Posts

Showing posts with the label Bawa

Buhari ya gana da Emefiele da EFCC kan karancin Naira

Image
  Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya yi ganawar sirri  da Gwamnan Babban Bankin Kasar, CBN, Godwin Emefiele da shugaban Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa , EFCC, AbdulRasheed Bawa da Sakataren Gwamnatin Tarayya, Boss Mustapha da kuma shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, Farfesa Ibrahim Gambari  game da halin da kasar ke cikin na karancin takardar kudin Naira Kazalika gwamnan Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal da takwaransa na Kebbi, Atiku Bagudu, su ma sun halarci zaman na yau Talata. An gudanar da wannan zaman ne a daidai lokacin da  ake fama fa matsanancin karancin takardar kudin Naira wanda ya haddasa zanga-zanga a wasu sassan Najeriya tare da kaddamar da hari kan wasu bankuna da jami’an tsaro. A Juma’ar da ta gabata  ne, shugaba Buhari ya roki ‘yan kasarr da su ba shi wa’adin kwanaki bakwai domin magance matsalar karancin takadar Nairar wadda ta samo asali sakamakon shirin Babban Bankin CBN na sauya fasalin Naira 1000 da 500 da kuma 200. Nan da ranar 10 ga wannan wata ne, wa’a