Posts

Showing posts with the label Kujerun Aikin Hajji

Hajj 2024 : Hukumar Alhazai Ta Bauchi Ta Siyar Da Kujerun Haji Guda 1700- Imam Abdurrahman

Image
Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Bauchi ta sayar da kimanin guraban kujerun aikin hajji akalla *1700* daga cikin guda *3364* da Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta ware wa Jihar Bauchi. A sanarwar da Jami'in hulda da jama'a na hukumar, Muhammad Sani Yunusa ya sanyawa hannu, yace Sakataren zartarwa na hukumar jindadin alhazan ta jihar Bauchi Imam Abdurrahman Ibrahim Idris,shi ne bayyana hakan yayin  zantawarsa da manema labarai kan shirye shiryen aikin hajji daga Bauchi, inda yace wayarda alumma kan sabbin tsare tsaren aikin hajjin na shekarar 2024 daya gudana a jihar Bauchi yayi tasiri kwarai da gaske. Imam Abdurrahman ya alakanta nasarar gudanar da atisayen wayarda kan alummar ne da irin gudumawa da goyon bayan da tsarin ya samu daga sarakunan mu na jihar Bauchi da shugabannin kananan hukumomi da limamai da sauran masu ruwa da tsaki a aikin Hajji. Ya kara da cewa sabbin tsare-tsare na Saudiyya kan ayyukan Hajji na shekarar 2024 ne suka tilastawa kasashe fara  s

NAHCON Ta Dakatar Da Rabon Kujeru Ga Kanfanonin Jirgin Yawo

Image
Hukumar Aikin Hajji ta kasa (NAHCON) a dakatar da rabon kujeru aikin Hajjin 2024 ga kamfanonin jirgin yawo 40 da suka yi nasarar samun aikin jigilar maniyyata. NAHCON ta dakatar da rabon kujerun ne saboda korafe-korafen da zargin rashin adalci da wasu kamfanonin da ba su yi nasara ba ke yi. Mai magana da yawun NAHCON, Fatima Sanda Usara, ta ce hukumar na sane da irin wadanna zarge-zarge daga wasu kamfanonin da ba su yi nasara a tantancewar da aka yi ba. Don haka aka dakatar da akai na tsawon awa 48 masu zuwa, domin daukar matakin da ya dace, tabbatar da tsafta a aikin da kuma kare martabar kukumar. (AMINIYA)

Hukumar Alhazai Ta Kano Ta Bukaci Jami’anta Na Kananan hukumomi Da Su Gaggauta Siyar Da Kujerun Aikin Hajji

Image
Darakta Janar na Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kano, Alhaji Laminu Rabi’u Danbappa, ya jaddada bukatar daukar matakin gaggawa na jami’an Hukumar alhazai na kananan hukumomi domin ganin an siyar da kujerun aikin Hajji a kan lokaci. A sanarwar da Jami'in hulda da jama'a na hukumar, Sulaiman Abdullahi Dederi ya sanyawa hannu, yace Darakta Janar din yayi jawabin ga mahalarta taron a ranar Alhamis a taron bita na yini daya da hukumar ta shirya a sansanin ‘yan yawon bude ido na jiha, Alhaji Laminu Rabi’u Danbappa ya bukaci jami’an su kara zage damtse wajen siyar da dukkanin kujerun aikin Hajji da aka ware daga kananan hukumomi daban-daban. Da yake karin haske game da lamarin, ya jaddada wajabcin karbar kudaden ajiya 4.500,000 daga maniyyatan da suka nufa a karshen wata mai zuwa, musamman nan da ranar 25 ga Disamba, 2023. Bugu da kari, Alhaji Laminu Danbappa ya bayyana muhimman bayanai, inda ya bayyana cewa Saudiyya na shirin kammala bayar da bizar kwana 5