Search This Blog

Showing posts with label Albashi. Show all posts
Showing posts with label Albashi. Show all posts

Thursday, 27 February 2025

Gwamna Abba Kabir Yusuf Ya Bayar Da Umarnin Yin Bincike Kan Yankar Albashin Ma'aikata


… Ya Kaddamar da Kwamitin Bincike da Zai Gabatar da Rahoto Cikin Kwana Bakwai

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya bayyana takaicinsa kan rahotannin da suka nuna ana rage albashin wasu ma’aikatan gwamnati ko kuma hana su albashinsu gaba ɗaya, yana mai cewa hakan babban cin zarafi ne ga haƙƙin ma’aikata kuma cin amanar jama’a.

Wannan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar a ranar Alhamis.

Gwamna Yusuf, wanda ya nuna matuƙar ɓacin ransa kan labarin cewa wasu ma’aikata sun kwashe watanni ba tare da an biya su haƙƙinsu ba, ya yi alkawarin binciko masu hannu a wannan aika-aika tare da ɗaukar matakin da ya dace a kansu.

“Wannan gwamnati ba za ta lamunci zalunci ga ma’aikata ba. Duk wanda aka samu da hannu a wannan aika-aika, doka za ta yi aiki a kansa ba tare da rangwame ba,” in ji gwamnan.

A wani mataki na kawo ƙarshen wannan matsala, gwamnan ya kaddamar da wani kwamitin bincike mai ƙarfi don gano musabbabin matsalar, ko dai matsalar fasaha ce ko kuma ganganci da gangan da wasu suka aikata.

Kwamitin zai gudanar da bincike na musamman kan albashin ma’aikatan gwamnati daga Oktoba 2024 zuwa Fabrairu 2025, domin gano waɗanda abin ya shafa, tantance irin asarar da aka yi, tare da ba da shawarwari kan yadda za a magance matsalar da kuma hukunta masu hannu a ciki.

Kwamitin mai mambobi bakwai, wanda Hon. Abdulkadir Abdussalam, Kwamishinan Harkokin Karkara da Ci gaban Al’umma, kuma tsohon Akanta-Janar na Jihar Kano ke jagoranta, ya ƙunshi ƙwararru a fannin kuɗi da tsarin biyan albashi.

Ga cikakken jerin mambobin kwamitin:l

1. Hon. Abdulkadir Abdussalam – Shugaban Kwamitin
Kwamishinan Harkokin Karkara da Ci gaban Al’umma

2. Dr. Bashir Abdu Muzakkari – Memba
Mai Bai wa Gwamna Shawara Kan Tattalin Arzikin Zamani (Digital Economy)

3. Dr. Aliyu Isa Aliyu – Memba
Daraktan Hukumar Kididdiga ta Jihar Kano

4. Dr. Hamisu Sadi Ali – Memba
Daraktan Hukumar Sarrafa Basussuka ta Jihar Kano

5. Hajiya Zainab Abdulkadir – Memba
Daraktar Cibiyar Kwamfuta ta Jihar Kano

6. Aliyu Muhammad Sani – Sakataren Kwamitin
Daraktan Bincike da Tantancewa, Ofishin Sakataren Gwamnati

7. Ummulkulthum Ladan Kailani – Mataimakiyar Sakataren Kwamitin
Babbar Mataimakiyar Sakataren Gudanarwa, Ofishin Sakataren Gwamnati

An ba wa kwamitin wa’adin kwana bakwai kacal domin ya kammala bincikensa tare da gabatar da cikakken rahoto kan masu hannu a lamarin, girman barnar da aka yi, da kuma hanyoyin magance matsalar gaba ɗaya.

Gwamna Yusuf ya jaddada cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da aiki don tabbatar da Adalci, gaskiya, da biyan albashi cikin lokaci, yana mai cewa duk wanda aka samu da laifi ba zai tsira ba.

“Zamanin cin zarafin ma’aikata ya ƙare. Wannan gwamnati ce ta gaskiya da riƙon amana, kuma duk wani da aka samu da hannu a wannan aika-aika ba zai tsira ba,” in ji gwamnan.

Kwamitin binciken na fatan gano duk wata badakala da aka tafka a tsarin biyan albashi, tare da dawo da martabar tsarin albashi a Kano domin kare haƙƙin ma’aikata.

Sakataren Gwamnatin Jihar Kano, Alhaji Umar Faruk Ibrahim, ne ya kaddamar da kwamitin a madadin mai girma Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf.


