Search This Blog

Showing posts with label Kannywood. Show all posts
Showing posts with label Kannywood. Show all posts

Thursday, 7 September 2023

Kungiyar Kannywood Ta Bawa Kwamishinan Kudi Na NAHCON Lambar Yabo

Da yake jawabi, jagoran tawagar Alhaji Ahmed Kaka ya taya hukumar murnar kammala aikin Hajjin 2023 cikin nasara duk da kalubalen da ake fuskanta.

A sanarwar da Shafi'i Sani Muhammad na sashen yada labarai da Dab'i na Hukumar NAHCON ya sanyawa hannu, Shugaban kungiyar ya yi kira da a hada kai a tsakanin bangarorin guda biyu musamman ta fannin wayar da kan alhazai da tsawaita amfani da kafafen sada zumunta na zamani.

Kungiyar ta baiwa Alhaji Nura Hassan Yakasai, Kwamishinan kudi lambar yabo ta taimakon jin kai bisa gudunmawar da ya bayar wajen bayar da muhimmin taimako ga marasa galihu a cikin al’umma.

Alhaji Yakasai wanda ya bayyana jin dadinsa ga dandalin ya tabbatar musu da shirye-shiryen Hukumar na yin bincike da hada kai da kungiyar nan gaba.


Tunda farko da yake nasa jawabin, Shugaban Hukumar NAHCON, Alhaji Zikrullah Kunle Hassan ya yi kira ga ‘yan wasan kwaikwayon Najeriya da su ci gaba da amfani da kafar sadarwar su wajen wayar da kan ‘yan Nijeriya musamman Alhazai ta hanyar fasaharsu.
Ya bayyana haka ne a yau a lokacin da kungiyar Kannywood Action Forum karkashin jagorancin Alhaji Ahmed Kaka ta kai ziyarar ban girma ga hukumar NAHCON a  Abuja.

Shugaban ya bayyana imaninsa cewa tare da dimbin masu sauraronsu musamman a Arewacin Najeriya, ayyukansu ko labaransu za su taimaka matuka wajen nuna kyakykyawan kimar kasar da kuma taimakawa wajen kawo canji ga al’umma.


Monday, 7 August 2023

Dawo Da Makarantar Koyar Da Sana'ar Fim Dake Tiga, Babbar Nasara Ce Ga Masana'antar Kannywood- Abba El-Mustapha

Shugaban Hukumar tace Fina-finai da Dab'i ta Jahar Kano, Abba El-mustapha ya bayyana farin cikinsa tare da karfin gwiwa dangane da kara bude makarantar koya Sana'ar Fina-finai dake garin Tiga a Jahar Kano.

A sanarwar da jami'in hulda da jama'a na Hukumar, Abdullahi Sani Sulaiman ya sanyawa hannu, tace nada sabon Daraktan Makarantar Alh. Dr. Maigari Indabawa yace, hakika abu ne da ya dace duba da yadda Sana'ar fina-finan ke bukatar sauyi ta fannin ilimi Wanda hakan zai bunkasa tattalin arzikin Kano tare da kawo kudin shiga.

Ya Kara da cewa, da yawa daga cikin yan masana'antar na bukatar Samin karin horo domin a nuna musu sabbin da baru ta yadda  Sana'ar zata tafi da zamani haka kuma su kansu yan masana'antar zasuyi gogayya da takwarorin su na kasashen waje .

Abba El-mustapha ya godewa Gwamna tare da yiwa sabon shugaban makarantar fatan alheri tare da addu'ar Allah yasa yafara a sa'a ya Kuma gama lafiya.

El-mustapha ya kuma yi wa sauran wadanda aka nada a mukamai daban-daban fatan alheri tare da addu'ar samun Nasara adukkan aiyukan su. 

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

FG Urges KOICA, FAO to Align Agricultural Intervention with Nigeria’s Development Priorities, Ward-Based Strategy

The Federal Government has called for stronger alignment between development partners’ interventions and Nigeria’s national deve...