Posts

Showing posts with the label Max Air

Bamu Siyar Da Gurbataccen Mai Ga Max Air Ba - Kamfanin Man Jirgin Sama Na Octavus

Image
Octavus Petroleum Limited ya musanta zargin da ake yi masa na sayar da gurbataccen man jirgi ga kamfanin sufurin jiragen na Max Air Limited. A cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun Peter Dia, Babban Manajan kamfanin, Octavus ya ce babu wata shaida da ta nuna cewa man da Octavus ya haifar da "abubuwan da aka ruwaito". A cewar Octavus, ya samu nasarar bada kusan kashi 90% na man da jiragen Max Air ke amfani da shi wajen jigilar alhazai Hajj, inda ya kara da cewa har yanzu wadannan jiragen na jigila ba tare da wata matsala ba. Kamfanin ya bayyana cewa ya da kayan sa ana zirga-zirgar jiragen sama kusan sawu 100 a kowace rana, a matakin jirgi daya kowane minti 10, ba tare da rahoton koke-koke kan ingancin  man ba. A cikin sanarwar da kamfanin ya fitar ta ce, “Sau biyar Æ™ungiyar  kamfanonin sufurin jiragen sama ta Najeriya (AON) na zaÉ“ar kamfanin mu  don gudanar da aikin samar da man jirgi na jiragen kaya da NNPC ke yi a daidai lokacin da ake fama da matsalar man fe

Hajj2023 : Hukumar NAHCON Ta Sahalewa Kamfanin Max Air Yin Jigilar Alhazan Kano

Image
Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON, ta baiwa kamfanin Max Air damar jigilar maniyyatan jihar Kano 5,917 zuwa kasar Saudiyya a lokacin aikin Hajjin bana. Idan ba a manta ba, matakin da NAHCON ta dauka na baiwa kamfanin Azman Air jigilar Alhazan jihar a shekarar da ta gabata ya fuskanci suka daga hukumar jin dadin alhazai ta jihar Kano da gwamnatin jihar. A wata ganawa da manema labarai a ranar Talata, babban sakataren hukumar, Muhammad Abba Dambatta, ya bayyana cewa hukumar alhazan ta baiwa kamfanin Max Air aikin hajjin bana. Ya kara da cewa kamfanin yana da inganci kuma yana da jiragen da za su iya jigilar alhazai sama da 1,000 a kowace rana. Hakazalika, Dambatta ya kuma sanar da cewa hukumar ta rufe sabon rajistar aikin Hajji bisa umarnin NAHCON. A cewarsa, Alhazan Jihar sun ci gajiyar kusan guraben aikin Hajji 6,000 da Hukumar Hajji ta ware musu, inda ya ce maniyyata 4,900 ne suka biya kudin Hajjin gaba daya, yayin da sauran wadanda suka ajiye Naira miliyan 2.5 za su biya