Search This Blog

Tuesday, 26 December 2023

Hajj 2024 : Hukumar Alhazai Ta Bauchi Ta Siyar Da Kujerun Haji Guda 1700- Imam Abdurrahman

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Bauchi ta sayar da kimanin guraban kujerun aikin hajji akalla *1700* daga cikin guda *3364* da Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta ware wa Jihar Bauchi.

A sanarwar da Jami'in hulda da jama'a na hukumar, Muhammad Sani Yunusa ya sanyawa hannu, yace Sakataren zartarwa na hukumar jindadin alhazan ta jihar Bauchi Imam Abdurrahman Ibrahim Idris,shi ne bayyana hakan yayin  zantawarsa da manema labarai kan shirye shiryen aikin hajji daga Bauchi, inda yace wayarda alumma kan sabbin tsare tsaren aikin hajjin na shekarar 2024 daya gudana a jihar Bauchi yayi tasiri kwarai da gaske.

Imam Abdurrahman ya alakanta nasarar gudanar da atisayen wayarda kan alummar ne da irin gudumawa da goyon bayan da tsarin ya samu daga sarakunan mu na jihar Bauchi da shugabannin kananan hukumomi da limamai da sauran masu ruwa da tsaki a aikin Hajji.

Ya kara da cewa sabbin tsare-tsare na Saudiyya kan ayyukan Hajji na shekarar 2024 ne suka tilastawa kasashe fara  shirye-shiryen ayyukan Hajjinsu da wuri.

 Imam Abdurrahman ya ci gaba da tunatar da cewa NAHCON ta sanya *N4.5M* a matsayin kudin ajiya na bana tare da bayar da wa'adin watan Disamba na tura kaso na farko daga dukkan Jihohin a kasa domin su kare  gurbin kujerun  aikin Hajji da aka ware musu.

A cewar sa "a baya dai mun aiyana karshen watan Disamba na 2023 a matsayin wa'adin karban kudin ajiyar aikin hajjin 2024, zamu saurari hukumar alhazai ta kasa don jin umurni na gaba"

Imam Abdurrahman ya shawarci maniyyata dasu yi anfani da wannan lokaci na musamman wajen cikita kudin ajiyarsu na N4.5M, harilayau sabbin masu biya, suma dama ce garesu dasu biya kudin ajiyar tasu.

 

Wednesday, 20 December 2023

Shugaban Majalisar Dokoki Ta Katsina Ya Raba Tallafin Naira Miliyan 35

Kakakin Majalissar Dokoki ta Jihar Katsina, Nasir Yahaya, ya bayar da tallafin Naira Million Talatin da Huɗu da Dubu Ɗari Tara da Hamsin. (34,950,000) ga Mutum Dubu Ukku (3000) a filin wasan Ƙwallon Kafa dake Daura

Hadimin tsohon Shugaban Najeriya, Buhari Sallau, ya rawaito a shafinsa na Facebook cewa, an bayar da Tallafin ga Marayu, Limamai, Zawarawa, Masu Ƙananan Sana'oi, Exco, Mata, Matasa, Students, yan Media, Dagattai, Mabuƙata, yan siyasa, Ƙungiyar Teloli, Ƙungiyar Masu Shayi da Masu chajin waya, da sauran su. Inda ko wanne daga cikinsu zai amfana da Tallafin, Naira Dubu Goma (10,000)

Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Radda PhD, yayi Jin-Jina gami da fatan Alkhairi ga Kakakin Majalissar akan wannan abin Alkhairi da yayi, sannan yayi roƙo gami da Jan hankali ga wanda suka amfana da wannan Tallafin da suyi amfani dashi ta hanyar daya dace, domin su bunƙasa Kasuwar su. 

Haka kuma Mataimakin Shugaban Jam'iyyar APC na Jihar, Alh. Bala Abu Musawa, ya taya mutanen Daura murna, bisa ga Jajirtaccen Shugaba da suka samu.

