Search This Blog

Showing posts with label Borno. Show all posts
Showing posts with label Borno. Show all posts

Thursday, 11 January 2024

Bom Ya Kashe Mutane 8, Wasu Dama Sun Jikkata A Borno

 


Akalla mutane takwas ne ake fargabar sun mutu sakamakon fashewar wasu bama-bamai a kan hanyar Ngala zuwa Dikwa a Karamar Hukumar Ngala a Jihar Borno.

Rahotannin sun nuna cewar, mutane da dama sun samu raunuka a sakamakon tashin bom din a kauyen Kinewba a ranar Talata.

Wata majiyar tsaro ta ce “Akalla Mutane  8 ne ake fargabar sun mutu, ciki har da yara biyu, sannan wasu da dama sun samu munanan raunuka sakamakon fashewar nakiyoyin.”

Majiyar ta ce fashewar bom din ya yi kaca-kaca da wasu motocin biyu yaddda ba za a iya gyara su ba.

Wata babbar majiya ta jami’an farin kaya na  JTF ta ce motocin biyu kirar Isuzu da wata babbar mota ce suka taka bom din kuma ana fargabar kashe kusan dukkan fasinjojin ciki.

“Wadannan motocin dai sun bar garin Ngala da misalin karfe 9 na safe, yayin da lamarin ya faru a nisan kilomita 15,” in ji majiyar.

Majiyarmu ya ruwaito cewa, tashin bama-baman ya faru ne a tazarar kilomita 15 daga Maiduguri, babban birnin jihar.

(AMINIYA)

Sunday, 3 December 2023

Yanzu-Yanzu: Zulum ya amince da nadin Mohammed Dawule a matsayin mai rikon Hukumar Alhazai ta Jahar Borno

Gwamnan jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya amince da nadin Mohammed Dawule Maino a matsayin mukaddashin sakataren hukumar jin dadin alhazai ta jihar Borno.

An bayyana nadin ne a ranar Lahadin da ta gabata a wata sanarwa da sakataren gwamnatin jihar Borno, Hon. Bukar Tijjani.

Sakataren gwamnatin jihar ya kara da cewa nadin wanda ya fara aiki nan take, ya dogara ne akan cancanta da kuma bayanan shekarun baya a aikin gwamnati.

Har zuwa lokacin da Dawule ya nada shi mamba ne a sabuwar Hukumar Ilimi ta Larabci da Sangaya ta Jihar Borno (BOSASEB. Kafin nan, Dawule ya yi aiki a Ma’aikatar Ilimi ta Jihar Borno tsakanin 2015 zuwa 2022.

Ya kuma yi aiki a Makarantar Sakandare ta islamiyya da ke Maiduguri da Kwalejin Gwamnati da ke Maiduguri da kuma Makarantar Alkur’ani ta Model da ke Konduga.

An haifi Mista Dawule mai shekaru 50 a duniya a karamar hukumar Kaga da ke arewacin jihar Borno.

Gwamna Zulum ya taya Mohammed Dawule Maino murna sannan ya ce yana fatan ci gaba da yi masa hidima tare da nagartar al’ummar jihar Borno.

Insight Northeast 

Sunday, 21 May 2023

An Wajabta Wa Mata Musulmi ’Yan Sakandare Yin Shigar Musulunci A Borno

Gwamnatin Borno ta wajabta yin lullubi ga ’yan mata Musulmai da ke makarantunta na sakandare a fadin jihar. 

Daraktan Kula da Makarantu na Ma’aikatar Ilimi ta Jihar Borno, Bukar Mustapha-Umara, ya bayyana cewa, ƙarƙashin sabon tsarin, wajibi ne kowace ɗalibar sakandare Musulma ta sanya wando da riga da ɗankwali da lullubi a duk makarantar da take a fadin jihar.

