Search This Blog

Sunday, 30 April 2023

Gyara a dokar aikin Hajji zai rage tsadar tafiya Makkah a Najeriya - Sanata Dan Baba

Dan Majalisar Dattijai mai wakiltar Sokoto ta Kudu a Majalisar Dokokin Najeriya Sanata Ibrahim Abdullahi Dan Baba ya sha alwashin yin duk abin da zai iya wajen ganin an yi wa dokar aikin Hajji kwaskwarima a sabuwar majalisa ta goma da za ta fara aiki.

Sanatan wanda ya kasance a tsohuwar majalisa ta tara wacce za ta gama aikinta cikin watan Mayun shekaran nan ta 2023 ya ce tun da farko ya gabatar da kudurin gyaran a gaban majalisar mai karewa.

Sanata Dan Baba ya kara da cewa lokaci ya yi da ya kamata a samar wa mahajjata sauki wajen biyan makudan kudade domin aikin Hajji.

A cewar dan majalisar, yin gyara ga dokar Hukumar Aikin Hajji ta kasar shi ne zai magance yadda ake samun karuwar kudin tafiya Hajjin.

 Ya ce ya bukaci majalisa ta gudanar da bincike kan badakalar da ke cikin aikin Hajji a Najeriya kuma majalisar ta kafa wani kwamitin bincike.

"Biciken ya gano ana sama da fadi da kudaden mahajjata, otel da ya kamata a kama na kwana arba'in sai a kama na tsawon kwana casa'in sauran kwanakin kuma sai a sanya Larabawa a dakunan bayan alhazai sun tafi, sai a raba kudin tsakanin masu otel da kuma shugaban Hukumar Alhazai na wancan lokacin inda otel zai dauki kashi 25 shi kuma shugaba ya dauki kashi 75" A cewar Sanata Baba. 

Saudiyya ta bai wa Najeriya kujeru 95,000 a Hajjin 2023
21 Disamba 2022
Mene ne bambancin yin Umrah cikin azumi da sauran lokuta?
16 Aprilu 2023
Ana nuna mana bambanci a Saudiyya – Alhazan Najeriya
11 Yuli 2022
Dan majalisar ya ce kadan daga cikin kudaden da aka gano an wawure sun kai Naira biliyan daya.

Sanatan ya kara nuna bukatar yin kwaskwarima ga dokar wadda za ta hana duk wanda zai shugabanci hukumar ya yi abin da aka yi a baya.

Dan majalisar yana ganin Naira miliyan uku sun yi tsada ga masu zuwa aikin Hajji kuma da an dauki matakan da suka dace da kudin aikin Hajjin bai kai haka tsada ba a cewarsa.

Ya kuma kara da cewa lallai sai ya sake tayar da maganar a sabuwar majalisa har sai an bai wa mahajjata hakkinsu.

An shafe shekaru da dama ana kwan-gaba-kwan-baya kan batun yin gyara ga dokar a gaban majalisar dokokin ta Najeriya.
BBC 

APC Group Calls For All Stakeholders To Consider Senator Barau As Next Senate President

Kano Chapter of APC national supporters center calls for all stakeholders to consider senator Barau Jibirin as the next Senate president of the 10th Senate.

In a statement signed by its State Coordinator, Aliyu A Aliyu, the Group argued that his widespread acceptance, pragmatic leadership skills have made him the best to be considered as the next Senate president.

Accordingly his perfection to duty especially as Chairman Senate committee on appropriation defined his competency.

North West support for APC especially Kano that produced about two million votes in 2015,over a million votes in 2019 and five hundred and thirteen thousand votes this year need to be considered by the party's leadership in the incoming administration of Bola Ahmed Tinubu.

The Group advice APC and the president elect not to neglect Kano by doing so it can jeopardize the party chances in the future.

It called on senators to support Barau Jibirin in his effort to bring about purposeful leadership.

Under the current administration of President Buhari Lagos alone got vice president, speaker House of Representatives and National leader of the party.

Accordingly the Group will organize a peaceful two million man march in support of Barau Jibirin in Kano state as he is the only Candidate that win thirteen local Governments of his senatorial zone.

Democracy is the Government of the people by the people to the people.


Wutar Lantarki: Katse Layin KEDCO A Kano Somin-Tabi Ne —TCN

Kamfanin Samar da Wutar Lantarki na Kasa (TCN) ya ce katse wutar da ya yi wa Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na KEDCO a Jihar Kano somin-tabi ne.

Wasu sassan Jihar Kano sun yi kwanaki a cikin duhu bayan TCN ya katse layin wutar da suke kai saboda taurin bashin da yake bin KEDCO.

TCN ya katse wasu layikan wutar KEDCO mai kula da jihohin Kano da Jigawa da Katsina bayan kokarinsa na ganin kamfanin ya biya bashin ya faskara.

Mataimakin Janar-Manajan TCN na Shiyyar Kano, Bello Muhammad da kuma kakakin KEDCO, Sani Bala Sani, sun tabbatar cewa TCN ya katse wutar a ranar 26 ga watan Afrilu da muke ciki.


Layukan wutar da TCN ya kashe a Kano su ne Club Road da CBN da kuma Flour Mills (Dan Agundi), wanda hakan ya jefa yankunan da ke samun wuta daga nan a cikin duhu na tsawon kwanaki.

Tun ranar 24 ga watan ranar 24 ga wata Babban Jami’in Kasuwanci na TCN, E. A. Eje ya sanar cewa, “TCN ya ba da umarnin katse wutar KEDCO saboda saba ka’idar biyan bashi.”

Ya bayyana cewa katse layikan somin-tabi ne kafin TCN ya katse wutar gaba daya idan kamfanin bai biya bashin ba.

Ya bayyana cewa katse layikan somin-tabi ne kafin TCN ya katse wutar gaba daya idan kamfanin bai biya bashin ba.


Ya ce, “Mun riga an sanar da KEDCO da duk wadanda ake bi bashi game da saba alkawarin nasu; Mun kuma wallafa a jarida inda muka bayyana ranar da za mu yanke musu wuta bisa tsarin kasuwancin, kuma har wa’adin ya wuce.”


Amma mai magana da yawun KEDCO, Sani Bala Sani, ya ce, “Duk da haka, kamfanin na aiki tare da TCN da sauran masu ruwa da tsaki domin ganin an daidaita nan ba da jimawa ba.”

Sani ya ba wa jama’a hakuri, da alkawarin tabbatar da sama musu wutar lantarki mai inganci.
AMINIYA 

Saturday, 29 April 2023

Gwamnatin Tinubu Ce Za Gudanar Da Kidaya —Buhari

 


Shugaba Muhammadu Buhari ya amince a dage lokacin gudanar da Kidayar Jama’a da Gidaje da aka shirya farawa ranar 3 ga watan Mayu mai kamawa.

Kwana hudu kafin fara aikin Buhari ya ce ya bai wa gwamnati mai jiran gado damar yanke shawara kan lokacin gudanar da kidayar domin tabbatar da nasararsa.

