Posts

Showing posts with the label Borno

Bom Ya Kashe Mutane 8, Wasu Dama Sun Jikkata A Borno

Image
  Akalla mutane takwas ne ake fargabar sun mutu sakamakon fashewar wasu bama-bamai a kan hanyar Ngala zuwa Dikwa a Karamar Hukumar Ngala a Jihar Borno. Rahotannin sun nuna cewar, mutane da dama sun samu raunuka a sakamakon tashin bom din a kauyen Kinewba a ranar Talata. Wata majiyar tsaro ta ce “Akalla Mutane  8 ne ake fargabar sun mutu, ciki har da yara biyu, sannan wasu da dama sun samu munanan raunuka sakamakon fashewar nakiyoyin.” Majiyar ta ce fashewar bom din ya yi kaca-kaca da wasu motocin biyu yaddda ba za a iya gyara su ba. Wata babbar majiya ta jami’an farin kaya na  JTF ta ce motocin biyu kirar Isuzu da wata babbar mota ce suka taka bom din kuma ana fargabar kashe kusan dukkan fasinjojin ciki. “Wadannan motocin dai sun bar garin Ngala da misalin karfe 9 na safe, yayin da lamarin ya faru a nisan kilomita 15,” in ji majiyar. Majiyarmu ya ruwaito cewa, tashin bama-baman ya faru ne a tazarar kilomita 15 daga Maiduguri, babban birnin jihar . (AMINIYA)

Yanzu-Yanzu: Zulum ya amince da nadin Mohammed Dawule a matsayin mai rikon Hukumar Alhazai ta Jahar Borno

Image
Gwamnan jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya amince da nadin Mohammed Dawule Maino a matsayin mukaddashin sakataren hukumar jin dadin alhazai ta jihar Borno. An bayyana nadin ne a ranar Lahadin da ta gabata a wata sanarwa da sakataren gwamnatin jihar Borno, Hon. Bukar Tijjani. Sakataren gwamnatin jihar ya kara da cewa nadin wanda ya fara aiki nan take, ya dogara ne akan cancanta da kuma bayanan shekarun baya a aikin gwamnati. Har zuwa lokacin da Dawule ya nada shi mamba ne a sabuwar Hukumar Ilimi ta Larabci da Sangaya ta Jihar Borno (BOSASEB. Kafin nan, Dawule ya yi aiki a Ma’aikatar Ilimi ta Jihar Borno tsakanin 2015 zuwa 2022. Ya kuma yi aiki a Makarantar Sakandare ta islamiyya da ke Maiduguri da Kwalejin Gwamnati da ke Maiduguri da kuma Makarantar Alkur’ani ta Model da ke Konduga. An haifi Mista Dawule mai shekaru 50 a duniya a karamar hukumar Kaga da ke arewacin jihar Borno. Gwamna Zulum ya taya Mohammed Dawule Maino murna sannan ya ce yana fatan ci gaba da yi masa hid

An Wajabta Wa Mata Musulmi ’Yan Sakandare Yin Shigar Musulunci A Borno

Image
Gwamnatin Borno ta wajabta yin lullubi ga ’yan mata Musulmai da ke makarantunta na sakandare a fadin jihar.  Daraktan Kula da Makarantu na Ma’aikatar Ilimi ta Jihar Borno, Bukar Mustapha-Umara, ya bayyana cewa, Æ™arÆ™ashin sabon tsarin, wajibi ne kowace É—alibar sakandare Musulma ta sanya wando da riga da É—ankwali da lullubi a duk makarantar da take a fadin jihar. “Wannan shigar ta zama wajibi ga dukkan É—alibai mata Musulmi a duk makarantunmu na sakandare da ke Jihar Borno. “Amma ga É—alibai Kirista mata zaÉ“i ne; In sun so sa su iya kasancewa da shigar da suke da ita a yanzu ko kuma su canza wando kawai.” Tinubu ya gana da Ganduje a Abuja Da sanin Ganduje Tinubu ya gana da Kwankwaso —Kofa Daraktan ya kara da cewa cewa wajibi ne shugabannin makarantun su tabbatar da bin Æ™a’idojin sabuwar shigar. Ya kuma bayyana cewa sabuwar dokar sanya tufafin dole ga É—alibai Musulmi za ta fara aiki daga zangon karatu na farkon shekarar karatu ta 2023/2024 da ke tafe. Sannan ya yi kira ga iyaye

Ana shirin mayar da tubabbun mayaƙan Boko Haram 613 cikin al'umma

Image
Hukumomi a Najeriya sun kammala shirin miÆ™a wasu mayaÆ™an Boko Haram fiye da 600 da suka tuba ga gwamnatocin jihohinsu domin shigar da su cikin sauran al`umma. Hedikwatar tsaron Najeriyar ta bayyana cewa an É—auki wannan matakin ne bayan an shigar da su cikin wani shirin gyara hali.  BBC Hausa ta rawaito Hafsan hafsoshin Najeriya, Janar Lucky Irabor ya bayyana cewa an kammala shirin miÆ™a mayakan Boko Haram É—in da suka tuba su 613, bayan an gyara musu hali. Ya yi bayanin ne a wajen wani taron masu hannu ko ruwa da tsaki a Æ™arÆ™ashin tsarin nan na ba da damar miÆ™a wuya ko tuba ga mayaÆ™an Boko Haram, wato Operation Safe Corridor. Ya ce za a mika su ne ga jihohinsu na asali domin shigar da su cikin al`umma, kuma a halin da ake ciki ana gab da kammala aikin sauya musu tunani da zare musu tsattsaurar akida.  A cewar Hafsan hafsoshin, tubabbun mayakan Boko Haram É—in na bukatar kulawa sosai a wannan gaÉ“a ta gyara hali da sake shiga cikin jama`a, don haka sai jihohin sun tsaya sosai