“Wannan shigar ta zama wajibi ga dukkan ɗalibai mata Musulmi a duk makarantunmu na sakandare da ke Jihar Borno.

“Amma ga ɗalibai Kirista mata zaɓi ne; In sun so sa su iya kasancewa da shigar da suke da ita a yanzu ko kuma su canza wando kawai.”

Tinubu ya gana da Ganduje a Abuja
Da sanin Ganduje Tinubu ya gana da Kwankwaso —Kofa
Daraktan ya kara da cewa cewa wajibi ne shugabannin makarantun su tabbatar da bin ƙa’idojin sabuwar shigar.

Ya kuma bayyana cewa sabuwar dokar sanya tufafin dole ga ɗalibai Musulmi za ta fara aiki daga zangon karatu na farkon shekarar karatu ta 2023/2024 da ke tafe.

Sannan ya yi kira ga iyaye da su yi cikakken shirin fara amfani da sabuwar shigar makarantar kafin a ahekarar karatu ta 2023/2024
AMINIYA 

Friday, 6 January 2023

Ana shirin mayar da tubabbun mayaƙan Boko Haram 613 cikin al'umma

Hukumomi a Najeriya sun kammala shirin miƙa wasu mayaƙan Boko Haram fiye da 600 da suka tuba ga gwamnatocin jihohinsu domin shigar da su cikin sauran al`umma.

Hedikwatar tsaron Najeriyar ta bayyana cewa an ɗauki wannan matakin ne bayan an shigar da su cikin wani shirin gyara hali.

 BBC Hausa ta rawaito Hafsan hafsoshin Najeriya, Janar Lucky Irabor ya bayyana cewa an kammala shirin miƙa mayakan Boko Haram ɗin da suka tuba su 613, bayan an gyara musu hali.

Ya yi bayanin ne a wajen wani taron masu hannu ko ruwa da tsaki a ƙarƙashin tsarin nan na ba da damar miƙa wuya ko tuba ga mayaƙan Boko Haram, wato Operation Safe Corridor.

Ya ce za a mika su ne ga jihohinsu na asali domin shigar da su cikin al`umma, kuma a halin da ake ciki ana gab da kammala aikin sauya musu tunani da zare musu tsattsaurar akida.

 A cewar Hafsan hafsoshin, tubabbun mayakan Boko Haram ɗin na bukatar kulawa sosai a wannan gaɓa ta gyara hali da sake shiga cikin jama`a, don haka sai jihohin sun tsaya sosai a kan su.

Batun gyara hali aikin ne jawur, saboda ko a nasu matakin sai da suka haɗa da kwararru daga fannoni daban-daban, da ma'aikatu da hukumomin gwamnati masu yawa, da kuma taimakon kungiyoyin agaji na kasa da kasa.

Ya ce za yi nasarar shigar da tsoffin mayakan cikin al'umma idan jihohi suka yi tsari mai kyau, tare da haɗa gwiwa da sarakunan gargajiya wajen sa-ido a kan tubabbun yayin da suke sajewa a cikin al'umma.

Janar Irabor ya ce idan aka zo sallama ko yaye tsoffin ƴan Boko Haram din, za a ba su guzurin kayan abinci da kayan zaman gida da kuma kayan aiki irin sana'ar da suka koya don fuskantar gangariyar rayuwa.

Game da yakin da ake yi da kungiyar Boko Haram kuwa, Hafsan hafsoshin ya ce askarawan gwamnati na samuN nasara a kan su, kuma da dama sai mika wuya suke yi sakamakon mamayar dajin Sambisa da zaratan sojojin suka yi da fatattakar su da ake yi inda ta kai ga fiye da mayakan Boko Haram da iyalansu 80,000 sun mika wuya.


Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

FG Urges KOICA, FAO to Align Agricultural Intervention with Nigeria’s Development Priorities, Ward-Based Strategy

The Federal Government has called for stronger alignment between development partners’ interventions and Nigeria’s national deve...