Posts

Showing posts with the label Taron Addu'a

Kofa ya shirya taron addu'a na musammam ga Tinubu, Kwankwaso da Gwamna Abba Kabir Yusuf

Image
...Ya ce har yanzu ƙofar NNPP a buɗe take don yin ƙawance da APC da sauran jam’iyyu Abdulmumin Jibrin Kofa, ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar mazaɓar Kiru da Bebeji, Kano, a yau ya tara malamai 1,000 a garinsa na Kofa a Bebeji, Kano, domin addu’a ta musamman ga Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu da kasar baki daya, Jagoran jam’iyyar NNPP da Ɗarikar Kwankwasiyya, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso, PhD, FNSE da kuma neman nasara ga Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf a Kotun Ƙoli, da kuma addu’ar neman taimakon Allah ga ɗan majalisar.  A sanarwar da hadimin dan majalisar kan harkokin yada yada labarai, Sani Ibrahim Paki ya sanyawa hannu, yace yayin taron, malaman sun sauke Alƙur’ani sau 1,101, sannan suka yi addu’o’i na musamman. A taƙaitaccen jawabin da ya gabatar a wajen taron, Hon. Jibrin ya ce alaƙarsa da Shugaba Tinubu ba ɓoyayya ba ce. Ya kuma ce Kwankwaso ne maigidanshi, sannan zai ci gaba da iya ƙoƙarinsa wajen ganin an samu kyakkyawar alaƙa a tsakanin Tinubun da Kwankwaso.

Abdulmumin Jibrin Kofa Ya Shirya Taron Addu'a Kan Nasarar Kotu, Ya Kuma Tallafa Wa Mutum 10,000

Image
Dan Majalisar Wakilai mai wakiltar mazabar Bebeji da Kiru, Abdulmumin Jibrin Kofa, ya shirya taro na musamman wanda ya haɗa sama da mutum 10,000 domin yin addu’o’i a garinsa na Kofa da ke Karamar Hukumar Bebeji ta Jihar Kano a ranar Lahadi  Ɗan majalisar mai hawa huɗu ya shirya taron ne domin ya gode wa Allah saboda nasarar da ya samu a Kotun Sauraron Ƙararrakin Zaɓe da ta Ɗaukaka Ƙara da ke Abuja a kwanakin baya, da kuma raba wasu kayan tallafi ga ’yan mazabarsa. A yayin kasaitaccen taron dai, an bayar da tallafi ga ’yan mazabar su 10,000 maza da mata. Bugu da ƙari, an ba mutanen tallafin kuɗi da kayan sanaa da motoci da kayan abinci da sutturu da kuma sauran kayan amfanin yau da kullum. Kazalika, an yi addu’a ta musamman ga Gwamnan Jihar Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf, domin neman Allah Ya ba shi nasara a Kotun Ɗaukaka Ƙara da ta Ƙoli, da sauran ’yan majalisar Kano na NNPP da suka yi nasara a kotu, da ma fatan nasara ga waɗanda ba a kai ga yanke

Abdulmumin Jibrin Kofa Ya Gudanar Da Taron Shan Ruwa Na Mutum Dubu Biyu

Image
Zababben Dan majalisar  tarayya mai wakiltar kananan hukumomin Kiru da Bebeji, Abdulmumin Jibrin Kofa (Jarman Bebeji) ya jagoranci taron shan ruwa da al'umar Kiru da Bebeji mutane 2000 a gidansa dake garin Kofa. Bayan buda baki Kofa ya jagoranci mahalatta wannan taro Sallah.  Taron shan ruwan ya sami halartar Dagatai, Limamai, 'Yan siyasa, da sauran mutane daban-daban dake mazabarsa ta dan majalisar tarayya  Yayin taron, anyi amfani da wannan dama wajen yi wa Zababben Dan Majalisar Tarayyar, Alhaji Abdulmumin Jibrin Kofa addu'a da  Gwamna jihar Kano mai jiran rantsuwa Injiniya Abba Kabir . Yusif tare da Jagoran Kwankwasiyya Sanata Rabiu Musa Kwankwaso. Haka kuma an roki madaukakin Sarki Allah ya dauwamar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a Jahar Kano da ma Najeriya baki daya

Kofa Ya Gudanar Da Taron Addu'a, Godiya Da Kuma Sako Ga Jami'an Tsaro Da Hukumar Zabe

Image
A ranar Asabar ce sabon zababben dan majalissar tarayya mai wakiltar Kiru da Bebeji, Abdulmumin Jibrin Kofa PhD, ya jagoranci Sallar Nafila tare da addu'oi da godiya ga Allah da al'umma bisa nasara da Allah ya bashi a zaben da ya gabata  Haka kuma an gudanar da addu'oi na musamman wa mai girma Madugu Sen Rabiu Musa Kwankwaso da addu'oin samun nasarar Engr Abba Kabir Yusif da yan takararsu na majalisar jiha a Bebeji da Kiru da kano a zabe mai zuwa. A hanu guda kuma Kofa ya kaddamar da tsare tsare na musamman akan zabe mai zuwa kuma yayi kira da babbar murya ga jami'an tsaro da ma'aikatan zabe wanda aka turo su Kano, akan su tabbatar sun tsaya akan gaskiya don samun zaman lafiya a kano