Search This Blog

Showing posts with label Hukumar Tace Finafinai. Show all posts
Showing posts with label Hukumar Tace Finafinai. Show all posts

Wednesday, 23 August 2023

Hukumar Tace Finafinai Ta Rufe Sutudiyon Mawaki Ɗanzaki

Hukumar Tace Finafinai da Dab’i ta Jihar Kano ta tabbatar da cewa ita ce ta garƙame sutudiyon mawakin siyasar nan Idris Ɗanzaki tare da yin awon gaba da kayan aikinsa.

Jami’in Hulda da Jama’a na Hukumar, Abdullahi Lawan Sulaiman ya shaida wa ’yan jarida a Kano cewa hukumar ta ɗauki matakin ne bayan mawaƙin ya yi biris da gayyatar da ta yi mana na bayyana a ofisoshint

Ya ce tun ranar Asabar Hukumar ta nemi mawakin ya bayyana a ofisoshinta, amma har zuwa lokacin da muke kawo muku wannan labari bai amsa gayyatar ba.

“Kasancewar a yanzu zamani ya sawwake abubuwa mun yi amfani da waya inda muka kira wannan mawaki Idris Ɗanzaki inda kuma muka nemi ya zo wannan hukuma.

“Bayan sun kira ni a waya sun ce suna gayyata ta, na tura lauyana hukumar don ya wakilce ni.

“Amma me zai faru sai aka kira ni cewa wai hukumar ta rufe sutudiyona haka kuma ta kwashe wasu kayayyakin aikina.”

Abdullahi Lawan ya kara da cewa hakan ya sa Hukumar ta sa aka kulle sutudiyon tare da kwashe kayayyakin aikinsa.

Sai dai yayin da majiyarmu ta tuntubi mawaƙin ya tabbatar mata cewa hukumar ta gayyace shi amma ya tura lauyansa ya wakilce shi.

Mawakin ya yi iƙirarin cewa Hukumar ba ta sanar da shi laifin da take zargin sa da aikatawa ba.

Duk da cewa hukumar ba ta bayyana dalilin gayyatar mawakin ba, amma rahotanni sun nuna cewa ana zargin sa ne da yin munanan kalamai ga jagoran darikar Kwankwasiyya Injiniya Rabiu Musa Kwankwaso a cikin wata waka da ya yi a kwanan baya.
(AMINIYA)





Monday, 7 August 2023

Dawo Da Makarantar Koyar Da Sana'ar Fim Dake Tiga, Babbar Nasara Ce Ga Masana'antar Kannywood- Abba El-Mustapha

Shugaban Hukumar tace Fina-finai da Dab'i ta Jahar Kano, Abba El-mustapha ya bayyana farin cikinsa tare da karfin gwiwa dangane da kara bude makarantar koya Sana'ar Fina-finai dake garin Tiga a Jahar Kano.

A sanarwar da jami'in hulda da jama'a na Hukumar, Abdullahi Sani Sulaiman ya sanyawa hannu, tace nada sabon Daraktan Makarantar Alh. Dr. Maigari Indabawa yace, hakika abu ne da ya dace duba da yadda Sana'ar fina-finan ke bukatar sauyi ta fannin ilimi Wanda hakan zai bunkasa tattalin arzikin Kano tare da kawo kudin shiga.

Ya Kara da cewa, da yawa daga cikin yan masana'antar na bukatar Samin karin horo domin a nuna musu sabbin da baru ta yadda  Sana'ar zata tafi da zamani haka kuma su kansu yan masana'antar zasuyi gogayya da takwarorin su na kasashen waje .

Abba El-mustapha ya godewa Gwamna tare da yiwa sabon shugaban makarantar fatan alheri tare da addu'ar Allah yasa yafara a sa'a ya Kuma gama lafiya.

El-mustapha ya kuma yi wa sauran wadanda aka nada a mukamai daban-daban fatan alheri tare da addu'ar samun Nasara adukkan aiyukan su. 

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

FG Urges KOICA, FAO to Align Agricultural Intervention with Nigeria’s Development Priorities, Ward-Based Strategy

The Federal Government has called for stronger alignment between development partners’ interventions and Nigeria’s national deve...