A Karhse Dai Emefiele Ya Bayyana A Gaban Kwamitin Majalisar Wakilai Kan Batun Sababbin Kudi

A ranar Talata ne gwamnan babban bankin Najeriya Godwin Emefiele ya gurfana gaban kwamitin majalisar wakilai, inda suke binciken yadda aka yi musanya da Naira.

A halin yanzu dai kwamitin da tawagar CBN na gudanar da taro a majalisar dokokin kasar.

An fara taron ne da misalin karfe 12:05 na rana bayan shafe sama da awa daya a sirrance.

Idan dai za a iya tunawa majalisar da kwamitin sun yi barazanar kama wasu da dama a ranar Alhamis bayan Mista Emefiele ya kauracewa majalisar.

Shugaban bankin na CBN ya sanar da tsawaita wa’adin canza canjin kudin zuwa ranar 10 ga watan Fabrairu. Sai dai kwamitin ya dage cewa dole ne Emefiele ya bayyana a gabansu.

A lokacin da aka fara taron, Shugaban Kwamitin, Ado Doguwa ya ce shugaban CBN ya bayar da dalilan rashin amsa gayyata a baya.

Cikakken labarin zai zo muku nan gaba kadan 

SOLACEBASE 

Popular posts from this blog

Yanzu - Yanzu: Bankuna Zasu Karbi Tsofaffin Kudi Ko da Bayan Karewar Wa'adi - Emefiele

Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki