Search This Blog
Saturday, 18 November 2023
Yanzu-yanzu: Gwamnan Kano Abba Kabir Zai Daukaka Kara Zuwa Kotun Koli
Welcome to Alheekmah News Alheekmah News is a Nigerian digital news platform committed to delivering timely, accurate, and credible news to readers across Nigeria and beyond. We provide comprehensive coverage of national affairs, politics, governance, Hajj and Umrah, religion, education, business, security, health, and other issues that shape our society. Our mission is to inform, educate, and inspire through responsible journalism founded on accuracy, fairness, and integrity. We strive to provide factual reporting while promoting public awareness and constructive engagement. At Alheekmah News, we believe that reliable information empowers individuals and strengthens communities. We are dedicated to bringing you breaking news, in-depth reports, exclusive interviews, and insightful analysis you can trust. Stay informed. Stay connected. Stay ahead with Alheekmah News.
Tuesday, 27 December 2022
Almajiran Abduljabbar Kabara sun ce zasu daukaka kara
Almajiran Sheikh Abduljabbar Nasiru Kabara da Kotun Musulunci ta yanke wa hukuncin rataya kan laifin batanci ga Manzon Allah (SAW) suna shirin daukaka kara.
Almajiran fitaccen malamin mazaunin Kano, karkashin inuwar A’shabul Kahfi Warraqeem, Reshen Jihar Bauchi, sun yi zargin siyasa a hukuncin da aka yanke masa, saboda a cewarsu, malamnin nasu ya caccaki Gwamnan Jihar Kano, kan zargin almundahana.
“Ba mu gamsu da hukuncin ba saboda muna zargin akwai hannun Gwamnan Jihar Kano da wasu malamai da suka dade suna zaman doya da manja da shi (Abduljabbar), wadanda suka yi masa kagen yin batanci domin su kawar da shi daga doron kasa ta hanyar amfani da karfin kotu,” in ji mai magana da yawunsu, Abdullahi Musa a Bauchi.
Ya shaida wa manema labarai cewa, “Zargin batancin ba komai ba ne illa neman goga masa kashin kaji daga magauta, ciki har da Ganduje da wasu malamai da ke ganin daukakar da Abduljabbar ke samu a matsayin baraza a gare su.“Shi ya sa suka jefe shi da yin batanci domin su ja masa bakin jini saboda su samu dalilin kawar da shi.
“Saboda haka mun yanke shawarar zuwa kotu ta gaba mu nemi ta soke wannan mugun hukuncin, tare da tabbatar masa da ’yancinsa, musamman na yin addini da bayyana ra’ayi kamar yadda kunin tsarin mulkin Najeriya ya tanadar.
“Muna rokon Hukumar Kare ’Yancin Dan Adam ta Kasa, kungiyar Amnesty International, da sauran kungiyoyin kare hakkin dan Adam na cikin gida da na kasa da kasa, da kuma lauyoyin kare hakkin dan Adam irin su Femi Falana, da mai rajin kare hakkin dan Adam, Ahmad Isa — Ordinary President, da sauransu, da su fito su yaki wannan zalunci da taron dangi da aka yi wa jagoranmu na addini, Sheikh Abduljabbar, ta hanyar sama mishi agajin shari’a,” in ji Abdullahi Musa.
Ya yi zargin hadin bakin Gwamnatin Jihar Kano da wasu malaman da ba sa shiri da Abduljabbar wajen hallaka shi a kan laifin da bai amsa ba.
“Mun lura cewa wadansu daga cikin wadanda suka yi taron dangi domin kawar da Abduljabbar, su ke aikata batanci a karatuttukansu, ba tare da wani tarnaki ba.”
(AMINIYA)
Welcome to Alheekmah News Alheekmah News is a Nigerian digital news platform committed to delivering timely, accurate, and credible news to readers across Nigeria and beyond. We provide comprehensive coverage of national affairs, politics, governance, Hajj and Umrah, religion, education, business, security, health, and other issues that shape our society. Our mission is to inform, educate, and inspire through responsible journalism founded on accuracy, fairness, and integrity. We strive to provide factual reporting while promoting public awareness and constructive engagement. At Alheekmah News, we believe that reliable information empowers individuals and strengthens communities. We are dedicated to bringing you breaking news, in-depth reports, exclusive interviews, and insightful analysis you can trust. Stay informed. Stay connected. Stay ahead with Alheekmah News.
Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa
FG Urges KOICA, FAO to Align Agricultural Intervention with Nigeria’s Development Priorities, Ward-Based Strategy
The Federal Government has called for stronger alignment between development partners’ interventions and Nigeria’s national deve...
-
Gwamnan Babban Bankin Najeriya, Godwin Emefiele, ya ce Bankuna za su ci gaba da karbar tsoffin takardun kudi na Naira ko da baya...
-
Matar hamshakin dan kasuwa na Kano, Alhaji Aminu Alasan Dantata, Hajiya Rabi ta rasu Jaridar SOLACEBASE ta rawaito cewa, Hajiya ...
-
Zababben Gwamnan Jihar Kano Ya Sanar Da Kwamitin Karbar Mulki …… Dr. Baffa Bichi, Abdullahi Musa ya nada a matsayin Shugaba da Sakatare Baya...
