Posts

Showing posts with the label Gobara

Gwamnan Kano Ya Karbi Gudunmawar Kayan Kashe Gobara

Image
Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya jaddada kudirin gwamnatinsa na yin shiri na gaggawa domin kare rayuka da dukiyoyi. Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa ya fitar a ranar Laraba. Yayin kaddamar da motocin kashe gobara guda biyu da hukumar kashe gobara ta tarayya ta ware wa jihar Kano, Gwamna Yusuf ya bayyana bada tabbacin yin amfani da na’urar kashe gobara guda biyu da gwamnatin tarayya ta samar kwanan nan. Ya kuma karbi tallafin daga hannun Kwanturola na Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Kano, inda ya mika godiyarsa bisa wannan karimcin tare da yin alkawarin samar da kayayyakin da ake bukata da kuma tallafa wa Hukumar domin gudanar da ayyukanta yadda ya kamata. Gwamnan ya kuma yabawa Gwamnatin Tarayya bisa wannan tallafin, inda ya jaddada muhimman alfanun da take baiwa al’ummar Jihar Kano ta hanyar inganta tsaro da tsaro. Ya kara da cewa, sabbin motocin kashe gobara za su kara hab

Gobara ta tashi a Kotun Kolin Najeriya

Image
Zuwa yanzu dai ba a kai ga gano musabbabin tashin gobarar ba, amma majiyarmu ta ce jami’an hukumar kashe gobara sun isa harabar kotun. Wannan na daga cikin gobarar da aka samu a manyan cibiyoyin gwamnati a Babban Birnin Tarayya, Abuja. A watan Mayun 2023 gobara ta lakume wani yanki na barikin sojojin sama da ke Abuja. A cikin watan ne aka yi gobara a ginin Hukumar Akwatin Gidan Waya (NIPOST) a Abujar. A watan Afrilu Ofishin Akanta-Janar na Kasa (AGF) ya yi gobara. (AMINIYA)

Buhari Ya Je Maiduguri Domin Jajantawa 'Yan Kasuwar Monday Market

Image
Shugaban Kasa Muhamamdu Buhari ya isa Jihar Borno, domin jajanta wa ’yan kasuwar da iftila’in gobora ta shafa a Kasuwar Monday da ke Maiduguri. An wayi gari ranar Lahadi a Maiduguri da gobarar, wadda ta lakume dubban shaguna a kasuwar, wadda ita ce mafi girma a Jihar Borno da ma yankin Arewa maso Gabashin Najeriya. ’Yan sanda na ci gaba da tsare Ali Madaki kan daukar bindiga a yakin neman zabe Ana sa ran a yayin ziyarar ta ranar Alhamis, Buhari zai je Fadar Shehun Borno, inda zai jajanta wa ’yan kasuwar da suka yi asarar dukiyoyinsu a gobarar ta ranar Lahadi. Shugaban kasar zai kuma kaddamar wa wasu ayyuka da suka hada da rukunin gidajen da Gwamna Babagana Zulum ya gina da wasu tituna a garin Maiduguri. Sauran su ne Cibiyar Kula da Masu Cutar Kansa a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Maiduguri da kuma Tashar Iskar Gas ta kamfanin NNPC.

LABARI DA DUMIDUMINSA : Gobara ta tashi a Hedikwatar 'yan sanda ta Kano

Image
Hedkwatar ‘yan sandan Kano da ke Bompai a karamar hukumar Nasarawa, tana cin wuta, inda ake zargin ta kona ofisoshi da muhimman bayanai da dama.  Hukumar kashe gobara ta jihar ta ce tuni ta tura jami’an ta wurin da lamarin ya faru domin dakile gobarar da ta tashi a ginin bene mai hawa daya na rundunar.  Rahotanni da basu tabbata ba sun nuna cewa gobara ta tashi ne a saman benen, Inda ta kama ko’ina amma banda ofishin kwamishinan ‘yan sandan jihar, Mamman Dauda. Ko da Majiyarmu ta tuntubi kakakin rundunar ‘yan sandan, SP Abdullahi Haruna Kiyawa ta wayar hannu, mun sami wayarsa a kashe har lokacin haÉ—a wannan rahoton, amma har yanzu ba a san musabbabin tashin gobarar ba.