Ya sake dage lokacin gudanar da kidayar ne bayan wata ganawa da tsakanin Shugaba Buhari da shugaban hukumar, Nasir Isa Kwarra tare da Majalisar Zartarwa ta Tarayya a ranar Juma’a a Fadar Shugaban Kasa.

Sanarwar da Ministan Yada Labarai da Raya Al’adu, Lai Mohammed ya fitar ta ce duk da haka Shugaba Buhari ya jaddada muhimmancin gudanar da kidayar wadda rabon da a gudanar shekara 17 ke nan.

Shugaban ya kuma yaba da kyakkyawatan shirin da hukumar ta yi wa kidayar, wanda zai tabbatar da ingancinsa kamar na sauran kasashen duniya.

Wata majiya a hukumar ta ce an dage aikin kidayar ne saboda wasu matsalolin da hukumar ke fuskanta da za su hana ta gudanar da aikin a lokaci guda; sai dai ba ta yi karin bayani ba.

Idan za a tuna, Hukumar Kidaya ta Kasa ta dage aikin daga 27 ga watan Maris zuwa ranar 3 ga watan Mayu, saboda kauce wa cin karo da zaben gwamnoni da aka kara wa lokaci.

A baya-bayan nan hukumar ta dakatar da horar da ma’aikatan wucin-gadi da za su gudanar da aikin, saboda matsalolin kudi da na jigila da sauransu.

A ranar Alhamis shugaban hukumar kidayar, Nasir Isa Kwarra ya shaida wa wakilan kasashen waje a Abuja cewa ba duka na’urorin aikin da hukumar take bukata ne suka shiga hannunta ba.

Amma ya ce nan gaba kadan hukumar za ta karbi cikon na’urori 300,000 da suka rage daga cikin na’urori 800,000 da za a yi amfani da su.

Duk bayan duk shekara 10 ake gudanar da kidaya Najeriya, amma yanzu shekara 17 tun tun bayan wanda kasar ta gudanar a shekarar 2006.

AMINIYA

’Yan Bindiga Sun Sako 70 Daga Cikin Yara 85 Da Suka Sace A Zamfara

 


’Yan ta’adda da suka yi garkuwa da yara sama da 85 a Jihar Zamfara sun sako 70 daga cikin yaran, amma sun kashe biyu.

A ranar Juma’a ’yan ta’addan suka sako yaran, kimanin mako uku bayan sun sace su daga kauyen Wanzamai na Karamar Hukumar Tsafe ta jihar.

Wani mazaunin yankin Sani Aliyu ya ce, “Yara biyu da ’yan bindigar suka kashe sun yi kokarin tserewa ne, wadanda aka sako din kuma sun galabaita saboda tsananin yunwa, kuma yanzu ana duba lafiyarsu.”

Ya ce ganin irin galabaitan da yaran suka yi ya sa iyayensu koke-koke, kuma “An sako su ne bayan an biya kudin fansa Naira miliyan shida; da farko miliyan uku aka ba su, amma suka ki sako su, sai an kara musu da sabbin babura guda biyu.”

Wakilinmu ya yi kokarin jin ta bangaren Rundunar ’Yan Sandan Jihar Zamfara, amma hakarsa ta yin magana da kakakin rundunar, CSP Muhammad Shehu, ba ta cim ma ruwa ba.

Kimanin makonni uku da suka gabata ne ’yan bindiga suka  ritsa wasu yara da suka je neman icen girki da wasu manya a gonaki suka yi awon gaba da su a yankin Tsafe na Jihar Zamfara.

Daga cikin manyan da ’yan bindigar suka yi garkuwa da su har da mata.

AMINIYA

Ba Ma Yi Wa Shirin Mika Mulki Zagon Kasa - Ganduje

Gwamnatin jihar Kano  ta ce a shirye take domin miƙa mulki ga sabuwar gwamnati cikin ruwan sanyi ba tare da tayar da ƙura ba.

Cikin wata sanarwa da ta fitar mai ɗauke da sa hannun kwamishinan yaɗa labarai Muhammad Garba, gwamnatin ta ce tuni aka samar da babban kwamiti da kuma ƙanana da za su taimaka domin ganin an miƙa mulkin salin alin.

Ya musanta iƙirarin jam’iyyar NNPP da ta ke jiran karɓar mulki na cewa gwamnatin Ganduje na yi wa shirin miƙa mulki zagon ƙasa.

Kwamishinan ya ƙara da cewa kwamitin miƙa mulki na ɓangaren gwamnatin Ganduje na rubuta rahoton ƙarshe kafin miƙa mulki. Ya bayyana cewa kamata ya yi kwamitin karɓa na gwamnati mai jiran gado shi ma ya shirya domin karɓar rahoton, wanda ya yi alƙawarin miƙawa a kan lokaci.

Muhammad Garba ya ƙara da cewa manufar miƙa mulki shi ne gwamnati mai sauka ta miƙa duk wasu abubuwa na tafiyar da shugabanci cikin ruwan sanyi. Ba yunkurin yaɗa wani tunani ko wata aƙida ba.

Ya kuma ce kamata ya yi gwamnati mai jiran gado ta mayar da hankali game da shirin da take yi na karɓar mulki, ta kuma kiyaye duk wani abu da zai iya janyo fitina a yayin miƙawar.

Ƙorafin da NNPP ta yi a jiya shi ne gwamnatin ta ba ta gurbi uku kawai a cikin kwamitin da aka kafa don miƙa mulki hannun sabuwar gwamnati.

BBC 

Labari da dumiduminsa : Shugaba Buhari Ya Dage Kidayar 2023

A wata ganawa da ya yi da mambobin majalisar zartaswa ta tarayya da kuma shugaban hukumar kidaya ta kasa, shugaban kasa Muhammadu Buhari ya amince da dage kidayar yawan jama’a da gidaje na shekarar 2023, wadda aka shirya gudanarwa tun daga ranar 3-7 ga watan Mayun 2023. Za a tantance sabon ranar ne ta hanyar gwamnati mai shigowa.


An cimma matsayar ne bayan taron ya jaddada muhimmancin da ke akwai na kidayar jama’a, wanda ba a yi ta tsawon shekaru 17 ba, na tattara sabbin bayanai domin inganta rayuwar ‘yan Nijeriya, da kuma fitar da manufofin ci gaban kasar. Duk da irin gagarumin ci gaban da aka samu da suka hada da kammala aikin tantance yankin da kuma daukar ma'aikata da horar da ma'aikata, shugaban ya bayyana cewa kamata ya yi gwamnati mai jiran gado ta samu damar karfafa wadannan nasarori.

Shugaba Buhari ya yaba wa tsarin hukumar kidaya ta kasa, musamman yadda ake tura na’urorin zamani domin tabbatar da kidayar jama’a mai inganci kuma abin dogaro. An umurci hukumar da ta ci gaba da shirye-shiryen kidayar jama’a don dorewar nasarorin da aka samu.

