Posts

Showing posts with the label Daukar aiki

NAHCON Ta Gargadi Jama'a Kan Yada Labaran Karya Na Daukar Aiki

Image
Wannan sanarwa ce daga hukumar alhazai ta kasa (NAHCON) na fadakar da alhazai musulmi masu niyyar zuwa aikin Hajji, da masu neman aikin likita ko duk wani mai sha’awa game da yadda ake yada sakonnin bogi dangane da daukar aiki a tawagar likitocin NAHCON.   A sanarwar da mataimakiyar daraktar harkokin yada labarai da dab'i ta hukumar, Fatima Sanda Usara ta sanyawa hannu, tace labari ya riski hukumar cewa ana yada bayanan karya ga daidaikun mutane da ke ikirarin daukar ma’aikata na dundundun a NAHCON ko a matsayin mambobin tawagar likitoci da sauran mambobin kwamitin aikin Hajji. A halin yanzu NAHCON ba ta daukar ma’aikata na dundundun , ko wasu ma’aikata a kan haka da duk wani sakon da ke nuni da cewa karya ne.   Sahihan tsarin aikace-aikacen tawagar likitocin Hajji ana gudanar da shi ne ta hanyar shafin hukumar na yanar gizo kuma har yanzu tana ci gaba. Hukumar ta bukaci jama’a da su yi watsi da duk wata hanyar sadarwa ta daban, su dogara ne kawai da bayanai daga tashar

Gwamnan Kano ya bayar da kyautar Miliyan daya, kujerar Haji da kuma daukar aiki na dundundun ga ma'aikacin wucin gadin hukumar alhazai

Image
Dayyabu Bala Gezawa (Dan Gezawa) shi ne ma'aikacin wucin gadin hukumar alhazai ta Kano da ya tsinci dala dubu 16 kudin guzurin maniyyatan wata kararmar hukuma gaba daya kuma ya damkasu ga Darakta Janar na hukumar  Gwamnan Kano ya bayar da kyautar Miliyan daya, kujerar Hajj da kuma daukar aiki na dundundun ga ma'aikacin wucin gadin hukumar alhazai da ya mayar da naira miliyan 16 ya guzurin alhazai da ya tsinta Alhaji Abba Kabir Yusuf ya bayar da wannnan kyauta ne a ranar Litinin, yayin taron mika masa rahoton aikin Hajin 2023 daga hannun Hukumar kula da Jin dadin Alhazai ta Jahar Kano Gwamnan wanda ya bayyana farin cikinsa bisa tarin nasarorin da sabon shugabancin hukumar ya samar a yayin aikin hajin da ya gabata, duk Kuwa da cewar sun tarar da tarin matsaloli dangane da shirin aikin Hajin Yace gwamnatinsa na bayar da cikakkiyar kulawa ta dukkanin lamarin da ya shafi Harkokin addinin islama, musammam ma aikin haji da ya kasance daya daga Cikin shikashikan musulinci