Taron ya samu Halartar Tsohon Shugaban Ƙasar Nigeria, Gen. Muhammadu Buhari, Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Raɗɗa PhD, Shugaban Jam'iyyar APC na Jiha da Mataimakinsa, Yan Majalissar Dokoki ta Jihar Katsina, kwamishinoni da masu bada shawara, Wakilin Mai Martaba Sarkin Daura, Hajia Ambarud Sani Wali, Shugaban karamar hukuma, Tsofaffin yan Majalissar Jiha, Barr. Ahmad Usman El-Marzuq, da sauran manyan baƙi

Kakakin Majalissa ya bayar da kyautar Sa (Bijimi) ga Muhammadu Buhari, da kyautar Doki ga Gwamna Malam Dikko Umaru Raɗɗa. 
 
Sannan Ƙungiyoyin Daura Forum, DECA, DEDA, Health and Education Department, Ƙungiyoyin Addini, da Babbar Ƙungiyar, Daura Consortium sun bayar da Lambobin Yabo da Girmamawa (Award) ga Mai Girma Kakakin Majalissar Dokoki a bisa ayyukan Alkhairin da yake aikatawa ba dare ba rana a Daura

Haka zalika Ƙungiyar Daura Forum ta bada lambar yabon ga  Muhammadu Buhari, da Gwamna Malam Dikko Umaru Raɗɗa  

Daga karshe Kakakin Majalissa yayi Godiya ga manyan baƙi da suka halarci wannan Babban taron, sannan yayi Addu'a da fatan Allah ya maida kowa gidanshi lafiya, l

Shugaban NAHCON Ya Ziyarci Ofishin Jakadancin Saudiyya na Abuja.

Shugaban Hukumar Aikin Hajji ta Najeriya wato NAHCON, Malam Jalal Ahmad Arabi, ya kai ziyarar ban-girma zuwa ofishin Huldar Jakadanci na Saudiyya inda ya gana da Jakadan Saudiyya dake Abuja, Ambasada Faisal Ibrahim Al-Ghamidy, a ranar Laraba  

A sanarwar da Hukumar ta fitar ta ce, Shugaban ya kai ziyarar ce da nufin bunkasa dangantaka da habakar da hadin-gwiwa tsakanin bangarorin biyu.
 
Malam Arabi ya jaddada jin dadinsa ganin yadda Jakadan Kasar Saudiyya Ambassada Faisal ke bada cikakken goyon-baya ga Hukumar da tareraya irinta Huldar Jakadanci karkashin  Ofishin Jakadancin Saudiyyar.

Sanarwar tace ziyarar, ta bayyana karara yadda dadaddiyar alaqa ta jituwa ke tsakanin NAHCON da Ofishin Jakadancin Saudiyyar, abinda ke nuni da fahimtar-juna da hadin kai dake wanzuwa a tsakanin Kasashen biyu.

A Yayin ganawar, bangarorin biyu
 sun zanta batutuwa masu ma’anar gaske, abunda ke tabbatar da muhimmancin tarayyarsu wajen kara inganta gudanar da Al-amurran Aikin Hajji A Najeriya

Shugaban NAHCON ya bayyana jinjinarsa ga cigaba da habakar da temakekeniyar da Ofishin Jakadancin Saudiyya ke baiwa Hukumar Hajjin, abunda ke haifar da samun nasarar gudanar da Aikin Hajji cikin walwala da dadin-rai ga Alhazan Najeriya. 

Bisa wannan ci gaba, bangarorin guda biyu sun sha  alwashin kara jajircewa da yin tsayin-daka wajen ganin sun kara zama tsintsiya madaurinki daya wajen aiwatar da hadahadar Aikin Hajjin tare da cikakken hadin-gwiwa da zai cigaba da samar da sakamako melai dorewa da wanzar da ingantaccen Hajji ga Alhazai da sauran masu ruwa da tsaki a Harkar Gudanar da Hajji.

Wannan hadin gwiwa dake tsakanin NAHCON da Ofishin Huldar Jakadancin Saudi Arabiya, zai ci gaba da share fagen ingantuwar kai kawo da musayar bayanai da samar da walwala ga dubban Alhazai Maniyyata zuwa Ibadar Hajji. 

Hakazalika, Sun daura azama da aniyar gaggauta hanyoyin samarwa Maniyyata jin dadi yadda ya kamata.

A wani ci gaba kuma, nan ba da jimawa ba ne, Hukumar NAHCON  zata kammala bincike-binciken korafe-korafen da kamfanonin jirgin yawo suka gabatar a gabanta don tabbatar da ganin wadanda aka tantance ba suda wata matsala domin su gudanar da kai Alhazan shekarar bana ta hanyar jiragen-yawo lami lafiya. 
 