Taron ya samu halartar manyan jami’an gwamnati da suka hada da babban lauyan gwamnatin tarayya kuma ministan shari’a, Abubakar Malami; ministar kudi, kasafi da tsare-tsare ta kasa, Mrs Zainab Ahmed; ministan yada labarai da al'adu, Alhaji Lai Mohammed; Karamin Ministan Kasafi da Tsare-Tsare na Kasa, Mista Clem Agba da Sakataren Gwamnatin Tarayya, Mista Boss Mustapha.


A wata sanarwa da ministan yada labarai da al’adu, Alhaji Lai Mohammed ya fitar a ranar 29 ga Afrilu, 2023, an sanar da jama’a shawarar dage kidayar.
NIGERIAN TRACKER 

Friday, 28 April 2023

PDP Ta Bukaci Sanyawa Buhari Takunkumi

Babbar jam’iyyar adawar Najeriya ta PDP ta bukaci kasashen duniya da su hana shugaban kasa Muhammadu Buhari bizar tafiye tafiye da zaran ya mika mulki ranar 29 ga watan gobe, saboda abinda ta kira kalamansa dangane da zaben shugaban kasar da akayi ranar 25 ga watan Fabarairu. 


Yayin tsokaci akan zaben, Buhari ya bayyana ‘yan adawar Najeriya a matsayin wadanda suka shantake akan cewar zasu samu nasara ba tare da neman goyan bayan jama’a kamar yadda jam’iyarsa ta APC tayi ba. 

Sakataren hulda da jama’a na jam’iyyar Debo Ologunagba yace kalaman shugaban na iya tinzira jama’a da kuma haifar da illa ga zaman lafiyar kasar. 

Ologunagba ya kuma ce kalaman na iya karfafawa alkalai gwuiwa wajen yanke hukunci akan karar da suka shigar a gaban kotu domin kalubalantar sakamakon zaben wanda yace tuni wasu a ciki da wajen kasar ke bayyana shi a matsayin mafi muni a tarihin Najeriya. 

Jam’iyyar PDP tace zaben da akayi bana ya gamu da matsalolin da suka sabawa kundin tsarin mulkin kasa da kuma dokar zabe ta shekarar 1999 da kuma 2022 musamman abinda ya shafi wallafa sakamako daga tashoshin zabe da kuma aikewa da su kai tsaye zuwa cibiyar hukumar ta kasa. 

Kakakin jam’iyyar ya jaddada cewar suna da yakinin cewar basu fadi zabe ba, kamar yadda shugaba Buhari ke fadi, kuma ba zasu bada kai bori ya hau ba duk da barazanar da gwamnatin APC ke musu. 

Jam’iyyar tace ganin yadda Buhari ya yiwa dimokiradiya illa a Najeriya, suna bukatar kasashen duniya da su kakaba masa takunkumi da kuma hana shi da iyalansa tafiye tafiye da zaran ya mika mulki ranar 29 ga wata. 

Ologunagba yace wannan bukatar tasu tayi dai dai da bukatar da shugaba Buhari ya gabatarwa kungiyar kasashen Turai a ranar 17 ga watan Fabarairun shekarar 2022 lokacin da ya ziyarci kungiyar EU a Brussels. 

RFI

Ci-da-zucin 'yan adawa ne ya kayar da su zaɓe - Buhari

Shugaba Muhammadu Buhari ya ce ya yi imani ci-da-zuci ne babban abin da ya janyo taron 'yan adawar Najeriya suka sha kaye a zaɓen shugaban ƙasa da ya wuce.

Ya bayyana haka lokacin da ya karɓi gwamnonin jam'iyyarsa ta APC a ƙarƙashin jagorancin Gwamna Abubakar Atiku Bagudu na jihar Kebbi.

Yana cewa a daidai lokacin da jam'iyya mai mulki take aiki tuƙuru don ci gaba da mulki a zaɓukan da aka yi a baya-bayan nan, 'yan adawa suna can sun cika da ci-da-zuci.

"Sun je suna ta faɗa wa masu goya musu baya a ƙasashen waje cewa, sai sun kayar da APC.

Yayin zaɓen na 25 ga watan Fabrairu, ɗan takarar jam'iyyar APC mai mulki Bola Ahmed Tinubu ya smau ƙuri'a 8,794,726.

Sai Atiku Abubakar, tsohon mataimakin shugaban ƙasar da ya samu ƙuri'a miliyan 6,984,520.

Ɗan takarar jam'iyyar Labour, Peter Obi yana da ƙuri'a miliyan 6,101,533, yayin da tsohon gwamnan Kano, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya zo na hudu da ƙuri'a miliyan 1,496,687.


Shugaba Buhari ya ce jam'iyyarsu ta yi nasara ne saboda ta haɗa ƙwarin gwiwar da take shi da taka-tsantsan kuma ta yi aiki tuƙuru har ya kai ta ga nasara.

Ya ce yanzu ma ga shi ci-da-zucin yana haifar wa 'yan adawan ƙarin matsaloli fiye da kowa.

"Abin na yi musu wahala su yi wa masu goyon bayansu na ƙasashen waje gamsasshen bayani a kan abin da ya sa suka gaza kayar da mu," in ji Buhari.

A cewarsa, sun haɗa ci-da-zuci da ji-ji-da-kai da bahagon lissafi, kuma su ne suka ja musu faɗuwa a zaɓukan bana. "Wannan ya sake haifar da ƙarin matsaloli a cikinsu. ta kai har ana tambaya. Me ya sa suka kasa kayar da mu?"

Shugaba Buhari ya ce babban dalilin da ya sa shi taya Asiwaju Bola Ahmed Tinubu murna kan nasarar da ya samu, shi ne 'yan adawa sun samu goyon baya, kuma masu goyo musu bayan daga ƙasashen waje sun lasa musu zuma a baki.

"Hakan ta sa sun tafi da burin cewa za su ci zaɓe, za su kayar da mu.

Wanne irin kuskure ne wannan?" shugaban ya sake tambaya.

'Kaduna zan koma bayan na huta a Daura'
Shugaba Buhari ya kuma yi bayani game da burinsa na rayuwa bayan sauka daga mulki, inda ya ce ya yi niyyar komawa gidansa na Daura, inda zai zauna tsawon wata shida kafin ya koma Kaduna.

Sanarwar Mallam Garba Shehu mai magana da yawun shugaban ƙasar, ta ambato Buhari yana yaba wa "Gwamna Nasir El-Rufa'i na Kaduna saboda ƙoƙarin da ya yi wajen samar da ababen more rayuwa da za su kyautata rayuwarsa da ta al'ummar jihar bayan ya kammala mulki".


Tun bayan sanar da sakamakon zaɓen 25 ga watan Fabrairu, masu sharhi kan al'amuran siyasa a Najeriya, suka yi ta tsokaci game da sakamakonsa.

