Search This Blog

Showing posts with label Farashin Man Fetur. Show all posts
Showing posts with label Farashin Man Fetur. Show all posts

Monday, 24 July 2023

Labari da dumiduminsa : Ahmed Musa ya rage farashin man fetur a Kano

Shahararren dan wasan kwallon kafa na Najeriya, Ahmed Musa ya sanar da rage farashin farashin Motoci na Premium Motor Spirit (PMS) a gidan man shi , MYCA7 a Kano daga N620 zuwa N580 kowace lita.

Daily News 24 ta ruwaito cewa kwararren dan kwallon ya bayyana hakan ne a shafin sa na twitter da aka tabbatar.

Ta hanyar Twitter, Musa ya ce, "Fuel ⛽️ #580 @MYCA -7 Filling Station Kano 🏃‍♀️🏃‍♀️," wanda ya haifar da farin ciki a tsakanin 'yan Najeriya.
Wani mai amfani da Twitter, Scala @lakaas123, cikin zumudi ya tambaya Yaya Alhaji? N580 a Kano ba a Legas ba? Kana yi mana arashi ne?" Musa ya ce, "Ni ne na yanke shawarar sayar da nawa haka."

Wannan dai na zuwa ne kwanaki kadan bayan da Kamfanin Mai na Najeriya (NNPCL) ya sanar da karin farashin man fetur zuwa Naira 617 kan kowace lita.

Jaridar Daily News 24 ta tattaro cewa dan wasan ya rage farashin man fetur don bayar da tallafi ga masu abin hawa a jihar.

Masu ababen hawa sun yaba da wannan tunanin nasa, kamar yadda Usman Muhammad ya bayyana bayan siyan mai, “Abin farin ciki ne; Yanzu zan iya ajiye wasu kuɗi maimakon in saya a farashi mai yawa."

Ahmed Musa kwararren dan kwallon Najeriya ne wanda ke taka leda a matsayin dan wasan gaba da hagu zuwa kulob din Sivasspor na Süper Lig na Turkiyya da kuma kungiyar kwallon kafa ta Najeriya.

Tuesday, 18 July 2023

Yanayin Kasuwa Ne Ya Sa Man Fetur Ya Kara Tashi — NNPC

Shugaban Kamfanin Man Fetur na Kasa (NNPCL), Mele Kyari, ya danganta tashin farashin man fetur daga Naira 540 zuwa Naira 617 da yanayin kasuwa.

Ya bayyana haka ne ga manema labarai a Fadar Shugaban Kasa da ke Abuja a ranar Talata, bayan wata ganawa da Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima.


“Farashin ya danganta da yanayin kasuwa. Wannan shi ne ma’anar tabbatar da cewa kasuwa ta daidaita kanta. Farashin zai iya hawa kuma a wani lokacin zai iya sauka. Ba batun samar da mai ba ne.

“Idan ka je kasuwa, ka sayi kaya, za ka zo kasuwa ka sayar da shi a kan farashin da kasuwa ta ke. Ba shi da alaka da wadatarsa. Mun samu sama da kwanaki 32 muna shigo da mai. Wannan ba matsala ba ce,” in ji shi.

Kyari, ya ce abu ne mai kyau ga ‘yan kasuwa su daidaita farashin.

“Ina tabbatar wa ’yan Najeriya cewa wannan ita ce hanyar da ta dace don daidaita farashin yanayin kasuwa. Ba ni da cikakken bayanai a wannan lokacin, amma na san cewa wannan ba mai dorewa ba ne. Na san cewa kamfanoni da yawa sun shigo da man fetur kuma komai zai daidaita nan bada jimawa.”

Martanin nasa na zuwa ne baya da wasu gidajen man NNPC aka wayi gari sun kara farashin man fetur daga 540 zuwa 617 a Abuja.


A nasa bangaren, babban jami’in hukumar kula da harkokin man fetur ta kasa, Farouk Ahmed, ya ce karin farashin ya faru ne sakamakon tashin farashin danyen mai.

Ya kuma ba da misali da sauye-sauyen farashin kaya tare da wasu karin kudadeen da masu shigo da kaya ke yi.

“Don haka, idan kuka ce yanayin kasuwa ya yi aiki, wannan shi ne ainahin abin da ake nufi, ya hau ko ya sauka… Kuna ganin farashin danyen mai ya tashi.

“Cikin mako daya farashin danyen mai ya kai kusan Dala 70 kan kowace ganga. Yanzu, yana kan Dala $80 kowace ganga.


“Don haka, babu shakka farashin danyen mai ne haifar da karin farashin kayayyaki. Kamar yadda masu shigo da kayayyaki ke shigo da su, suna dogara ne akan farashin shigo da kayayyaki da sauran abubuwan kashe kudi ta fuskar rarraba su a cikin gida,” cewar Ahmed.

A ranar Talata ne ‘yan kasuwa mai masu zaman kansu suka tabbatar da karin farashin man fetur, yayin da suka bayyana cewa duk wani canjin farashin da gidajen man NNPC suka yi na nuni da tashin farashin man.

A jawabinsa na farko a ranar 29 ga watan Mayu, shugaba Bola Tinubu ya sanar da dakatar da tallafin man fetur.

Wannan ya haifar da hauhawar farashin man fetur daga Naira 198 kan kowace lita zuwa sama da Naira 500 kan kowace lita a ranar 30 ga Mayu, 2023.
(AMINIYA) 


Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

FG Urges KOICA, FAO to Align Agricultural Intervention with Nigeria’s Development Priorities, Ward-Based Strategy

The Federal Government has called for stronger alignment between development partners’ interventions and Nigeria’s national deve...