Search This Blog

Showing posts with label Paris. Show all posts
Showing posts with label Paris. Show all posts

Sunday, 21 May 2023

Tinubu Ya Gana Da Ganduje A Abuja

 


Shugaban kasa mai jiran gado, Asiwaju Bola Ahmad Tinubu, ya gana da Gwamnan Jihar Kano mai barin gado, Abdullahi Umar Ganduje a gidansa na Defense House da ke Abuja.

Da yammacin Asabar ɗin nan dai Ganduje ya shiga sahun waɗanda suka taro Asiwaju Tinubu lokacin da ya sauka Abuja daga ƙasar Faransa.

Bayan an isa gida kuma sun yi ganawar sirri tsakaninsu.

Ganawar dai ba ta rasa nasaba da ƙorafin da Ganduje yake da shi game da ganawar Asiwaju Tinubu da tsohon gwamnan Kano Injiniya Rabiu Musa Kwankwaso a birnin Paris.

A baya-bayan nan dai aka ji wani sautin hirar wayar tarho na yawo inda Ganduje ke kukan zaɓaɓɓen shugaban ƙasar bai kyauta masa ba da ya yi wannan tattaunawar.

Kawo yanzu dai Ganduje bai bayyana wa manema labarai matsayar da suka cimma da Asiwaju Tinubu ba.

AMINIYA

Tuesday, 16 May 2023

Da dumi-dumi: Kwankwaso yayi ganawar sa’o’i hudu da Tinubu a birnin Paris

Zababben shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, da Rabiu Musa Kwankwaso, wanda ya yiwa jam’iyyar NNPP a zaben shugaban kasa da aka gudanar a ranar 25 ga watan Fabrairu, sun yi ganawar akalla sa’o’i hudu a birnin Paris na kasar Faransa a ranar Litinin, kamar yadda jaridar TheCable ta ruwaito.

A tsakiyar tattaunawar, TheCable ta fahimci cewa, akwai yuwuwar shigar Kwankwaso cikin gwamnati mai zuwa yayin da Tinubu ke shirin kafa “gwamnatin hadin kan kasa” – wanda ke nufin bai wa jam’iyyun adawa wasu mukamai a cikin gwamnatin.


Taron ya kuma tattauna batutuwan da suka shafi zaben shugabannin majalisar kasa, gabanin kaddamar da majalisar ta 10 a ranar 13 ga watan Yuni.

Zaben gwamnan kano: Inda aka Kwana game da karar APC da NNPP a Kotu

An fara taron Paris tsakanin Tinubu da Kwankwaso ne da karfe 12:30 na rana kuma aka kammala da karfe 4:45 na yamma, kamar yadda wasu majiyoyi suka shaida wa jaridar TheCable.

Ko Kun zabi aiki ko ba ku zaba ba, mun yi titin Kurna babban layi ne saboda Allah -Ganduje

Femi Gbajabiamila, kakakin majalisar wakilai kuma shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, ya halarci taron yayin da Abdulmumin Jibrin, dan takarar jam’iyyar NNPP kuma tsohon jigo a kwamitin yakin neman zaben Tinubu na daga cikin wadanda suka raka Kwankwaso.

Oluremi Tinubu, Sanata kuma matar zababben shugaban kasa ita ce ta tarbi matar Kwankwaso, Salamatu.

Idan za’a iya tunawa Tinubu da Kwankwaso sun yi aiki a matsayin gwamnonin kano da Lagos a Shekarar 1992.


Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

FG Urges KOICA, FAO to Align Agricultural Intervention with Nigeria’s Development Priorities, Ward-Based Strategy

The Federal Government has called for stronger alignment between development partners’ interventions and Nigeria’s national deve...