Idan da 'yan adawan ƙasar sun haɗa ƙarfi wuri ɗaya, mai yiwuwa da cikin sauƙi, sun cinye zaɓen shugaban ƙasa.

Ana dai ɗora alhakin faɗuwar jam'iyyun adawar na Najeriya ne a kan matsalar rarrabuwar kai, da shiga zaɓe a lokacin da suke fama da ɓaraka.

'Yan takarar shugaban ƙasa a zaɓen watan Fabrairu guda biyu, Peter Obi da Rabi'u Musa Kwankwaso, duk sun ɓalle ne daga babbar jam'iyyar adawa ta PDP, wadda ta shiga zaɓen kuma tana fama da ɓaraka da rikicin cikin gida.

Idan an haɗa lissafin ƙuri'un da 'yan takarar biyu suka samu da na jagoran adawar Najeriya, Atiku Abubakar jimillar ƙuri'un za su kai 14,582,740.

Adadin dai ya kusa ninka abin da zaɓaɓɓen shugaban ƙasar Bola Ahmed Tinubu ya samu, har suka ba shi nasara
 BBC 

Kwamitin Karbar Mulki Na NNPP Na Kano Ya Zargi Gwamna Ganduje da gurgunta Tsarin Karbar mulki

Kwamitin Karbar Mulki na jam’iyyar NNPP reshen jihar Kano, ya zargi gwamnatin Gwamna Abdullahi Umar Ganduje mai barin gado da yin zagon kasa ga tsarin mika mulki ga gwamnatin Injiniya Abba Kabir Yusuf mai jiran gado.


A cewar shugaban kwamitin mika mulki na jam’iyyar NNPP, Farfesa Abdullahi Baffa Bichi, gwamnatin Ganduje ta nuna turjiya da rashin hadin kai tun bayan kafa kwamitin mika mulki na NNPP da zababben gwamna Abba Kabir Yusuf ya yi.

Jaridar Nigerian Tracker ta rawaito Bichi yana bayyana cewa kwamitin mika mulki na NNPP ya kafa kananan kwamitoci 33, amma babu daya daga cikin kwamitocin da ya samu hadin kai daga gwamnatin Ganduje. Duk da yunkurin kwamitin mika mulki na jam’iyyar NNPP na shirya taron hadin gwiwa da kwamitin mika mulki na gwamnati mai barin gado, gwamnatin Ganduje ta bukaci su zabi mutane uku ne kawai a taron wanda jam’iyyar NNPP ba ta amince da shi ba.

Bichi ya zargi Gwamna Ganduje da mayar da dukkan sakatarorin dindindin na jihar a wani bangare na kokarinsa na kawo cikas ga tsarin mika mulki a Kano.

Kwamitin rikon kwarya na NNPP ya yi kira ga dukkanin hukumomin  da su ba kwamitin mika mulki tare da mutunta zabin mutanen Kano da suka zabi Injiniya Abba Kabir Yusuf.

Kwamitin Karbar mulkin na NNPP zai gudanar da taron hadin gwiwa tare da dukkanin sakatarorin dindindin, shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnati, da daraktocin gudanarwa na dukkanin kananan hukumomi 44 daga ranar Talata 2 ga watan Mayu, domin tabbatar da samun saukin aikin. 

"Muna kira ga Gwamna Ganduje da ya mutunta zabin mutanen Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf kamar yadda Allah Madaukakin Sarki Ya ba da mulki ga wanda Ya so"

Kotu ta sake umartar Ganduje da ya amince da Muhuyi Magaji a matsayin Shugaban Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa

Kotun ma'aikata ta kasa da ke zamanta a Kano ta yi watsi da karar farko da gwamnatin jihar Kano ta shigar kan wata doka da ta hana gwamnatin jihar nada kowane mutum a matsayin shugaban hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta jihar.

Idan dai za a iya tunawa, a kwanakin baya ne Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya mika sunan mukaddashin shugaban hukumar Mahmud Balarabe ga majalisar dokokin jihar domin tabbatar da shi a matsayin kwararren shugaba.

Majalisar ta tsara tantance shugaban riko a ranar 2 ga Mayu, 2023.

SOLACEBASE ya bayar da rahoton a wani hukuncin da kotu ta yanke a baya a cikin wani umarni na musamman cewa dakataccen shugaban hukumar korafe-korafen al’umma da yaki da cin hanci da rashawa ta jihar Kano, Muhuyi Magaji Rimigado ya ci gaba da kasancewa a matsayin shugaban hukumar.

Biyan kuɗi zuwa wasiƙarmu
Shigar da adireshin imel ɗin ku
Yi rijista
Karanta kuma:Kwarai Muhuyi a matsayin Shugaban Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Kano- Kotu ta umarci Ganduje

A zaman kotun a ranar Juma’a, Mai shari’a E.D. Isele ta yi watsi da karar farko da gwamnatin jihar Kano ta shigar kan lamarin yayin da ta amince da bukatar Muhuyi Magaji Rimingado ta amince da shi a matsayin shugaban hukumar.


Kotun ta kuma gargadi Lauyan Gwamnatin Jihar Kano da ya gargadi wanda yake karewa da ya daina duk wani tsari na tabbatar da wani mutum a matsayin Shugaban Hukumar Korafe-korafen Jama’a da Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Jihar Kano.

HAJJIN 2023: Rikicin Sudan Ka Iya Kawo Matsala Ga Jigilar Ahazan Najeriya - Kungiyar Fararen Hula

Rikicin da ake fama da shi a kasar Sudan na iya kawo cikas ga jigilar maniyyatan Najeriya zuwa kasar Saudiyya cikin sauki, domin gudanar da aikin hajjin shekarar 2023, in ji kungiyar daukar rahotannin aikin hajji mai zaman kanta.
 
Kungiyar farar hula a cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Juma'a mai dauke da sa hannun shugabanta na kasa Ibrahim Muhammad, ta ce tuni yakin ya kai ga rufe sararin samaniyar Sudan ba zato ba tsammani.
 
Kungiyar ta ce Najeriya "dole ne ta hanyar NAHCON ta yi gaggawar sake duba kalubalen da ke gabanta sannan ta fito da wasu zabin da za a yi a matsayin ma'auni."
 
Kamar yadda jadawalin NAHCON ya nuna, za a fara jigilar maniyyatan Najeriya zuwa kasa mai tsarki a ranar 21 ga Mayu, 2023.
 
Jiragen saman jigilar alhazan Najeriya na tafiya ta sararin samaniyar Sudan a lokacin da suke tafiya Saudiyya, kuma ana daukar matsakaicin sa'o'i hudu zuwa biyar kafin su isa kasar.
 
Sai dai kuma rufe sararin samaniyar kasar Sudan ba zai tilastawa masu jigilar jigilar Alhazan jiragen sama na zirga-zirga ta wasu hanyoyi daban-daban da za su dauki sama da sa'o'i bakwai daga Najeriya ba, ta yadda za a kara wa'adin aikin jigilar jiragen.
 
