Posts

Showing posts with the label Nasiru Yusuf Gawuna

GAME DA SHARI’AR ZABEN JIHAR KANO: ABINDA YAI SAURA - Saidu Ahmad Dukawa

Image
Bismillahir Rahmanir Raheem Yau, Juma’a 12/1/2024, Allah ya kawo karshen dakon da aka sha wajen sanin wanene halartaccen Gwamna a Jihar Kano.  Ina zaton an dade al’umar Kano, da wadanda suka damu da halin da Kano take ciki a fadin Duniya, ba su shiga zulumi (tension) da fargaba (anxiety) kamar a wadannan watannin da aka gudanar da shari’u a mataki daban daban ba. Alhamdu lillah, Allah ya nunawa wadanda suke raye karshen dambarwar. Muna fatan kada Allah ya sake jarrabar Bayinsa da irin wannan halin. Yanzu abu uku ne suka saurar mana. Abu na farko shine kowa ya karbi hukuncin da zuciya daya. Wandanda suka yi nasara kada su dauka iyawarsu ce, wadanda ba su samu yadda suke so ba kada su dauka wani ne ya janyo musu. Wannan ne zai taimaka wajen kaucewa irin wannan jarrabawar anan gaba. Abu na biyu shine gawmanati da dukufa wajen samar da shugabanci nagari, ba tare da tunanin ramuwar gayya ba, ko wariya, ko wani abu mai kama da haka. Ya kamata a sani cewar gwargwadon yadda al’umma

Kotun Koli Ta Tsayar Da Ranar Da Za Ta Saurari Karar Zaben Gwamnan Kano

Image
Kotun koli ta sanya ranar Alhamis 21 ga watan Disamba domin cigaba da sauraron karar zaben gwamnan Kano tsakanin gwamna Abba Kabiru Yusuf na jam’iyyar New Nigeria Peoples Party NNPP da Nasiru Yusuf Gawuna na jam’iyyar APC.  KANO FOCUS ta rawaito cewa a cikin sanarwar da magatakardar kotun daukaka kara ta aikewa lauyoyin bangarorin biyu, kotun za ta saurari karar da NNPP ta shigar da kararrakin wasu jam’iyyu.  Gwamna Yusuf na kalubalantar hukuncin da wasu bangarori uku na kotun daukaka kara suka yanke wanda ya soke nasarar da ya samu tare da tabbatar da hukuncin da kotun sauraren kararrakin zabe ta yanke. Kotun sauraron kararrakin zabe karkashin jagorancin mai shari’a Osedebay ta bayyana dan takarar jam’iyyar APC, Nasiru Gawuna a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan jihar Kano a watan Maris.  Kotun daukaka kara ta yi watsi da karar da Gwamna Yusuf ya shigar bisa matsayinsa na zama mamba a jam’iyyarsa sannan ta zargi kotun da yin watsi da hujjar da ta yanke. Kotun ta kori Gw

Labari Da Dumiduminsa: Kotun Daukaka Kara Ta Kebe Hukuncin Da Za Ta Yi Kan Zaben Gwamnan Kano

Image
Idan dai za a iya tunawa,Dan takarar jam’iyyar  APC Nasiru Yusuf Gawuna, ya lashe zaben.  Kwamitin mutum uku na kotun karkashin mai shari’a Oluyemi Akintan Osadebay ya kori Yusuf a ranar 20 ga watan Satumba, 2023, bayan ya zare kuri’u 165,663.  Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta sanar da cewa Yusuf ne ya lashe zaben ranar 18 ga Maris, 2023, inda ta ce ya samu kuri’u 1,019,602 inda ya doke Gawuna wanda ya samu kuri’u 890,705. Sai dai jam’iyyar APC ta tunkari Kotun, bisa zargin tafka magudin zabe.  Kotun da ta amince da APC ta soke zaben Yusuf, inda ta kara da cewa sama da katunan zabe 160,000 “ INEC ba ta sanya hannu ko tambari ba. An rage kuri’un Yusuf zuwa 853,939 yayin da kuri’u 890,705 Ganuwa bai shafa ba.  Daga nan sai gwamnan ya shigar da kara a gaban kotun daukaka kara. Jam’iyyun APC da INEC da NNPP su ma sun shigar da kara a gaban kotun. A ranar Litinin, babban lauyan gwamnan, Wole Olanipekun SAN (wanda shi ne babban lauyan Tinubu a PEPC), ya bukaci kotun