanin al’ummar unguwar.

Sanarwar da Sherifdeen ya sanya wa hannu ta ce, “farin cikinmu game da dawowarsu ba zai misaltu ba, muna godi ga Allah da al’umma da suka ba mu gudunmawa.

“Muna addu’ar samun rahama ga wadanda suka rasu, Allah ya kawo dauki ga iyalan wadanda ke hannun masu garkuwa, ya kubutar da su.”

An yi garkuwa da ’yan matan su biyar ne tare da mahaifinsu, wanda daga bisani masu garkuwar suka sako shi cewa ya kowa kudin fansarsu Naira miliyan 60 cikin kwana uku.

Rashin samun kudaden ya sa suka kashe Najeeba, ’yar aji 500 a Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya, suka kuma kara kudin fansan zuwa miliyan 100, gami da baranar kashe ragowar idan ba a kawo kudin cikin lokacin da suka kayyade ba.

Duk da cewa an biya kudin fansa Naira miliyan 100, masu garku wa da su sun ci gaba da tsare su na tsawon kwanaki, lamarin da ya sanya iyalan cikin zullumi har zuwa daren Asabar.

(AMINIYA)

Thursday, 18 January 2024

Dokar Najeriya Ta Haramta Biyan Kuɗin Fansa — Ministan Tsaro

 


Ministan Tsaro Mohammed Badaru Abubakar ya ce Dokar Najeriya ta haramta biyan masu garkuwa da mutane kuɗin fansa.

Ministan wanda ya bayyana haka ne a taron Majalisar Zartarwa da aka gudanar a wannan Larabar, ya ce lokaci ya yi da za a daina biyan kuɗin fansar saboda haka ne kaɗai hanyar kawo ƙarshen masu garkuwa da mutane.

Ya ce Shugaban Kasa ya bai wa dukkan hafsoshin tsaro goyon bayan da ya kamata don ganin an kawo karshen garkuwa da mutane da ya yi ƙamari a ƙasar.

Tsohon Gwamnan na Jihar Jigawa, ya ce kasancewar dokar Najeriya ta haramta bayar da kuɗin fansa ya sanya bai kamata mutane su riƙa biyan kuɗin ba saboda ba shi da amfani.

“Babbar matsalar ita ce yadda mutane ke fitowa a kafafen yaɗa labarai suna neman taimako, har a zo a tara musu kuɗi domin biyan fansa. Hakan bai dace ba.

“Idan muka daina biyan kuɗin fansa, sannu a hankali ayyukan masu garkuwa da mutane zai zama tarihi,” in ji Badaru.

Dangane da yadda rashin tsaro ke ƙara ta’azzara a Abuja, babban birnin ƙasar da kuma garkuwa da mutane da ake yi a yankunan gefen birnin, Ministan ya ce ayyukan da ake yi na korar ’yan bindiga a Arewa maso Yamma da Arewa ta Tsakiya shi ya sa suke ta ƙaura da guje-guje.

“Shugaban ƙasa ya ba mu umarni tare da duka hafsoshin tsaro, ya kuma ce lallai a je a tsayar da wannan abu da ke faruwa. Kuma mun sa ƙaimi don ganin mun kawo ƙarshensu,” in ji Badaru.

Ya ce ana ci gaba da fatattakar ’yan bindigar a jihohin Zamfara da Borno don ganin an daƙile ayyukansu.

A makon jiya ne tsohon Ministan Sadarwa da Tattalin Arziki na Zamani, Isa Pantami, ya samo wanda zai biya miliyan 50 daga Naira miliyan 100 na kudin fansar sauran ’yan mata ’yan gida daya da ’yan bindiga suka sace a Abuja.

Aminiya ta ruwaito yadda a daren Talatar makon jiya ’yan bindiga suka sace wani magidanci da ’ya’yansa mata shida a Karamar Hukumar Bwari ta Babban Birnin Tarayya.

Daga bisani suka sako shi sannan suka nemi ya biya Naira miliyan 60 zuwa ranar Juma’a kafin su sako ’ya’yan nasa.

Zuwa ranar Juma’ar Naira miliyan 30 iyalan suka iya tarawa, amma ’yan ta’addan suka ki amincewa, lamarin da ya sanya suka kashe babbar ’yarsa, Nabeeha, wadda ke ajin karshe a Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya.

Daga nan suka kara kudin fansa zuwa miliyan 100, tare da barazanar kashe sauran ’yan uwanta idan har ba a biya ba.

A kan haka ne tsohon minista Isa Pantami ya bayyana cewa ya tattauna da “aboki kuma dan uwa” wanda zai biya Naira miliyan 50 daga kudin fansar ragowar ’yan matan.

Ya rubuta cewa, “Duk da cewa ba na goyon bayan biyan kudin fansa ga ’yan bindiga, amma ya zama dole, tunda ta tabbata jiya mun rasa ’yarmu Nabeeha, kuma ana barazanar kashe sauran ’yan uwanta biyar, kamar yadda mahaifinsu ya shaida min.