Kungiyar ta ce wani ma’aikacin canjin hanyoyin mota baya ga lokacin, shi ne farashin tikiti wanda wani karin nauyi ne kan mahajjata.
 
Sanarwar ta ce, "Muna cikin fargabar cewa za a iya tilasta wa maniyyatan mu su tashi ta kasashen Kamaru, Afirka ta Tsakiya, Eritrea, Habasha, Kenya, Uganda, ko DRC don isa Saudiyya."
 
Kungiyar  ta damu da cewa tuni rufe sararin samaniyar Sudan ya tilastawa wasu manyan kamfanonin jiragen sama irin su Qatar Airways, Turkish Airlines, Etihad Airways, Emirates da Saudi Airlines fara jigilar jiragensu zuwa wasu kasashen Afirka da Kudancin Amurka.
 
Ta ce, kamfanin jiragen saman kasar Habasha wanda ke kan gaba wajen gudanar da aikin Hajji a Najeriya, tuni ya sake karkata hanyoyin sadarwa har guda 38.
 
“Muna kira ga Gwamnatin Tarayya, da ta gaggauta duba lamarin, ta samar da hanyar da ta dace ga masu jigilar alhazai kafin a fara jigilar maniyyatan Najeriya. Yin dinki a cikin lokaci yana ceton tara," in ji sanarwar.

Firaministan Pakistan ya tsallake rijiya da baya

 


Firaministan Pakistan Shehbaz Sharif ya tsallake rijiya da baya, bayan da ‘yan majalisar kasar suka kada kuri’ar yanke kauna, yayin da sauran kungiyoyin fararen hula suka matsa kan a fara shirin gudanar da babban zaben kasar. 

Sharif ya sami kuri’un amincewa guda 180, yayin da ‘yan majalisa 172 suka nuna rashin amincewa da salon shugabancin sa, abinda ya bashi damar ci gaba da rike mukamin sa da kyar. 

Ko da yake jawabi, kakakin majalisar dokokin kasar Raja Pervais Asharf, yace a yanzu abinda majalisar zata mayar da hankakli shine batun babban zaben da ke tafe. 

Sharif wanda ya gaji Imran Khan ya yabawa mambobin jam’iyyyar sa da ke majalisar bayan da suka amince da salón mulkin sa, tare da yanke hukuncin sake bashi dama, ta hanyar kada kuri’ar amincewa da shi. 

rfi

An tilasta wa 'ya'yanmu ba da fasfo kafin a kai su Masar - Iyayen ɗaliban Sudan

 


Hausawa kan ce tsuguno ba ta ƙare ba a kan lamarin ɗaliban Najeriya da ke karatu a Sudan, waɗanda gwamnatin Najeriyar ta ce za ta kwaso su zuwa gida.

Yayin da ake kukan cewa har yanzu akwai tarin ɗalibai da aka bari a ƙasa - a gefe ɗaya kuma iyayensu na kukan lokaci na ƙurewa, ko da yake an tsawaita yarjejeniyar tsagaita wuta da ƙarin sa'a 72.

Iyayen ɗalibai da dama da BBC ta tattauna da su, sun ce yanzu haka halin da yaransu ke ciki ya fi wanda suka baro a Khartoum.

Asma'u Yarima Muhammad, sakatariyar ƙungiyar iyayen ɗaliban Najeriya da ke karatu a Sudan, ta ce 'ya'yanta biyu "na cikin tsakiyar sahara ba tare da sanin inda suka dosa ba".

Asma'u Yarima na da yara biyu 'yan shekara 18, wato 'yan tagwaye ne duka maza.

Daya na karantar fannin zane, sai kuma ɗayan da ke nazarin aikin likita.

Ta ce yawancin dare sukan yi waya da yaranta irin ta iyaye da 'ya'ya wadda rabinta nishaɗi ne, ɗaya rabin maganar karatu.

Amma tun daga 15 ga watan Afrilun da muke ciki rayuwa ta sauya.

Ta ce "ƙasa da awa biyu da muke magana da kai na yi magana da su, kuma suna shaida min cewa motoci 7 cikin 13 da suka taso daga Khartoum sun tsaya a sahara, suna neman a ba su (cikon) kuɗin aikinsu.

"Ganin cewa yaran ba su da kuɗin da za su ba su, sai suka ce to su bayar da fasfo ɗinsu, kafin su ƙarasa da su Aswan da ke cikin ƙasar Masar, kamar yadda suka cimma yarjejeniya da gwamnatin Najeriya", in ji Hajiya Asamau.

Wata mahaifiya da BBC ta tattauna da ita ko da yake ta nemi a sakaya sunanta, ta ce sai da yarinyarta ta shiga mota a cikin motocin da aka kawo, amma daga baya aka fitar da ita.

"Kimanin sa'a biyu suka kwashe a cikin motar, duk murna ta ishe mu, ni da yan uwanta muna ganin ta tsira, amma daga baya aka fitar da ita.

Ta yi zargin cewa mutanen gari ne suka riƙa biyan kuɗi ana maye gurbinsu da ɗaliban da aka aika motacin su kwaso.

Yarjejeniya da ke tsakin gwamnati da masu kwaso ɗalibai

Asma'u Yarima Muhammad ta ce yarjejeniyar da aka cimma tsakanin gwamnatin Najeriya da kamfanin jigilar motocin da zai kwashi ɗaliban Najeriya shi ne za a biya su dalar Amurka miliyan1.2.

"Gwamnati ta bai wa kamfanin dalar 400,000, saura dubu 800,000. A kan wannan sauran kuɗin ne suka tsayar da yaranmu a tsakiyar sahara, suka ce sai an cika musu kuɗinsu.

"Kuma kuɗin nan garinsu aka yi magana za a biya ba wai a aika musu ta asusunsu na banki ba,'' in ji ta.

Sai dai Hukumar ba da agajin gaggawa ta Najeriya ta ce daga safiyar yau Juma'a ne za a fara kwaso ɗaliban.

Kuma jirgin saman Air Peace da zai yi aikin kwashe ɗaliban da sauran 'yan Najeriya, zai tashi da ƙarfe 6 na yamma zuwa Aswan, cewar shugaban hukumar ba da agajin gaggawar.

Mustapha Habib Ahmed ya ce tuni motoci guda biyu ɗauke da ɗaliban da aka kwaso daga Khartoum suka isa bakin iyakar Masar.

Ya amsa cewa ba shakka sun samu matsala da wasu direbobi da suka zubar da ɗalibai a cikin Sahara kusa da Dongola, wani wuri mai nisan kilomita 411 daga Khartoum.

Mustapha Habib ya ce suna aikin shirya takardu tare da ofishin jakadancin Najeriya a Masar don ganin jirgin Air Peace ya samu damar jigilar 'yan Najeriyan daga birnin Aswan.

Ya ce tuni suka daidaita da kamfanin sufurin da ya zubar da ɗalibai a Sahara, har ma sun shiga motocinsu guda bakwai sun ci gaba da tafiya.