Za a iya tunawa ranar sha uku ga watan nan na Disamba, NAHCON ta sanar da dakatarwa ta wani dan-lokaci don tsagaita raba kujerun tafiya Hajjin bana ga kampanonin-jigilar Maniyyata. Anyi hakan don kwatanta rabo na Allah da Annabi, biyo bayan korafe-korafe da suka bijiro daga wasu bangarori. 

Sanarwar tace NAHCON na nan kan wannan tsaikon har sai ta tabbatar da gaskiyar lamari don samun Rabo na gaskiya ga dukkan kamfanonin na jigilar Alhazan.


Monday, 18 December 2023

Kotun Koli Ta Tsayar Da Ranar Da Za Ta Saurari Karar Zaben Gwamnan Kano

Kotun koli ta sanya ranar Alhamis 21 ga watan Disamba domin cigaba da sauraron karar zaben gwamnan Kano tsakanin gwamna Abba Kabiru Yusuf na jam’iyyar New Nigeria Peoples Party NNPP da Nasiru Yusuf Gawuna na jam’iyyar APC. 

KANO FOCUS ta rawaito cewa a cikin sanarwar da magatakardar kotun daukaka kara ta aikewa lauyoyin bangarorin biyu, kotun za ta saurari karar da NNPP ta shigar da kararrakin wasu jam’iyyu. 

Gwamna Yusuf na kalubalantar hukuncin da wasu bangarori uku na kotun daukaka kara suka yanke wanda ya soke nasarar da ya samu tare da tabbatar da hukuncin da kotun sauraren kararrakin zabe ta yanke. Kotun sauraron kararrakin zabe karkashin jagorancin mai shari’a Osedebay ta bayyana dan takarar jam’iyyar APC, Nasiru Gawuna a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan jihar Kano a watan Maris. 

Kotun daukaka kara ta yi watsi da karar da Gwamna Yusuf ya shigar bisa matsayinsa na zama mamba a jam’iyyarsa sannan ta zargi kotun da yin watsi da hujjar da ta yanke. Kotun ta kori Gwamna Yusuf ne saboda amfani da takardun zabe da hukumar zabe mai zaman kanta (INEC) ba ta sa hannu, ko kwanan wata ko tambari ba. 

An dai samu rudani a dukkan shari'ar yayin da NNPP ta gano hujjojin da CTC na kotun daukaka kara da ta tabbatar da Gwamna Yusuf a matsayin wanda ya lashe zaben, wanda ya sabawa abin da alkalan kotun suka karanta. Raba wannan: 
 

Sunday, 17 December 2023

Kofa Ya Raba Tallafin Kudi Ga Mata Guda Dari Biyar A Mazabarsa

A ci gaba da tagomashin arzikin da yake yi wa mutanen mazaɓarsa, Abdulmumin Jibrin Kofa, ɗan Majalisar Wakilai na Kiru da Bebeji daga jihar Kano, a ranar Lahadi ya sake gwangwaje mata 500 da tallafin kuɗi.

A sanarwar da hadimin ɗan majalisar kan yaɗa labarai, Sani Ibrahim Paki ya fitar, yace an  yi taron rabon tallafin ne a mahaifar ɗan majalisar da ke Kofa a Ƙaramar Hukumar Bebeji, Kano, kuma wannan shi ne karo na bakwai da yake raba irin wannan tallafin a ’yan makonnin nan. 
Idan za a iya tunawa, a baya ɗan majalisar ya raba tallafin ga shugabannin al’umma, mata da matasa, ɗalibai, ’yan social media, malamai da masu rike da sarautun gargajiya. 

Wannan ne dai rabon tallafi karo na bakwai tun bayan farawa, kuma karo na biyu ga mata.
Bugu da ƙari, ɗan majalisar ya karɓi baƙuncin fitacciyar ’yar asalin Bebejin nan, kuma jigo a jam’iyyar NNPP, Hajiya Azumi Babeji, wacce ita ma ta halarci bikin sannan ta gabatar masa da takardar nadin da Gwamnatin Jihar Kano ta yi mata. 
Dan majalisar ya mika godiya ga gwamnatin saboda ganin cancantarta har ta ba ta wannan muƙamin.


