Posts

Showing posts with the label Barka da sallah

Gwamna Abba Kabir Yusuf Ya Taya Sanata Kwankwaso Murnar Sallah, Tare Da .Yabawa Da Kyawawan Halayensa Na Shugabanci

Image
Gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya yiwa dan takarar shugaban kasa a jam'iyyarsa ta NNPP Injiniya Rabi'u Kwankwaso barka da Sallah a lokacin da ya hada kai da dubban magoya bayan Kwankwasiyya domin yi wa shugaban kasa mubayi'a a wani bangare na gudanar da bukukuwan Sallah. A sanarwar da mai rikon mukamin babban sakataren yada labaran gwaman, Hisham Habib ya sanyawa hannu, Ta Ce, Gwamna Yusuf ya ce shugaban da ya yi gwamnan jihar har sau biyu ya na yi wa mutane da yawa jagoranci kuma ya kasance abin koyi a jihar da kuma yankin Arewa. A lokacin da yake jawabi a wajen bikin da magoya bayansa suka shirya, gwamnan ya ce shugaban wanda yay Gwamna har sau biyu, ya jagoranci ci gaba rayuwar mutane da dama Ya godewa Sanata Kwankwaso bisa nasiharsa ta uba da kuma ka’idojinsa na karfafa mutane. Mawaka da dama ne suka baje kolin fasaharsu a wajen taron tunawa da ranar a gidan Sanata Kwankwaso tare da dan takarar mataimakin shugaban kasa na jam'iyyar NNPP. B

Gwamnan Kano ya taya al'ummar Kano murnar bukukuwan Sallah

Image
Gwamna Abba Kabir Yusuf ya taya al'ummar Kano murnar bikin Sallah. Gwamnan a cikin sakon da mai rikon mukamin babban sakataren yada labaransa, Hisham Habib ya sanyawa hannu, Ta Ce Gwamnan ya bukaci al’ummar musulmi da su daure su kasance masu taimakon juna. Gwamna Kabir ya yi wa alhazan kasa mai tsarki addu’ar Allah ya kai su gida lafiya. Ya kuma jaddada aniyar gwamnatinsa na tallafawa harkokin kiwon lafiya, ilimi, kare muhalli da kuma noma. Ya ce gwamnati za ta ci gaba da jaddada jin dadin ‘yan kasa Mai Martaba Sarkin Kano Alh Aminu Ado wanda ya tarbi Gwamna Abba Kabir a Gidan Shetima wanda ya bukaci al’ummar Kano da su fito a kidaya su a kidayar jama’a na gaba domin tabbatar da matsayin Kano a matsayin jiha mafi yawan al’umma.