BBC

Thursday, 27 April 2023

Muhuyi Magaji Ya Karbi Naira Miliyan Biyar Da Dubu Dari Biyar Bayan Da Kotu Ta Tursasa Gwamna Ganduje

Tsohon shugaban hukumar korafe-korafe da yaki da cin hanci da rashawa ta jihar Kano, Muhuyi Rimingado, ya karbi kudi naira miliyan 5,713,891.22 daga asusun albashi na gwamnatin jihar Kano.

Mista Rimingado ya tabbatar da karbar kudin ne a ranar Alhamis, inda ya ce zai yi amfani da wani bangare na su ne don bayar da agaji.

A ranar Talata, kotun ma'aikata ta kasa, Abuja ta umarci GTBank da ya biya Mista Rimingado bashin albashin ma’aikata daga asusun gwamnatin jihar, biyo bayan dakatarwar da Gwamna Abdullahi Ganduje ya yi ba bisa ka’ida ba a watan Yulin 2021.

Jaridar DAILY NIGERIAN ta ruwaito cewa gwamnan ya dakatar da Mista Rimingado ne bayan ya bude bincike kan wasu kwangiloli da ake zargin an baiwa wasu kamfanoni masu alaka da iyalan gwamnan.

A zaman da aka ci gaba da yi a ranar Talatar da ta gabata, bankin ta bakin lauyansa Joshua Shekwolo ya shaida wa kotun a cikin wata takardar rantsuwa cewa gwamnatin jihar Kano ta na da asusun ajiyar banki da jimillar kudaden da suka kai N5,713,891.22 kasancewar an toshe hukuncin da aka yanke kan lamarin. a cikin asusun. 

Shugaban NAHCON Ya Kaddamar Da Tawagar Ma'aikatan Lafiya Na Hajin 2023

Hukumar alhazai ta kasa NAHCON, ta gudanar da aikin tantance tawagar likitocin da zasu kula da alhazai a aikin hajjin na shekarar 2023. 

A sanarwar da Mataimakiyar Daraktar harkokin hulda da jama’a ta hukumar Hajiya Fatima Sanda Usara ta fitar, tace an  gudanar da taron ne a yau, 27 ga Afrilu, 2023 tare da kusan masu neman 212 da aka gayyata don tantancewa.

Manyan jami’ai karkashin jagorancin Dakta Usman Galadima na Ma’aikatar Lafiya ta Tarayya, wanda kuma shi ne Shugaban Ma’aikatan Lafiya na Hukumar Kula da Lafiya ta Kasa (NMT), sun tantance takardun kwararrun likitoci, masu harhada magunguna da ma’aikatan jinya da za su kafa tawagar NMT.


Da yake gabatar da jawabinsa a lokacin kaddamar da yan tawagar da wayar da kan jama’a, Alhaji Zikrullah Kunle Hassan, Shugaban Hukumar NAHCON ya taya ‘yan tawagar guda 230 murna wanda aka zabo su daga cikin  mutane sama da 10,000 da suka nema 

Ya umarce su da su dauki zabarsu a matsayin amana daga Ubangiji Madaukakin Sarki, wanda suke amfana da falalarsa. Shugaban ya kuma gargadi ‘yan tawagar da su mutunta ka’idoji da ka’idojin kasar Saudiyya da ba su yarda da keta haddi ba.


Prince Sheikh Suleman Momoh, Kwamishinan Tsare-tsare, Bincike, Watsa Labarai, Kididdiga da Ayyukan Laburare (PRISLS) wanda ya zama shugaban kungiyar likitocin, ya bayyana cewa zaben mambobin ya biyo bayan tsarin zabe na gaskiya karkashin kulawar mambobi 12. Don haka ya jaddada cewa duk wani memba da ba zai bi ka’ida ba, an gayyace shi da ya yi watsi da tayin. Sheikh Momoh ya sanar da cewa da zarar sun sanya hannu kan takardar karbar aiki, za a sa ran za su yi aiki kamar yadda aka tsara. Sheikh Momoh ya bayyana cewa NAHCON ta dauki nauyin kula da lafiya ga alhazai a ayyukanta.


Da suke tsokaci, Kwamishinonin biyu Alhaji Abdullahi Magaji Hardawa da Alhaji Nura Hassan Yakassai sun yi kira ga ‘yan tawagar da su nuna godiya ga Allah da ya zabe su ta hanyar sauke nauyin da aka dora musu ko an sa ido ko ba a sanya su ba. Alhaji Yakassai ya kara da cewa wasikar nadin nasu ta bayyana karara a kan kudaden da za a biya su bisa adadin kwanakin da za a dau aiki.

 
Sabon Dan Majalisar da aka nada mai wakiltar Ma’aikatar Lafiya ta Tarayya, Dokta Ahmad Baba ya yi kira ga ma’aikatan lafiya da su rika bin ka’idojin aikinsu a duk inda suke. Mai ba da shawara kan fasaha ga NMT ya kuma tunatar da zababbun mambobin hukumar aikin ma’aikatar lafiya ta tarayya a matsayin hukumar da ke sa ido kan yadda suke gudanar da ayyukansu.

Kundin tsarin na NMT hadaka ne na ma’aikatan lafiya da Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihohi ke daukar nauyinsu da kuma hukumomin tarayya da ke daukar nauyin kula da lafiyar alhazai a lokacin ayyukan Hajji a ciki da wajen teku.



Labari Da Dumiduminsa : Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Shirinta Na Janye Tallafin Man Fetur

Gwamnatin tarayya ta dakatar da shirin cire tallafin man fetur a karshen gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari.

Wannan na daga cikin shawarar da majalisar tattalin arzikin kasa ta yanke a zamanta na ranar Alhamis.

Ministar Kudi, Kasafin Kudi da Tsare-Tsare na Kasa, Misis Zainab Ahmed ce ta bayyana hakan a lokacin da take zantawa da manema labarai a fadar shugaban kasa a karshen taron hukumar zaben da mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo ya jagoranta a fadar shugaban kasa da ke Abuja.



Zainab ta bayyana cewa akwai yiyuwar cire tallafin zai fara aiki a watan Yuni saboda dokar masana'antar man fetur, PIA da kuma kasafin kudin 2023 sun ba da tallafi har zuwa watan Yuni, don haka duk wani jinkiri na iya buƙatar gyara PIA da tanadin kasafin kuɗi.

Ministan, ya ce babu wani wa'adi da aka bayar na cire tallafin, kuma gwamnati mai zuwa za ta yanke shawara a kan lokacin da za ta iya yin hakan.

Cikakken labarin zai zo muku nan gaba kadan

Saudiyya Ta Kwashe ’Yan Najeriya Da Suka Makale A Sudan Zuwa Kasarta


Gwamnatin kasar Saudiyya ta kwashe wasu daga cikin ’yan Najeriya da suka makale a yakin da ya barke a Sudan zuwa kasarta.