Friday, 15 December 2023

Hukumar Alhazai Ta Kano Ta Yi Ga NAHCON Da Ta Samar Canjin Dala Kan Farashin Gwamnati Ga Maniyyata

Darakta Janar na Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kano, Alhaji Laminu Rabi’u Danbappa, ya bukaci Hukumar Alhazai ta kasa NAHCON ta kara zage damtse wajen ganin an samu dala a farashin gwamnati  ga wadanda zasu halarci aikin hajjin bana.

A sanarwar da Jami'in hulda da jama'a na hukumar, Sulaiman Abdullahi Dederi ya sanyawa hannu, yace Alhaji Laminu Rabi’u Danbappa ya bayyana hakan ne a wata ganawa da kungiyar Arewa New Agenda a wata ziyarar wayar da kai da hukumar alhazai ta kasa suka kai Kano, wanda aka gudanar  a ofishinsa.

Ya kara da cewa karin kudin aikin Hajjin bana da kuma karancin lokacin biyan kudi na daga cikin matsalolin dake kawo tsaiko wajen biyan kudaden ajiya.

Da yake mayar da jawabi kan wadannan matsalolin, shugaban tawagar kungiyar Arewa New Agenda daga Hukumar Alhazai ta kasa, Dakta Muhd Lawan Salisu, ya tabbatar wa darakta Janar din cewa, sun dukufa wajen hada kai da hukumomin da abin ya shafa, ciki har da Sarkin Musulmi, domin mika kokon bara ga shugaban kasa kan wannan bukata. na tallafin aikin Hajji.

Dokta Muhd Lawan Salisu ya yi alkawarin binciko duk hanyoyin da za a bi domin saukaka samun sauki da samun saukin kwarewar aikin hajji.

A nasa jawabin shugaban hukumar, Yusif Lawan ya ce hukumar ta ci gaba da dukufa wajen tabbatar da jin dadi da walwala ga dukkan mahalarta aikin Hajji, tare da yin aiki kafada da kafada da hukumar alhazai ta kasa domin magance kalubale da habaka aikin hajjin baki daya.

Taron ya samu halartar dukkan ma’aikatan hukumar, da jami’an Hukumar na kananan hukumomi da wasu daga cikin malaman bita 


                  

Thursday, 14 December 2023

Gwamnatin Kano Ta Tabbatar da Gano Illar Bata Tarbiyya Yara Mata A Shirin Tallafawa Ilimi Na AGILE

Biyo bayan zarge-zargen bata tarbiyya da ake yiwa shirin tallafawa ilimin yaya mata na AGILE, ma’aikatar ilimi ta jihar Kano ta gudanar da taron karawa juna sani na yini biyu kan shirin.

Premier Radio ta rawaito a shafinta na Facebook cewa, Kwamishinan ilimi na jihar Kano, Umar Haruna Doguwa, wanda ya yi magana a yayin taron na masu ruwa da tsakin da ke nazarin horar da dabarun rayuwa a karkashin shirin, ya ce ma’aikatar ta fitar da wani sabon salo na abubuwan da shirin ya kunsa.


Ya ce malamai sun yi korafin cewa a cikin shirin akwai wasu abubuwa da basu amince da su ba inda suka duba korafin nasu kuma suka gano matsalar dake cikin sa yayin da aka cire duk wani da ya saba da al’ada da koyarwar addnini muslunci.

A nashi bangaren, co’odinetan shirin na AGILE a nan Kano, Alhaji Nasiru Abdullahi-Kwalli, ya ce ma

NAHCON Ta Dakatar Da Rabon Kujeru Ga Kanfanonin Jirgin Yawo

Hukumar Aikin Hajji ta kasa (NAHCON) a dakatar da rabon kujeru aikin Hajjin 2024 ga kamfanonin jirgin yawo 40 da suka yi nasarar samun aikin jigilar maniyyata.

NAHCON ta dakatar da rabon kujerun ne saboda korafe-korafen da zargin rashin adalci da wasu kamfanonin da ba su yi nasara ba ke yi.


Mai magana da yawun NAHCON, Fatima Sanda Usara, ta ce hukumar na sane da irin wadanna zarge-zarge daga wasu kamfanonin da ba su yi nasara a tantancewar da aka yi ba.

