Posts

Showing posts with the label Allurar Rigakafi

Hajin 2024: Hukumar Alhazai Ta Bauchi Ta Bayyana Farin Cikinta Bisa Yadda Maniyyata Suka Je Asibitoci Domin Yi Musu Rigakafi

Image
Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Bauchi ta bayyana jin dadinta kan yadda maniyya suka fita domin karbar allurar rigakafi A sanarwar da Jami'in hulda da jama'a na hukumar, Muhammad Sani Yunusa ya sanyawa hannu, yace Sakataren zartarwa na hukumar limamin Abdurrahman Ibrahim Idris ya bayyana haka a lokacin da yake karbar rahoton aikin rigakafin da ake yi daga kananan hukumomin jihar 20. Ya ce an fara gudanar da aikin ne a jiya Lahadi 11 ga watan Mayu, 2024 tare da maniyyatan karamar hukumar Bauchi da sauran kananan hukumomin da ke kusa da babban birnin jihar kamar Dass, Tafawa Balewa, Bogoro, Alkaleri, Kirfi da Ganjuwa Imam Abdurrahman ya kara da cewa maniyyatan wadanda ke nesa na kananan hukumomin Katagum, Gamawa da. Zaki, sun fita da yawa zuwa manyan asibitocinsu daban-daban domin ayi musu rigakafin, yana mai bayyana yadda lamarin ya kasance abin karfafa gwiwa. Don haka yay Kira ga maniyyatan da har yanzu ba a yi musu allurar ba da su yi hak

Hajjin 2024: Sakataren Hukumar Alhazai Na Bauchi Bayyana Muhimmancin Yi Wa Maniyyata Rigakafi

Image
Sakataren Zartarwa na Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Bauchi Imam Abdurrahman Ibrahim Idris ya bayyana jin dadinsa da tsare-tsaren Hukumar Kula da Lafiya a matakin farko ta jiha na fara gudanar da allurar rigakafin cututtukan da za a iya kauce musu kamar su diphtheria, polio da kyanda.  A sanarwar da Jami'in hulda da jama'a na hukumar, Muhammad Sani Yunusa ya sanyawa hannu, yace Imam Abdurrahman ya bayyana jin dadinsa a lokacin da ya ziyarci wajen ajiye magunguna na jihar da ke asibitin kwararru na Bauchi, a fadar jiha.  Ya bayyana cewa ya je gurin ajiyar ne domin ganewa idonsa shirye-shiryen hukumar lafiya matakin farko na jihar gabanin gudanar da allurar rigakafin cutar a fadin jihar. Babban sakataren wanda ya nuna farin cikinsa kan abin da ya gani a gurin ajiye magungunan, ya yi nadamar sanar da rashin fara aikin rigakafin a yau kamar yadda aka tsara tun da farko, a cewarsa, sakamakon cikas da aka samu ne wajen kawo maganin a jiha.    Ya bayyana wasu ’yan sau