Search This Blog

Showing posts with label Allurar Rigakafi. Show all posts
Showing posts with label Allurar Rigakafi. Show all posts

Monday, 13 May 2024

Hajin 2024: Hukumar Alhazai Ta Bauchi Ta Bayyana Farin Cikinta Bisa Yadda Maniyyata Suka Je Asibitoci Domin Yi Musu Rigakafi

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Bauchi ta bayyana jin dadinta kan yadda maniyya suka fita domin karbar allurar rigakafi

A sanarwar da Jami'in hulda da jama'a na hukumar, Muhammad Sani Yunusa ya sanyawa hannu, yace Sakataren zartarwa na hukumar limamin Abdurrahman Ibrahim Idris ya bayyana haka a lokacin da yake karbar rahoton aikin rigakafin da ake yi daga kananan hukumomin jihar 20.
Ya ce an fara gudanar da aikin ne a jiya Lahadi 11 ga watan Mayu, 2024 tare da maniyyatan karamar hukumar Bauchi da sauran kananan hukumomin da ke kusa da babban birnin jihar kamar Dass, Tafawa Balewa, Bogoro, Alkaleri, Kirfi da Ganjuwa

Imam Abdurrahman ya kara da cewa maniyyatan wadanda ke nesa na kananan hukumomin Katagum, Gamawa da. Zaki, sun fita da yawa zuwa manyan asibitocinsu daban-daban domin ayi musu rigakafin, yana mai bayyana yadda lamarin ya kasance abin karfafa gwiwa.
Don haka yay Kira ga maniyyatan da har yanzu ba a yi musu allurar ba da su yi hakan a cikin lokacin da aka tsara na yin allurar don su ba su damar cika ka’idojin aikin hajji.


Friday, 10 May 2024

Hajjin 2024: Sakataren Hukumar Alhazai Na Bauchi Bayyana Muhimmancin Yi Wa Maniyyata Rigakafi


Sakataren Zartarwa na Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Bauchi Imam Abdurrahman Ibrahim Idris ya bayyana jin dadinsa da tsare-tsaren Hukumar Kula da Lafiya a matakin farko ta jiha na fara gudanar da allurar rigakafin cututtukan da za a iya kauce musu kamar su diphtheria, polio da kyanda.

 A sanarwar da Jami'in hulda da jama'a na hukumar, Muhammad Sani Yunusa ya sanyawa hannu, yace Imam Abdurrahman ya bayyana jin dadinsa a lokacin da ya ziyarci wajen ajiye magunguna na jihar da ke asibitin kwararru na Bauchi, a fadar jiha.

 Ya bayyana cewa ya je gurin ajiyar ne domin ganewa idonsa shirye-shiryen hukumar lafiya matakin farko na jihar gabanin gudanar da allurar rigakafin cutar a fadin jihar.

Babban sakataren wanda ya nuna farin cikinsa kan abin da ya gani a gurin ajiye magungunan, ya yi nadamar sanar da rashin fara aikin rigakafin a yau kamar yadda aka tsara tun da farko, a cewarsa, sakamakon cikas da aka samu ne wajen kawo maganin a jiha.
 
 Ya bayyana wasu ’yan sauye-sauye a tsarin gudanarda rigakafin, inda ya ce maniyata daga karamar hukumar Bauchi da shirin adashen gata wato HSS, na hukumar alhazai da Alhazan da gwamnati ta dauki nauyin su, za'a mu rigakafinsu a gobe Asabar, *11 zuwa Litinin 13 ga Mayu, 2024* daga *10; 00 na safe zuwa 4;00* na yamma a asibitin kwararru na Bauchi (BACAS).

 Imam Abdurrahman ya kara da cewa, za a raba alluran rigakafin a dukkanin manyan asibitocin kananan hukumomi a jiha, ta yadda Alhazan kananan hukumomi za su samu saukin halartar cibiyoyi daban-daban kamar yadda aka tsara daga *Lahadi 12 ga Mayu, 2024.*

 Yayin da yake nanata cewa rigakafin ya yi daidai da sharuddan da hukumomin lafiya na kasar Saudiyya suka gindaya na maniyyata a lokacin aikin Hajji, Imam Abdurrahman ya bukaci maniyyatan da su tabbatar da sunyi allurar, Kuma zasu taho da slip din fom din aikin hajjin su don tantance su kafin musu rigakafin.

 A wani labarin kuma, Bankin Jaiz Bank reshen jihar Bauchi ya gabatar da wani tallafi ga babban sakataren hukumar jin dadin alhazai ta Bauchi.

 Da yake gabatar da tallafin, a madadin bankin, Manajan reshen Bankin dake Bauchi Muhammad Muhammad Gidado ya yi alkawarin cigaba da samun kyakyawar hadin gwuiwa da hukumar alhazai domin tallafawa don jin dadin alhazai.

 Ya kuma jaddada cewa Bankin ya samar da kyawawan matakai don tabbatar da walwalan maniyyata.

 A lokacin da yake karbar tallafin a madadin alhazai, Babban Sakataren Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Bauchi Imam Abdurrahman Ibrahim Idris ya yaba da wannan karimcin, inda ya ce dukkan alhazan HSS sun amfana da wannan shirin Bankin.

 Ya ce "Na gamsu matuka da jajircewar da kuka yi na kyautata jin dadin alhazanmu ta hanyar ba su kyauta da zai taimaka musu wajen gudanar da aikin hajjin su."

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

FG Urges KOICA, FAO to Align Agricultural Intervention with Nigeria’s Development Priorities, Ward-Based Strategy

The Federal Government has called for stronger alignment between development partners’ interventions and Nigeria’s national deve...