Don haka aka dakatar da akai na tsawon awa 48 masu zuwa, domin daukar matakin da ya dace, tabbatar da tsafta a aikin da kuma kare martabar kukumar.
(AMINIYA)


Wednesday, 13 December 2023

Na shiga matsananciyar damuwa da hare-haren 'yan bindiga a 'yan kwanakin nan - Gwamnan Zamfara

Gwamnan ya bayyana hakan ne a cikin wani sako da ya wallafa a shafinsa na Facebook

Inda yace "A madadin gwamnatin Jihar Zamfara, ina miƙa saƙon ta'aziyya da jaje ga al'ummar ƙaramar hukumar Zurmi, musamman iyalai da ‘yan uwan waɗanda suka rasa rayukansu a harin ta'addanci da 'yan bindiga suka kai garin" 

Ina son tabbatarwa da al'umma cewa gwamnatina za ta bayar da tallafi da agajin gaggawa ga mutanen da abin ya shafa. Sannan ina mai tabbatar da cewa muna nan jajirce akan tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin al'ummar Zamfara baki ɗaya.

Ina sane da sadaukarwar da jami’an tsaro suke yi a ƙoƙarin da suke na kare rayukan al’umma, gwamnatina za ta ba su duk wasu kayan aiki da kuma tallafin da suka dace domin yaƙar ‘yan bindiga, ba za mu huta ba har sai Zamfara ta samu cikakken tsaro insha Allahu.
 
Waɗannan sabbin hare hare sun biyo bayan nasarar da jami'an tsaro suka samu ne, na kashe shugabannin 'yan ta'addan. Ciki har da nasarar kashe Kachalla Ali Kawaje, Shugaban ‘yan bindiga da ya jagoranci sace ɗaliban jami’ar tarayya dake Gusau.
 
An samu nasarar kawar da shugabannin ɓarayin da dama a wurare daban-daban da suka haɗa da Danjibga, dajin ‘Yar tsakuwa, dajin Munhaye, dajin Kauran Zomo, dajin Dansadau, da kauyen Akuzo.
 
Ina sake jaddada wa al'ummar Jihar Zamfara cewa, da yardan Allah zan ci gaba da bin dukkan matakan da suka dace don tabbatar da zaman lafiya a faɗin jiharmu mai albarka.

Shugaban Hukumar NAHCON Ya Karbi Rahoto Kan Masaukin Alhazai Tare Da Alkawarin Sake Inganta Ayyuka

Mai rikon mukamin Shugaban Hukumar Alhazai ta Najeriya (NAHCON), Malam
Jalal Ahmed Arabi, OON, fwc, ya ce ba da fifiko tare da inganta jin dadin mahajjata da ayyukansu shi ne babban aikin da Hukumar za ta gudanar a lokacin aikin Hajjin shekarar 2024.

A sanarwar da Mataimakin daraktan yada yada labarai da dab'i na hukumar, Mousa Ubandawaki ya sanyawa hannu, yace Shugaban ya bayyana haka ne a lokacin da yake karbar rahoton kwamitin duba sharuɗɗan masauki da ciyarwa yau a dakin taro na hukumar

Ya ce samar da ingantacciyar hidima aiki ne mai matukar muhimmanci da hukumar za ta bi domin cika aikinta tare da dorewar amana da amincewar jama’a da kuma alhazai.
A cewarsa, gabatar da rahoton da shawarwari a cikinsa “zai taimaka matuka wajen farfado da kwarin gwiwa da amincewar mutane da alhazai musamman a gare mu.

“Ina so in gode muku bisa sadaukarwar da kuka yi. Wannan rahoto da shawarwarin ba shakka za su ba da gudummawa don haɓaka hanyoyin ci gaba da aiwatar da abubuwa. Na san cewa babu wani abu mai dorewa a rayuwa kamar canji don haka muna bukatar mu zama masu kirkira ta yadda muke yin abubuwa. Ina mai tabbatar muku da cewa za mu duba tashar jirgin, tare kafin aiwatar da shi domin samun damar samun sauye-sauye masu kyau a yadda muke gudanar da ayyukan alhazai.”

