Posts

Showing posts with the label Atiku Abubakar

Gobara Ta Barke A Gidan PDP

Image
  Ga dukkan alamu gobara ta sake barkewa a gidan babbar jam’iyyar adawa ta kasar nan wato PDP, wadda ta sake shiga rudu, makonni kadan da faduwarta a zaben Shugaban Kasa. A ranar Talata da ta gabata ce, Kwamitin Zartarwar Jam’iyyar na Kasa (NWC), ya ayyana Ambasada Iliya Umar Damagum a matsayin Shugaban Riko na jam’iyar ta kasa. Kafin nadinsa, Alhaji Iliya Damagum shi ne Mataimakin Shugaban Jam’iyyar PDP na kasa Shiyyar Arewa. Kakakin Jam’iyyar PDP, Debo Ologunagba ne ya bayyana nada Damagun a ranar Talata a wani taron manema labarai a Abuja. A sanarwar da PDP ta fitar, ta ce ya zame mata dole ta yi biyayya ga umarnin wata kotu da ta bukaci Shugaban Jam’iyyar na Kasa Dokta Ayu Iyorchia ya daina bayyana kansa a matsayin shugaban jam’iyyar har zuwa lokacin da za ta yanke hukunci kan kararsa da aka kai gabanta. Wata Babbar Kotu a Jihar Benuwai ce ta dakatar da Dokta Iyorchia Ayu daga shugabancin Jam’iyyar PDP ta Kasa. Alkalin Kotun, Mai Shari’a W.I Kpochi ne ya bayar da umarnin a rana...

Zamu Kalubalanci Zaben Shugaban Kasa - Atiku Abubakar

Image
Ɗan takarar shugaban ƙasa na babbar jam’iyyar hamayya a Najeriya, PDP, Atiku Abubakar ya ce dole ne kowa ya ƙalubalanci zaɓen da aka yi na ranar 25 ga watan Fabarairu. A taron manema labarai da ya gabatar a Abuja, tsohon mataimakin shugaban ƙasar ya ce, abin da ya faru a kan zaɓen fyaɗe ne aka yi wa dumukuradiyya. Atiku ya ce, a tarihin ƙasar wannan shi ne zaɓe mafi muni da aka taɓa yi, wanda kuma dama ce ta sake daidaita Najeriya. Amma kuma hukumar zaɓen ƙasar, INEC ta lalata tare da watsa wannan dama da buri na ‘yan Najeriya. Ɗan takarar na PDP, ya ce zaɓen ya kasa kaiwa matsayi da matakin da aka sa rai zai kai. Sannan ya ce lauyoyinsu suna duba lamarin kafin su san matakin da za su ɗauka na gaba. Ya ce idan har ya je kotu ba a yi masa adalci ba to zai bar su da Allah. Za mu kawo muku karin bayani a nan gaba. BBC