Minista a Ma’aikatar Harkokin Waje ta Najeriya, Zubairu Dada, ya ce Saudiyya ta tura jiragen ruwa da suka kwashe ’yan Najeriya zuwa birnin Jeddah na kasarta, bayan barkewar yaki a Sudan.

Ma’aikatar ta ce daga bisani za a maido da ’yan Najeriyan da aka kai Saudiyya gida, kuma gwamnatin Tarayya na kokarin ganin cewa babu dan Najeriya ko daya da ya rage a Sudan kafin cikar wa’adin awa 72 da bangarorin da ke yaki da juna suka bayar na tsagaita wuta.

Ta bayyana cewa a kokarinta na kwashe ’yan Najeriya da suka makale bayan barkewar yakin, Gwamnatin Tarayya ta kashe Naira miliya 552 kan daukar hayar motocin da za su fitar da su zuwa iyakar Sudan da kasar Masar.

Ministan Harkokin Waje na Najeriya, Geoffrey Onyema, ya ce an dauki hayar bas-bas 40 da za su kwashi ’yan Najeriya daga Khartoum, babban birnin Sudan zuwa iyakar kasar Masar da ke Aswan, inda za su hau jirgi zuwa gida.

“Dala miliyan 1.2 (Naira miliyan 552) aka caje mu kan bas 40 da muka nema; Mun samu bas guda 40 na alfarma da za su dauki ’yan Najeriya (daga Khartoum) zuwa iyakar kasar Masar.

“Sanin kowa ne cewa tabbas irin wannan yanayi akwai wadanda za su yi amfnai da rikicin Sudan wajen tatsar jama’a,” in ji Oyema.

Ya bayyana cewa Gwamnatin Tarayya na yin dukkan mai yiwuwa wajen ganin an gama kwashe ’yan Najeriya cikin sa’a 72 da gwamnatin Sudan ta bayar na tsagaita wuta.

“Ba mu da matsala da wa’adain awa 72 da gwamnatin ta bayar kuma mun tattauna da bangarorin da abin ya shafa, kuma sun ba mu hadin kai,” in ji shi.

Ya ci gaba da cewa “Za a kwashe ’yan Najeriya ne a rukuni-rukuni domin tabbatar da tsaron lafiyarsu; kuma Alhamdulillah babu dan Najeriya ko daya da ya rasa ransa.

AMINIYA

Buhari Ya Je Wurin Fareti Sanye Da Kakin Soja


Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya fito sanye da kakin sojoji a dandalin Eagles Square inda sojoji ke fareti a safiyar Alhamis. 

Buhari ya isa dandalin, inda sojoji 1,000 ke gabatar da fareti inda ya samu rakiyar Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Kasa, Ibrahim Gambari.

Babban Hafsan Taron Najeriya, Janar Lukcy Irabor da Babban Hafsan Sojin Kasa, Laftanar-Janar Faruk Yahaya da kuma Shugaban ’Yan Sandan Najeriya, Usman Baba na daga cikin mahalarta faretin.

Sauran hafsoshin tsaro da Shugaban Majalisar Dattawa, Ahmad Lawan na daga cikin mahalarta faretin sojojin.

AMINIYA

Wednesday, 26 April 2023

Labari Da Dumiduminsa : Hukumar NAHCON Ta Bayar Da Awa 48 Ga Hukumomin Alhazai Na Jihohi Dasu Sanya Kudaden Alhazansu

Shugaban Hukumar Alhazai ta Najeriya, NAHCON, Alhaji Zikrullah Kunle Hassan ya ba da ranar Juma’a 28 ga watan Afrilu a matsayin wa’adin tura kudin aikin Hajjin shekarar 2023 daga hukumomin kula da jin dadin Alhazai na Jihohi. 

A sanarwar da Mataimakiyar Daraktar harkokin hulda da jama’a ta hukumar, Hajiya Fatima Sanda Usara ta sanyawa hannu, shugaban Ya bayyana hakan ne a yau 26 ga watan Afrilu 2023 a yayin wani gagarumin taro da shugabannin hukumomin jin dadin alhazai na Jihohi a hedikwatar Hukumar ta NAHCON. 

Taron dai an yi shi ne domin tattauna muhimman batutuwan da suka shafi kudaden da maniyyata ke aikawa da maniyyata aikin Hajji domin kammala yawan wadanda suka cancanci zuwa aikin hajjin 2023 daga Najeriya. 

A cewar Alhaji Zikrullah Kunle Hassan, hukumar za ta yi farin cikin yin aiki da duk wani kudi da za ta aika kafin ranar Juma’a, sannan ta rattaba hannu kan yarjejeniyoyin jigilar jirage zuwa Saudiyya a shekarar 2023 bisa ga wannan adadin. 

Ya bayyana cewa ana sa ran kashi 50% na biyan kamfanonin jiragen sama bayan sanya hannu kan yarjejeniyar yayin da wani kashi 35% zai biyo baya bayan tura jiragen da masu jigilar kaya suka yi.

Babban jami’in hukumar ta NAHCON ya koka da cewa dole ne a yi la’akari da cewa duk wasu tsare-tsare sun dogara da adadin masu biyan kudin Hajji da aka tabbatar kafin a kammala.

Idan dai ba a manta ba an tsawaita wa’adin aika kudin Hajji a lokuta da dama tun daga watan Janairun 2023.

A wani labarin kuma, Kwamishinan Tsare-tsare, Bincike, Kididdiga na hukumar, Sheikh Suleman Momoh ya bayyana cewa za a gudanar da aikin tantance rukunin farko na ma’aikatan lafiya na aikin Hajjin 2023 a gobe Alhamis 27 ga watan Mayu da wayar da kan jama'a da sauran bukukuwa za su biyo baya bayan tabbatar da wadanda suka samu aikin 


Yanzu-yanzu: Tsohon Minista, Musa Gwabade ya rasu

Tsohon ministan kwadago da wadata, kuma jigo a jam’iyyar PDP, Alhaji Musa Gwadabe ya rasu.

Gwadabe ya rasu ne a Kano yana da shekaru 86 a daren ranar Talata, bayan doguwar jinya, kamar yadda jaridar SOLACEBASE ta ruwaito.

Dan uwan ​​marigayi dattijon jihar, Nasiru Gwadabe ya shaida wa SOLACEBASE cewa za a yi sallar jana'izar marigayin da misalin karfe 2:00 na rana a yau Laraba a gidansa da ke kan titin Maiduguri a Kano.


Biyan kuɗi zuwa wasiƙarmu
Shigar da adireshin imel ɗin ku
Yi rijista
Karanta Hakanan: PSC ta amince da tura sabbin CPs zuwa jihohin Kano, Katsina 9 sauran jihohi, FCT

Alhaji Musa Gwadabe wanda ya rike mukamin minista a lokacin Olusegun Obasanjo na farko daga shekarar 1999 zuwa 2003 ya kuma kasance sakataren gwamnatin jihar Kano a zamanin marigayi Sabo Bakin Zuwo kuma ya kasance mamba a kwamitin gudanarwa da dama.