Malam Arabi ya kuma bukaci Hukumar Jin Dadin Alhazai na Jiha da su baiwa hukumar hadin kai tare da marawa hukumar baya a aikinta inda ya ce, “ba wani riba ba ne a ce akwai bukatar karin hadin kai tsakanin Hukumar da Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jiha. Ina mai farin cikin ganin cewa wasu daga cikin shuwagabannin hukumar jin dadin Alhazai ta Jiha suna cikin kwamitin, ina fatan za ku mika sakon ga abokan aikin ku cewa suna bukatar yin layi a cikin wasu shawarwarin da kuke bayarwa, kuma ku gamsar da su. shawarwarin da kuka bayar a cikin rahoton shi ne mu sanya yadda muke gudanar da ayyuka cikin sauki da kuma ci gaban kowa."

Tun da farko, Dr Aliyu Tanko wanda shi ne Shugaban Kwamitin ya nuna jin dadinsa da amincewa da aka yi masu. 
Ya bayyana cewa Kwamitin ya ba da shawarwari masu nisa don kawar da shirye-shiryen ciyar da abinci da masauki daga wasu matsalolin.

Za a iya tunawa tuna cewa an kafa kwamitin mai wakilai 16 kuma an kaddamar da shi ne a ranar 5 ga watan Disamba tare da ayyuka kamar haka:
I. Don kimanta jagororin masauki da abinci na yanzu.

II. Don tantance ma'auni na yanzu na mahajjata masauki da ayyuka na ciyar da abinci.

III. Gano wuraren ingantasu

IV. Ba da shawarar sake duba jagororin da za su tabbatar da jin daɗi da ƙwarewa ga mahajjatanmu.


Monday, 11 December 2023

Labari Da Dumiduminsa: 'Yan Majlisar Jahar Rivers 27 Masu Biyayya Ga Wike Sun Bar PDP Zuwa Jam'iyyar APC

Akalla ‘yan majalisar dokokin jihar Ribas 27 cikin 32 ne suka sauya sheka daga jam’iyyar PDP zuwa jam’iyyar APC, sakamakon rikicin da ya barke tsakanin gwamnan jihar Ribas, Siminalayi Fubara da ministan babban birnin tarayya (FCT). Nyesom Wike ya zurfafa.


Wani dan majalisar, Enemi George, ya tabbatar wa gidan talabijin na Channels cewa ‘yan majalisar 27 na karkashin jagorancin Martin Amaewhule ne.

'Yan majalisar sun yanke Wannan hukuncin ne a yayin zamansu na safiyar ranar Litinin

(DailyNews24)

Sunday, 10 December 2023

Gwamnan Katsina Ya Ceto Wanda Yan Ta'adda Suka Sace

Gwamnan Katsina, Dikko Raddah, ya jagoranci fatattar ’yan bidiga a kauyen Zakka a Karamar Hukumar Safana ta jihar.

Gwamnan ya jagornaci jami’an tsaro hadin gwiwa wajen ceto wani matashi da ’yan bindiga suka yi garkuwa da shi.


Dikko Radda ya jagoranci kai daukin ne a lokacin da ya je karamar hukumar kaddamar da shirin tallafi na mataimakin shugaban majalisar jihar, Abduljalal Runka.

Sakataren yada labaran gwamna, Kaula Mohammed, ya ce kafin kaddamar da tallafin ne jami’an tsaro suka samu kiran gagawa cewa ’yan ta’adda sun kai hari kauyen Zakka.

Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya (NAN) ya ruwaito Kaula na cewa, nan take gwamnan ya dakatar da shirin, shige gaba aka fattaki ’yan bindigar, aka ceto matashin.

Daga nan gwamnan ya ba da umarnin kai mutumin asibiti domin kula da shi, saboda harbin sa da aka yi a kafa.

Sanatoci Sun Sallama Albashinsu Na Disamba Ga Mutanen Tudun Biri

Sanatocin Najeriya gaba dayansu sun sadaukar da albashinsu na watan Disamba ga mutanen da harin bom da jirgin soji ya samu a wurin taron Mauludi a Jihar Kaduna.

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau Jibrin ya sanar cewa sanatocin su 109 sun amince a ba da albashin nasu a matsayin gudunmuwar ga mutanen Tudun Biri.


Sanata Barau wanda ya yi bayani a yayin ziyararsu fadar gwamnatin Kaduna domin jajanta wa Gwamna Uba Sani kan tsautsayi, ya bayyana cewa albasjin ya kama Naira miliyan 109.

