Posts

Showing posts with the label Kudin Guzuri

Hajj 2024: CBN Ya Janye Batun Biyan Kudin Guzurin Alhazai Ta Katin ATM

Image
Babban Bankin Najeriya ya dakatar da bayar da guzurin Alhazai na Hajji 2024 ta hanyar katin ATM Kwafin takardar da Bankin ya fitar wacce kuma  HAJJ REPORTERS ta gani mai kwanan wata 17 ga Mayu 2024 mai dauke da sa hannun daraktan riko na sashen ayyuka na kudi Solaja Muhammed J. Olawumi wanda aka aikewa bankunan kasuwanci ya ce “bayan gaggawar da aka samu tare da lura da karancin lokaci dangane da jigilar jirgin. Alhazan 2024, Shugabancin Bankin ya amince da biyan dukkanin tsabar kudi ga maniyyatan. “Ku lura cewa wannan sanarwar ta zarce tsarin da aka gabatar muku na farko na ayyukan Hajji na 2024. Nan ba da jimawa ba za a mika wata wasika a hukumance kan hakan.” Idan dai za a iya tunawa babban bankin ya sanar da hukumar alhazai ta kasa NAHCON da Jihohi da Rundunar Soji cewa za a biya kudin guzurin na Hajjin bana  wanda aka biya dala 500 ga kowane mahajjaci da kashi 60/40 cikin 100. tsabar kudi da kati Bankin ya ce dala 200 ne kawai za a ba da tsabar kudi yayin da za a ba da

Hajj 2024: Kungiyar Fararen Hula Ta Yi Kira Ga Babban Bankin Najeriya Ya Sauya Tunani Kan Biyan Kudin Guzurin Alhazai

Image
An shawarci Babban Bankin Najeriya (CBN) da ya yi watsi da ra’ayin bayar da kudin  (BTA) ta hanyar katin biyan kudi. Kungiyar fararen hula masu daukar rahotannin aikin Hajji  (IHR) ne suka bayar da wannan shawarar a wata sanarwa da babban jami'inta na kasa Ibrahim Mohammed ya fitar. Kungiyar ta ce kasa da sa’o’i 24 da fara jigilar maniyyata zuwa kasa mai tsarki, babban Bankin ya umarci wasu bankunan kasuwanci da su biya maniyyatan dala 200 kacal daga cikin dala 500 da ake sa ran kowane mahajjaci zai samu yayin da sauran dala 300. za a bayar a kan katin cirar kudi  “Alhazai na bana sun riga sun shiga cikin rashin tabbas da yawa tun daga manufofin sayayya da suka haifar da hauhawar farashin Hajji zuwa raguwar kudin guzuri. Wannan shawarar da babban bankin ya yanke zai kara musu bala’i ne kawai”. “ Sanin kowa ne cewa mafi yawan alhazanmu sun fito ne daga karkara kuma ba su da masaniyar harkar hada-hadar kudi, yawancin ma ba su san yadda ake amfani da katin ATM ba.  Har

Kungiyar Fararen Hula Ta Yi Kira Ga Hukumar NAHCON Da Na Jahohi Su Sanar Da Kudin Guzurin Maniyyata Hajjn 2024

Image
Kungiyar dake daukar rahotannin aikin Hajji ta bukaci NAHCON da hukumomin alhazai na Jihohi da su sanar da mahajjata adadin kudin guzirinsu a  cikin kudin Hajjin 2024 Kungiyar farararen hula Masu daukar rahotannin Aikin Hajji mai zaman kanta,, ta bukaci hukumar alhazai ta kasa, NAHCON, da hukumomin jin dadin alhazai na jahohi da su sanar da dukkan maniyyatan da suke son zuwa aikin Hajji na 2024 ko nawa zasu karba a matsayin kudin guzirinsu  Kungiyar ta ce ya zama wajibi a ja hankalin hukumar NAHCON da hukumomin alhazai na jihohi cewa kudin aikin hajjin 2024 da suka sanar kawo yanzu bai nuna adadin da za a bai wa maniyyatan a matsayin kudin guziri ba sabanin yadda aka saba yi tsawon shekaru. Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun kodinetan kungiyar na kasa, Ibrahim Muhammed wanda aka rabawa manema labarai. Kungiyar ta IHR ta ce, alawus-alawus na kudaden waje ne wanda dan Najeriya, a irin wannan yanayi, alhazan kasar Saudiyya ke ba su damar ciro daga b