Har zuwa rasuwarsa dan jam'iyyar All Progressives Congress, APC ne kuma shugaban hukumar kula da harkokin horar da masana'antu, ITF.


Ya rasu ya bar ‘ya’ya 12 , jikoki da kuma ‘yan uwa.

Tuesday, 25 April 2023

Kotu ta umarci Bankin Guarantee Ya Biya N5.7m Da Muhuyi Rimingado Daga Asusun Gwamnatin Kano

Kotun ma'aikata ta kasa da ke Abuja ta umarci Bankin (GT) da ya biya korarren shugaban hukumar KORAFE-KORAFE jama’a da yaki da cin hanci da rashawa ta jihar Kano, Muhuyi Rimingado, kudi N5,713,891.22 daga asusun albashi na gwamnatin jihar.

Adadin kudaden da  Rimingado ke bin gwamnatin ne na albashin ma’aikata, bayan dakatar da shi a watan Yulin 2021.

DAILY NIGERIAN ta ruwaito cewa gwamnatin jihar ta dakatar da Mista Rimingado ne bayan bude bincike kan wasu kwangiloli da ake zargin an baiwa wasu kamfanoni masu alaka da iyalan gwamnan.


A zaman da aka ci gaba da yi a ranar Talatar da ta gabata, Bankin ta bakin lauyansa Joshua Shekwolo ya shaida wa kotun a cikin wata takardar neman sahalewa cewa gwamnatin jihar Kano ta na da asusun ajiyar banki da jimillar kudaden da suka kai N5,713,891.22 kasancewar an toshe hukuncin da aka yanke kan lamarin. a cikin asusun.



Da yake bayar da cikakkiyar umarnin, mai shari’a O.O Oyewumi ya umarci GTBank ya biya kudin a asusun Mista Rimingado cikin sa’o’i 48.

An bayar da umarnin ne bayan gazawar gwamnatin jihar wajen mutunta hukuncin da kotun ta yanke a ranar 14 ga Disamba, 2022, inda ta bayar da umarnin biyan da kuma amincewa da Mista Rimingado a matsayin halastacen shugaban hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta jahar Kano 

Shugaba Biden ya bayyana aniyar sake tsayawa takara

 


Shugaban Amurka Joe Biden ya sanar da cewa zai sake tsayawa takara a zaɓen shekara ta 2024, inda mai yiwuwa ya sake takara da Donald Trump.

An yi tsammanin jam'iyyar Democrat za ta sake neman wa'adin mulki na biyu tsawon shekara huɗu tare da ƙaddamar da yaƙin neman zaɓensa a wani bidiyo ranar Talata.

Ya ce wannan muhimmin lokaci ne da zai sake bayyana aniyrasa ta sake neman mulkin Amurka.

Mataimakiyar shugaban ƙasar Kamala Harris, mai shekaru 58, ita ma ta nuna aniyar sake zama abokin takararsa.

Mista Biden, mai shekaru 80, shi ne shugaban ƙasa mafi tsufa a tarihin Amurka, kuma da alama zai fuskanci tambayoyi kan shekarunsa a tsawon lokacin yakin neman zaɓe.

Zai kasance mai shekara 86 bayan kammala wa'adinsa na biyu a mulkii cikin shekara ta 2029.

BBC

’Yan Matan Chibok’ 2 Sun Gudo Daga Hannun Boko Haram


 Karin mutum biyu daga cikin daliban Makarantar Sakandaren ’Yan Mata da ke Chibok a Jihar Borno sun gudo daga hannun mayakan Boko Haram da suka sace su shekaru tara da suka gabata.

Majiyoyin tsaro da mazauna Jihar Borno sun shaida wa wakilinmu cewa matan su biyu sun samu tserewa a dalilin tsananta luguden wuta da sojoji suke yi a kan sansanonin kungiyar da ke Dajin Sambisa

Wata majiyar tsaro ta ce daliban da suka gudo su ne Hauwa Mutah da kuma Esther Markus.

Ta bayyana cewa, “Daya daga cikinsu ’yar kauyen Chibok ce, dayar kuma ’yar kauyen Dzilang ce.”

Mako biyu da suka gabata, rundubar soji ta Operation Hadinkai da ke yaki da kungiyar, ta bayyana cewa akwai saura mutum 98 daga cikin Daliban Chibok a hannun kungiyar.

Kwamandan Sashen Lelen Asiri na rundunar, Kanar Obinna Ezuipke ya ce, “Daga cikin Daliban Chibok 276 da aka sace, 57 sun tsere a 2014, an sako 107 a 2018.

Monday, 24 April 2023

‘Yan sanda sun fara farautar shugaban INEC na Adamawa


Babban Sufeton 'yan sandan Najeriya Usman Alkali Baba ya umurci wata tawagar 'yan sanda ta yi aiki tare da hukumar zaben Najeriya INEC wajen bincike da kuma gurfanar da shugaban hukumar zabe na jihar Adamawa da aka dakatar Hudu Yunusa Ari.

A wata sanarwar da rundunar ta fitar wacce kakakinta Olumuyiwa Adejobi ya sanya wa hannu, babban sufeton ya ce 'yan sanda za su tabbatar sun yi dukkan mai yiwuwa domin gano dalilin da ya sa Hudu aikata abun da ya yi.

Ana tsaka da tattara sakamakon zaɓen gwamna na jihar Adamawa da aka ƙarasa ne sai kwatsam Hudu wanda shi ne kwamishinan zaɓe na jihar, ya ayyana Sanata Aishatu Binani ta APC a matsayin wadda ta lashe zaɓen.

IGP Usman ya ce a shirye su ke su tabbatar an yi hukunci da ya dace kan dukkan wadanda aka samu da hannu a lamarin da ya faru a Adamawa domin martaba dokokin dimokradiya.

Sanarwar ta tabbatar wa 'yan Najeriya da kuma kasashen duniya cewa 'yan sanda za su binciki ayyana Aishatu Binani ta APC da Hudun ya yi tare sauran masu hannu a lamarin domin gurfanar da su a gaban kotu.

Tuni dai Shugaba Muhammadu Buhari ya amince da matakin hukumar zaɓen ƙasar na dakatar da kwamishinan na INEC a Adamawa ya zuwa lokacin da za a kammala bincike.

Buhari ya umarci gudanar da bincike da gurfanar da Hudu Ari gaban shari'a, matuƙar an same shi da laifi.

A baya dai hukumar zaben Najeriya ta INEC ta ce ba ta san inda Hudu Ari ya shiga ba tun lokacin da ta dakatar da shi.

BBC

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

SAPZ Kano partners ABCOAD to organize FFS Training for Youth and Women.

The Special Agro-Industrial Processing Zones (SAPZ) Programme, Kano State, in collaboration with Audu Bako College of Agricultur...