Wednesday, 15 May 2024

Kungiyar Kwadayo Ta Yi Watsi Da Naira 48, 000 A Matsayin Mafi Karancin Albashi

Ƙungiyar Ƙwadago NLC ta yi fatali da tayin naira 48,000 da Gwamnatin Tarayya ta gabatar a matsayin mafi ƙarancin albashin ma’aikata a ƙasar.


Mambobin ƙungiyar ta NLC a wannan Larabar su bayyana mamakin dalilin da gwamnati da mambobin kamfanoni masu zaman kansu ke tozarta su da abin da ta bayyana a matsayin tayi mai ban dariya.


Aminiya ta ruwaito cewa a yayin da Gwamnatin Tarayya ta miƙa tayin Naira 48,000, ‘yan ƙungiyoyi masu zaman kansu sun miƙa tayin N54,000.


Sai dai ƙungiyar NLCn ta bayyana adawartwa kan duk tayin da ɓangarorin biyu suka gabatar a wani taron tattaunawa da aka gudanar a babban Ofishin NLC na Labour House da ke Abuja.


Shugabannin ƙwadagon sun ce gwamnati ba ta gabatar da wasu bayanai da za su goyi bayan tayin da ta gabatar ba.


Monday, 22 April 2024

Gwamnatin Kano Ta Yi Alkawarin Mayar Da Karin Albashin Shekara-Shekara Ga Ma'aikata

Gwamnatin jihar Kano karkashin Alhaji Abba Kabir Yusuf, ta yi alkawarin dawo da biyan  karin kudaden da ake biyan ma’aikata a duk shekara, nan take bayan an gudanar da aikin tantance ma’aikata da tantance bayanan da aka yi.

A sanarwar da daraktan wayar da kan al'uma na hukumar, Bashir Habib Yahaya ya sanyawa hannu, yace Babban Akanta Janar na Jihar Kano, Alhaji Abdulkadir Abdulsalam ne ya bayyana hakan a lokacin wani taro da masu ruwa da tsaki kan yadda ake gudanar da aikin tantancewa da daukar bayanan ma'aikatan 

Alhaji Abdulkadir ya bayyana cewa tun bayan amincewar majalisar zartarwa ta jiha na gudanar da aikin da kuma abin da gwamnan jihar Alhaji Abba Kabir Yusuf ya kaddamar, nan da nan aka fara shirye-shirye tare da kara zage damtse don ganin an gudanar da aikin.

Ya ci gaba da cewa, gwamnatin jihar ta amince da kwamitoci biyu na dindindin kan aikin biyan albashin ma’aikata a matakin jiha da kananan hukumomi baya ga ‘yan fansho.

A nasa jawabin kwamishinan kudi da ci gaban tattalin arzikin jihar Alhaji Ibrahim Jibrin Fagge ya bayyana cewa gwamnatin jihar ta kaddamar da wannan aikin ne domin tantance adadin ma’aikatan ta domin kaucewa zurarewar kudaden jama’a.

A nasa jawabin shugaban kwamitin riko na biyan albashin ma’aikata na jiha, Alhaji Faruk Umar Ibrahim ya bayyana wasu ayyuka da shawarwarin kwamitin na sa kan yadda ya kamata a gudanar da aikin.

Ya ci gaba da cewa, kwamitocin biyu a shirye suke su karbi shawarwari da lura wadanda za su yi matukar amfani wajen gudanar da atisayen cikin nasara.

Tun da farko, a nasa jawabin, sakataren gwamnatin jihar (SSG), Dakta Abdullahi Baffa Bichi, ya umarci kwamitocin a maimakon rubuta lambar tantance bankin (BVN) a kan fom din a lokacin tantancewa.



Sunday, 10 December 2023

Sanatoci Sun Sallama Albashinsu Na Disamba Ga Mutanen Tudun Biri

Sanatocin Najeriya gaba dayansu sun sadaukar da albashinsu na watan Disamba ga mutanen da harin bom da jirgin soji ya samu a wurin taron Mauludi a Jihar Kaduna.

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau Jibrin ya sanar cewa sanatocin su 109 sun amince a ba da albashin nasu a matsayin gudunmuwar ga mutanen Tudun Biri.


Sanata Barau wanda ya yi bayani a yayin ziyararsu fadar gwamnatin Kaduna domin jajanta wa Gwamna Uba Sani kan tsautsayi, ya bayyana cewa albasjin ya kama Naira miliyan 109.