Ya ce hakika sun yi bakin ciki bisa tsautsayin da ya auka wa al’ummar garin na Tudun Biri da ke Karamar Hukumar Igabi, kuma majalisar ta sha alwashin yin bincike domin gano musabbabin abin da ya faru.


Gwamna Uba Sani a jawabinsa ya mika godidyarsa ga dukkan ’yan majalisar da suka jajanta masa, inda ya bukaci su tabbatar da Hakimin Yan Tudun Biri ya fito kunya ta hanyar yi musu adalci.

Ya kumu nuna rashin jin dadinsa bisa yadda wasu ke neman sanya rigar addini ko kabilanci a kan abin da ya faru, inda ya ce abin ba haka yake ba.
(AMINIYA)

Tuesday, 5 December 2023

Hajj 2014 : Hukumar NAHCON Ta Kafa Kwamitin Bitar Ka'idojin Samar Da Abinci Da Gidaje.

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta kaddamar da wani kwamiti da zai yi nazari kan wasu sharuddan da suka shafi masauki da abinci don samar da ingantacciyar hidima a lokacin aikin Hajjin 2024.

A sanarwar da Mataimakin daraktan yada labarai da dab'i na Hukumar Mousa Ubandawaki ya sanyawa hannu, yace da yake jawabi a wurin taron, mai rikon Shugabancin Hukumar,  Malam Jalal Ahmad Arabi OON, fwc, ya bayyana cewa sake duba ka’idojin da ake da su za su taimaka wajen inganta ayyukan masu ba da hidima wanda hakan zai amfanar da Alhazan Najeriya.

A cewarsa, kundin tsarin gudanarwar kwamitin ba sabon sabon abu ba ne, amma wata hanya ce kawai ta yin la'akari da tsarin da ake da shi don samar da kyakkyawan sakamako.

“Abin da muke yi yanzu ba wai sabon abu  ba ne kawai don inganta yadda muke yin abubuwa. Kamar yadda yake faruwa a wasu sassa na duniya, muna bukatar mu kasance da ƙwazo. Kamar yadda al'ada ce ta duniya, dole ne mu inganta ta hanyoyinmu, don dacewa da mafi kyawun ayyuka na duniya," in ji shi.

Shugaban ya kuma bukaci kwamitin da ya tunkari wannan aiki da hankali da sanin ya kamata domin rahoton nasu zai yi matukar tasiri wajen yadda hukumar za ta aiwatar da ayyukan na bana.
Wuraren masauki da ayyukan samar da abinci a Saudi Arabia.

“A matsayinku na ƙwararrun ma’aikata, ba ni da tantama cewa za ku yi aikin da cikakkiyar gaskiya. Haka nan kuna da damar fadada fiye da yadda ake tunani, ta yadda duk shawarwarin da kuka bayar za su wadatar da iliminmu da kuma ci gaban Hukumar."

Da yake jawabi a madadin ‘yan kwamitin, Dakta Aliyu Tanko, ya gode wa shugaban bisa wannan damar da aka ba su na yin hidima. Ya bayyana cewa duk da cewa aikin yana da wuyar gaske amma ya bayyana fata da kwarin gwiwa ga ’yan Kwamitin na gudanar da aikin ta hanyoyin da suka dace, yana mai jaddada alakar da ke tsakanin aikin da sakamakon aikin Hajjin 2024.
“Aiki ne mai ban tsoro, ko shakka babu, domin duk abin da muka yi zai yi tasiri ga sakamakon aikin Hajjin 2024 ko dai ko dai ko dai. Amma addu’armu ita ce rahotonmu ya ba da sakamako mai kyau.”


Sunday, 3 December 2023

Yanzu-Yanzu: Ganduje ya sake nada Aminu Hikima sabon mukami a matakin kasa

A cikin sanarwar da Aminu Dahiru Ahmed ya fitar a shafinsa na Facebook, ya ce, wannan shi ne karo na hudu da Baba Ganduje ya nada ni. A lokacinsa na farko a matsayin gwamnan jihar Kano, ya nada ni babban mai taimaka masa na musammam kan harkokin daukar hoto. Haka kuma a wa’adinsa na biyu ya sake nada ni a Wannan matsayi.
 
Lokacin da ya bar ofis bayan shekaru takwas, ya nada ni mai daukar hotonsa na kashin kai. Nadin na baya-bayan nan shi ne na hudu.
 