“Na yi magana da da wani abokina kuma dan uwa wanda ya ce zai biya Naira miliyan 50 …. duk wanda ke da hali zai iya karawa domin mahaifin ya samu abin biya ya ceto rayuwar ’ya’yan namu.”

Ya kuma yi addu’ar zaman lafiya a kasar, ya kuma jajanta wa iyalan dalibar da aka kashe tare da yi addu’ar Allaha Ya saka wa wadanda suka rasu, Ya sanya su a  Aljanna.

(AMINIYA)

Sunday, 27 August 2023

Masu Garkuwa Da Mutane Sun Sace Jami'in Alhazai A Kano

A daren jiya Asabar ne, wasu mutane da ake zargin masu garkuwa da mutane ne,suka je har gida suka tafi da Jami'in Alhazai na Karamar Hukumar Bebeji

Alhaji Sagiru Umar Kofa, ya kasance babban hadimi ga zababben dan majalisar tarayya mai wakiltar kananan hukumomin Kiru da Bebeji, Abdulmumin Jibrin Kofa 

Majiyarmu ta tabbatar mana cewa masu garkuwa wadanda suka shiga gidan Sagiru Kofa su biyar, an tabbatar cewa wasu daga cikinsu na dauke da bindiga

A halin yanzu dai tuni jami'an 'yan sanda sun dukufa domin gano inda masu garkuwar suka yi da shi don ƙoƙarin kubutar da shi 

Monday, 8 May 2023

'Yan sandan Najeriya sun ceto mutane 58 daga hannun 'yan bindiga

 


‘Yan sanda a Najeriya sun ce sun ceto mutane 58 da ‘yan ta’adda suka yi garkuwa da su a jihar Kogi, yayin da daya daga cikin wadanda aka yi garkuwa da sun ya rasa ransa yayin artabu tsakanin jami’an tsaro da ‘yan ta’addan

A cikin wata sanarwa da kakakin rundinar ‘yan sandan jihar Josephine Adeh ta fitar a wannan Lahadin, ta ce wannan nasara da suka samu wani bangare ne na aikin hadin gwiwa tsakanin rundunar da sauran jami’an tsaro, tare da hadin gwiwar ‘yan banga da mafarautan jihar. 

Adeh ta ce lamarin ya faru ne a dajin Udulu da ke Karamar Hukumar Gegu mai nisan kilomita 145 daga bababban birnin tarayya kasar. 

A cewarta, an yi musayar wuta tsakanin ‘yan ta’addan da kuma jami’an tsaro kuma daga bisani suka tsere suka bar mutanen da suka yi garkuwa da su.  

Sai dai bata bayyana inda aka sace mutanen ba da kuma tsawon lokacin da suka dauka a hannun ‘yan ta’addan.  

RFI

Friday, 13 January 2023

'Yan bindigar da suka yi garkuwa da ni suna so su isarwa da gwamnati wani sake ne - Kanal 'Yandoto


 

Sunday, 8 January 2023

Labari da dumiduminsa : 'Yan bindiga sun sake yin garkuwa da fasinjojin Jirgin kasa

Watanni bayan da ‘yan ta’addan suka kai hari tare da yin garkuwa da fasinjoji da dama a cikin jirgin kasa zuwa Kaduna, wasu ‘yan bindiga sun kuma kai farmaki tashar jirgin kasa tare da kwashe mutane da yawa a Jihar Edo dake kudu maso kudancin Najeriya.

Fasinjojin da suka samu raunuka, an ce suna jiran su hau jirgin kasa a wurin da lamarin ya faru, kafin su nufi garin Warri mai arzikin man fetur.

Tuni dai hukumar 'yan sanda ta Rahotanni sun tabbatar da faruwar lamarin a cewar tashar talabijin ta TVC.

Rundunar ‘yan sandan jihar Edo ta ce ‘yan bindigar da ke dauke da bindigogi kirar AK-47 sun kai farmaki tashar jirgin da misalin karfe 4 na yammacin ranar Asabar 7 ga watan Janairu, inda suka yi ta harbe-harbe kafin su fito da shirinsu. 

A ranar 28 ga Maris, 2022 ne wasu ‘yan bindiga suka kai hari kan jirgin kasa da ke kan hanyarsa ta zuwa Kaduna daga Abuja, inda suka kashe wasu tare da yin awon gaba da wasu fasinjoji. 2022 .

Har yanzu dai Hukumar Jiragen kasa ta Najeriya ba ta ce uffan ba game da sabon ci gaban da aka samu a daidai lokacin da ake hada wannan rahoto.

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

FG Urges KOICA, FAO to Align Agricultural Intervention with Nigeria’s Development Priorities, Ward-Based Strategy

The Federal Government has called for stronger alignment between development partners’ interventions and Nigeria’s national deve...