Ya ce hakika sun yi bakin ciki bisa tsautsayin da ya auka wa al’ummar garin na Tudun Biri da ke Karamar Hukumar Igabi, kuma majalisar ta sha alwashin yin bincike domin gano musabbabin abin da ya faru.


Gwamna Uba Sani a jawabinsa ya mika godidyarsa ga dukkan ’yan majalisar da suka jajanta masa, inda ya bukaci su tabbatar da Hakimin Yan Tudun Biri ya fito kunya ta hanyar yi musu adalci.

Ya kumu nuna rashin jin dadinsa bisa yadda wasu ke neman sanya rigar addini ko kabilanci a kan abin da ya faru, inda ya ce abin ba haka yake ba.
(AMINIYA)

Thursday, 4 May 2023

Saudiyya Ta Yi Wa Messi Tayin Ninkin Albashin Ronaldo

 


Kungiyoyin kwallon kafa a kasar Saudiyya na zawarcin gwarzon dan wasan duniya, Lionel Messi, na kungiyar PSG, da tayin albashin da ya zarce na kowane dan wasa a duniya.

Rahotanni sun nuna cewa wata kungiya da ke zawarcin Messi a Saudiyya ta yi masa tayin albashin Naira biliyan 183.5 (Dala miliyan 400) a shekara, idan kwantaraginsa ya kare da PSG a wata mai zuwa.

Kafar labarai ta Telegraph ta kasar Birtaniya ta ce dan wasan ya fara tunanin duba tayin kuma tuni kungiyar ta fara tattaunawa da Kyaftin din na kasar Argentina kan kwangilar da take masa tayi, bayan dakatarwar da PSG ta yi masa.

Idan hakan ta tabbata, Messi zai rika karbar kusan ninki biyun albashin babban abokin hamayarsa Cristiano Ronaldo, wanda a halin yanzu Al Nassr ta kasar Saudiyya ke biyan sa Naira biliyan 96.3 Dala miliyan 210 a shekara, zuwa 2025.

Wannan sabuwar ta taso ne bayan da kungiyar PSG ta dakatar da Messi na tsawon mako biyu ba tare da albashi ba, saboda wata ziyara da ya kai Saudiyya ba da izinin kungiyar ba.

A baya dai an yi ta rade-radin kungiyar Al Hilal ta Saudiyya ce ke neman daukar Messi, daga baya da PSG ta takatar da shi kuma maganar ta kara tasowa.

AMINIYA

Tuesday, 25 April 2023

Kotu ta umarci Bankin Guarantee Ya Biya N5.7m Da Muhuyi Rimingado Daga Asusun Gwamnatin Kano

Kotun ma'aikata ta kasa da ke Abuja ta umarci Bankin (GT) da ya biya korarren shugaban hukumar KORAFE-KORAFE jama’a da yaki da cin hanci da rashawa ta jihar Kano, Muhuyi Rimingado, kudi N5,713,891.22 daga asusun albashi na gwamnatin jihar.

Adadin kudaden da  Rimingado ke bin gwamnatin ne na albashin ma’aikata, bayan dakatar da shi a watan Yulin 2021.

DAILY NIGERIAN ta ruwaito cewa gwamnatin jihar ta dakatar da Mista Rimingado ne bayan bude bincike kan wasu kwangiloli da ake zargin an baiwa wasu kamfanoni masu alaka da iyalan gwamnan.


A zaman da aka ci gaba da yi a ranar Talatar da ta gabata, Bankin ta bakin lauyansa Joshua Shekwolo ya shaida wa kotun a cikin wata takardar neman sahalewa cewa gwamnatin jihar Kano ta na da asusun ajiyar banki da jimillar kudaden da suka kai N5,713,891.22 kasancewar an toshe hukuncin da aka yanke kan lamarin. a cikin asusun.



Da yake bayar da cikakkiyar umarnin, mai shari’a O.O Oyewumi ya umarci GTBank ya biya kudin a asusun Mista Rimingado cikin sa’o’i 48.

An bayar da umarnin ne bayan gazawar gwamnatin jihar wajen mutunta hukuncin da kotun ta yanke a ranar 14 ga Disamba, 2022, inda ta bayar da umarnin biyan da kuma amincewa da Mista Rimingado a matsayin halastacen shugaban hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta jahar Kano 

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

FG Urges KOICA, FAO to Align Agricultural Intervention with Nigeria’s Development Priorities, Ward-Based Strategy

The Federal Government has called for stronger alignment between development partners’ interventions and Nigeria’s national deve...