Search This Blog

Showing posts with label Siyasa. Show all posts
Showing posts with label Siyasa. Show all posts

Friday, 28 April 2023

Firaministan Pakistan ya tsallake rijiya da baya

 


Firaministan Pakistan Shehbaz Sharif ya tsallake rijiya da baya, bayan da ‘yan majalisar kasar suka kada kuri’ar yanke kauna, yayin da sauran kungiyoyin fararen hula suka matsa kan a fara shirin gudanar da babban zaben kasar. 

Sharif ya sami kuri’un amincewa guda 180, yayin da ‘yan majalisa 172 suka nuna rashin amincewa da salon shugabancin sa, abinda ya bashi damar ci gaba da rike mukamin sa da kyar. 

Ko da yake jawabi, kakakin majalisar dokokin kasar Raja Pervais Asharf, yace a yanzu abinda majalisar zata mayar da hankakli shine batun babban zaben da ke tafe. 

Sharif wanda ya gaji Imran Khan ya yabawa mambobin jam’iyyyar sa da ke majalisar bayan da suka amince da salón mulkin sa, tare da yanke hukuncin sake bashi dama, ta hanyar kada kuri’ar amincewa da shi. 

rfi

Thursday, 23 February 2023

Yau Ake Rufe Yakin Neman Zaben Shugaban Kasa

 


Daga karfe 12 na daren yau Alhamis 23 ga Fabrairu, 2023, za a fure yakin neman zaben ’yan takarar shugaban kasa da Majalisun Tarayya da za a gudanar ranar Asabar.

Dokar Zaben Najeriya ta haramta yin duk wani nau’in yakin neman zabe ko tallata dan takara daga sa’a 24 kafin ranar zabe.

A yayin rubuta wannan rahoton, kusan awa 12 ya rage wa daukacin jam’iyyu da ’yan takara su yi duk abin da za su iya, su kuma rufe yakin neman zabensu, sannan a fafata a akwatunan zabe a ranar Asabar.

Jam’iyyu 18 ne ke zawarcin kujerar shugaban kasa bayan kammala wa’adin Shugaba Muhammadu Buhari na biyu a ranar 29 ga watan Mayu.

Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ta bayyana cewa za a gudanar da zabukan ne a mazabu 1,491 da ke kananan hukumomi 774 da ke jimillar rumufunan zabe 176, 846.

’Yan Najeriya ne za su yi alkalanci a zaben mai mutum miliyan 95.5 da suka yanki katin zabe, wadanda akasarinsu matasa ne, masu shekara 18 zuwa 35, ko da yake kawo yanzu babu alkaluman adadin wadanda suka karbi katin zabensu.

Manyan jam’iyyu

Jam’iyyar APC mai mulki kasar tun 2015 na neman ci gaba da jan ragamar kasar na karin shekara hudu, a yayin da babbar jam’iyyar adawa ta PDP wadda ta mulki kasar na tsawon shekara 16, bayan dawowar tsarin dimokuradiyya daga 1999 zuwa 2015 na neman sake dawowa.

Bugu da kari, zaben na bana ya zo da sabon abu, inda ake da wasu kananan jam’iyyu biyu, LP da kuma NNPP da suke tashe da kuma samun magoya baya a wannan karon.

Batun shekarun ’yan takara dai ya dade yana tayar da kura a zabukan Najeriya, inda gabanin zaben 2019 Gwamnatin Tarayya ta yi dokar rage yawan shekarun tsayawa takara domin a dama da matasan kasa.

APC ta tsayar da tsohon Gwamnan Jihar Legas (1999-2007) kuma Uban Jam’iyyar na kasa, Asiwaju Bol Ahmed Tinubu, a yayin da PDP ta tsayar da Fsohon Mataimkin Shugaban Kasa Atiku Abubakar (1999-2007).

Karo na biyar ke nan Atiku yake neman zama shugaban kasa a yayin da Tinubu ke tutiyar cewa shi ya fi kowa dacewa ya mulki kasar a wannan karon bayan Buhari.

A nasa bangaren, yana takama da matasa, kasancewarsa mai karancin shekaru a cikin manyan ’yan takara.

Hakazalika, dan takarar NNPP, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso yana takama da kasancewa mai jini a jika yana kuma bugun gaba da irin ayyukan da ya yi a lokacin da yake Gwamnan Jihar Kano, ministan tsaro.

Yana kuma takama da farin jininsa, inda a 2015 ya zama na biyu a zaben dan takarar shugaban kasa na APC, wanda Buhari ya lashe.

Zaben na zuwa ne a yayin da Najeriya ke tsaka da fama da matsalar tattalin arziki bayan Gwamnatin APC ta yi sauyin takardun Naira 200, N500 da kuma N1,000.

Sauran abubuwan da ke ci wa kasar tuwo a kwarya sun hada da sha’anin tsaro, tsadar man fetur da rashin ingantattun ababen more rayuwa da suka hada da bangaren ilimi, lafiya, sufuri, da kuma uwa uba makamshi da wutar lantarki.

Friday, 6 January 2023

Yan sanda a jihar Kano sun kame 'yan daban siyasa fiye da 60

‘Yan sanda a jihar Kano sun sanar da kame ‘yan daban siyasa akalla 61 yayin wani sumame da suka kaddamar a kokarin kakkabe barazanar rashin tsaro da aikata laifukan da ke ci gaba da tsananta a sassan jihar.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Mr Mamman Dauda da ke bayyana hakan a wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Abdullahi Haruna ya rabawa manema labarai, ya ce matakin kame ‘yan daban umarni ne daga babban sufeton ‘yan sandan kasar Usman Alkali-Baba.

A cewar sanarwar galibin kamen an yi shi ne yayin gangamin siyasar da ke ci gaba da gudana a sassan jihar, a wani yunkuri na dakile barazanar ‘yan daban dai dai lokacin da babban zaben Najeriya ke ci gaba da karatowa.

A Sanarwar da gidan Rediyon Faransa (RFI) ya wallafa a shafinsa, ta bayyana cewa ta hanyar tsaftace gari daga barazanar ‘yan daban siyasa ne kadai za a iya samun damar tafiyar da harkokin zaben da ke tunakarowa a wata mai zuwa.

Rundunar ‘yan sandan ta jihar Kano ta ce ta gudanar da sumame ranar 4 ga watan da muke na Janairu yayin wani gangamin siyasa da ya gudana a filin wasa na Sani Abacha da ke jihar.

Sanarwar ‘yan sandan ta ce ta kame tarin makamai daga hannun ‘yan daban da suka kunshi wukake 33 da adda guda 8 da almakashi 4 baya ga kunshin tabar wiwi 117.

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

FG Urges KOICA, FAO to Align Agricultural Intervention with Nigeria’s Development Priorities, Ward-Based Strategy

The Federal Government has called for stronger alignment between development partners’ interventions and Nigeria’s national deve...