Aminu Dahiru yace Baba Ganduje ya yi min abin da uba kawai zai yi wa dansa. Ya dauki nauyin karatuna da sauran abubuwa da yawa. "Wacce irin ni'imomin Ubangijinku kuke karyatawa"?

A matsayina na mai daukar hotonsa, ina da abubuwa da yawa da zan ce game da Baba Ganduje. Mai daukar hoto yana aiki tare da maigidansa. Ni ma na yi aiki tare da Baba Ganduje tsawon wadannan shekaru. Ina shaidawa tsohon gwamnan yana da riko da addini, mai tausasawa, mai kirki, mai yarda da mutuntawa har da wadanda ke karkashinsa. Kasancewara da Baba Ganduje ya kawo min sauyi ta fuskoki da dama.
 
Bangaren addini na Baba Ganduje yana da ban sha'awa. Ku yi aiki da Baba Ganduje, tabbas za ku samu yin koyi da  al'adar yin addu'o'in ku a kan lokaci, kuma ku yi ayyukanku na addini cikin aminci.
 
Baba Ganduje ya shahara wajen gina masallatai, makarantun Islamiyya, shirya gasar karatun Alkur’ani da daukar nauyinsu da musulunta. Ganduje ya zuba jari mai yawa ga marasa galihu.
 
Mataimakin na musammam ga Shugaban jam'iyyar APC ta Kasa, ya ci gaba da cewa, A siyasance Baba Ganduje shi ne ainihin ma’anar dan siyasa. Shi ne gwanin da ke bayyana siyasar zamani. Abin sha'awa Baba Ganduje yana yafiya don Allah. Yana ramuwar gayya ne kawai akan cin zarafin da aka yi masa a siyasance.
 
Ta fuskar karfafawa mutane, Aminu yace Ganduje mai baiwa ne ajin farko, wanda yake yi a boye. Zai ba ku, ya sake ba ku kuma ya tambaye ku kada ku gaya wa kowa. Wannan mai bayarwa ne na gaske.
 
Wadannan kyawawan halaye da na lissafo su a sama sun fi su Baba Ganduje da Allah Ta’ala ya karawa rayuwa lafiya, arziki, iyali da mulki. Siffofin guda ɗaya suna zama kagara tsakaninsa da masu zaginsa.
 
Allah Ta'ala Ya ci gaba da kasancewa tare da shi, Ya kuma kare shi daga dukkan sharrin masu makirci. Amin.

Na gode Baba!

Yanzu-Yanzu: Zulum ya amince da nadin Mohammed Dawule a matsayin mai rikon Hukumar Alhazai ta Jahar Borno

Gwamnan jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya amince da nadin Mohammed Dawule Maino a matsayin mukaddashin sakataren hukumar jin dadin alhazai ta jihar Borno.

An bayyana nadin ne a ranar Lahadin da ta gabata a wata sanarwa da sakataren gwamnatin jihar Borno, Hon. Bukar Tijjani.

Sakataren gwamnatin jihar ya kara da cewa nadin wanda ya fara aiki nan take, ya dogara ne akan cancanta da kuma bayanan shekarun baya a aikin gwamnati.

Har zuwa lokacin da Dawule ya nada shi mamba ne a sabuwar Hukumar Ilimi ta Larabci da Sangaya ta Jihar Borno (BOSASEB. Kafin nan, Dawule ya yi aiki a Ma’aikatar Ilimi ta Jihar Borno tsakanin 2015 zuwa 2022.

Ya kuma yi aiki a Makarantar Sakandare ta islamiyya da ke Maiduguri da Kwalejin Gwamnati da ke Maiduguri da kuma Makarantar Alkur’ani ta Model da ke Konduga.

An haifi Mista Dawule mai shekaru 50 a duniya a karamar hukumar Kaga da ke arewacin jihar Borno.

Gwamna Zulum ya taya Mohammed Dawule Maino murna sannan ya ce yana fatan ci gaba da yi masa hidima tare da nagartar al’ummar jihar Borno.

Insight Northeast 

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

FG Urges KOICA, FAO to Align Agricultural Intervention with Nigeria’s Development Priorities, Ward-Based Strategy

The Federal Government has called for stronger alignment between development partners’ interventions and Nigeria’s national deve...