Posts

Showing posts with the label Sanatoci

Sanatoci Sun Sallama Albashinsu Na Disamba Ga Mutanen Tudun Biri

Image
Sanatocin Najeriya gaba dayansu sun sadaukar da albashinsu na watan Disamba ga mutanen da harin bom da jirgin soji ya samu a wurin taron Mauludi a Jihar Kaduna. Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau Jibrin ya sanar cewa sanatocin su 109 sun amince a ba da albashin nasu a matsayin gudunmuwar ga mutanen Tudun Biri. Sanata Barau wanda ya yi bayani a yayin ziyararsu fadar gwamnatin Kaduna domin jajanta wa Gwamna Uba Sani kan tsautsayi, ya bayyana cewa albasjin ya kama Naira miliyan 109. Ya ce hakika sun yi bakin ciki bisa tsautsayin da ya auka wa al’ummar garin na Tudun Biri da ke Karamar Hukumar Igabi, kuma majalisar ta sha alwashin yin bincike domin gano musabbabin abin da ya faru. Gwamna Uba Sani a jawabinsa ya mika godidyarsa ga dukkan ’yan majalisar da suka jajanta masa, inda ya bukaci su tabbatar da Hakimin Yan Tudun Biri ya fito kunya ta hanyar yi musu adalci. Ya kumu nuna rashin jin dadinsa bisa yadda wasu ke neman sanya rigar addini ko kabilanci a kan ab

Sanatoci 62 Sun Amince Da Barau Jibrin Ya Zama Shugaban Majalisar Dattawa

Image
A daidai lokacin da ake gudanar da sauye-sauye a zaben shugaban majalisar dattijai karo na 10, zababbun sanatoci 62 cikin 109 sun amince da Sanata Barau Jibrin daga jihar Kano a matsayin shugaban majalisar dattawa. Wani Sanata mai wakiltar Arewa maso Yamma kuma na hannun damar Jibrin ne ya bayyana hakan bayan wani taron gaggawa da suka yi da sanyin safiyar Talata a Abuja. Ya bayyana cewa kawo yanzu Zababbun Sanatoci 62 sun amince da Sanata Jibrin kuma 46 daga cikinsu sun halarci taron na dare a otal din Transcorp. Taron dai ya ta’allaka ne da dabarun hada kan sauran Zababbun Sanatoci domin hada hannu wajen ganin Sanata Jibrin ya zama Shugaban Majalisar Dattawa na 10. Zababbun ‘yan majalisar, sun nuna adawa da nadin Akpabio a matsayin shugaban majalisar dattawa. Mun san cewa Tinubu ya fi son Akpabio ne kawai don É—aukar Kiristoci a Najeriya, ba wai don cancanta ko gudunmawar da ya bayar don nasarar jam'iyyar ba. Sai dai abin takaici Akpabio ba zai iya tafiyar da harkokin