Posts

Showing posts with the label Kashim Shettima

Sababbin Shugabannin NAHCON Sun Kama Aikinsu Bayan Da Mataimakin Shugaban Kasa Ya Kaddamar Da Su

Image
A ranar Laraba ne Hukumar kula da aikin Haji ta kasa ta shaida wani muhimmin lamari, yayin da mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima ya kaddamar da shugabancinta a karo na biyar karkashin jagorancin Malam Jalal Ahmed Arabi Taron kaddamarwar ya faru ne a ofishin mataimakin shugaban kasar, inda bayan nan ne shugabannin suka zarce zuwa hukumar A sanarwar da mataimakiyar daraktar harkokin hulda da jama'a da dab'i ta hukumar, Fatima Sanda Usara ta sanyawa hannu, tace a yayin gudanar da taro shugabannin hukumar ta NAHCON, shugaban hukumar, Malam Jalal Arabi, yayi maraba da dukkanin wakilaninda ya bayyana kwarin gwiwarsa ga cancantarsu, inda ya kuma basu tabbacin samun hakan daga bangaren ma'aikatan hukumar kamar yadda shi ma ya samu yayin da ya kama aiki a watanni hudun da suka gabata. Daga nan sai yayi kira ga ma'aikatan hukumar su bayar da makamancin hadin kan sababbin shugabannin nasu don cimma manufar hukumar Sababbin shugabannin da aka nada sun

Mataimakin Shugaban Kasa Ya Kaddamar Da Sababbin Shugabannin NAHCON

Image
Mataimakin shugaban kasa, Sanata Kashim Shettima ya kaddamar da sababbin Jami'an hukumar alhazai ta kasa (NAHCON) tare da yin kira ga da su bullo da sabbin abubuwa a harkokin aikin hajji a Najeriya.  A sanarwar da mai taimakawa Mataimakin Shugaban kasar kan harkokin yada labarai  Stanley Nkwocha ya sanyawa hannu, yace d a yake jawabi yayin kaddamar da sababbin 'yan hukumar a fadar shugaban kasa da ke Abuja ranar Laraba, mataimakin shugaban kasar ya bukaci mambobin su hada kai tare da kawo sabbin ra’ayoyi kan ayyukan hukumar. A cewar Sanata Shettima, yin aiki a hukumar NAHCON na da matukar muhimmanci ganin cewa “Hajji na daya daga cikin rukunan Musulunci guda biyar”. “A gare ku, bayan nadaku da aka yi, abu ne mai nasara domin idan kun yi wa alhazai hidima da kyau, Allah Ta’ala zai biya ku a ranar lahira. Don haka, aikinku ya fi kusanci da na addini fiye da aikin gudanarwa,” in ji Shettima.  Da yake karin haske game da batun kafa sabuwar hukumar da aikin d

Gwamna Yusuf ya yabawa Tinubu da Shettima bisa rashin yin katsalandan a hukuncin Kotun Koli

Image
Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya yabawa shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu da mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima a matsayin jajirtattun jagororin da suka bijirewa gagarumin matsin lamba na yin tasiri ga hukuncin kotun koli kan zaben gwamna. A sanarwar da Darakta Janar kan kafafen yada labarai da sadarwa na Gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa ya fitar, yace Gwamna Yusuf ya bayyana jin dadinsa da yadda Tinubu da Shettima suka jajirce wajen fuskantar matsin lamba na yin katsalandan ga hukuncin kotun kolin, duk kuwa da kakkausar murya daga bangarori daban-daban. Dangane da yunkurin da ake zargin tsohon Gwamna Abdullahi Ganduje na yin amfani da fadar shugaban kasa wajen murde hukuncin da kotun koli ta yanke na goyon bayan dan takarar sa na gwamna a jam’iyyar APC, Nasiru Yusuf Gawuna, Gwamnan ya bayyana rashin tsoma bakin da Tinubu da Shettima suka yi a matsayin wata shaida da ke nuna cewa Najeriya na da kyakkyawan tsarin dimokwaradiyya. Bugu da kari, Yusuf ya mika goron

Mataimakin Shugaban Kasa Yayi Kira Ga Saudia Da Ta Bar NAHCON Ta Ci Gaba Da Ciyar Da Alhazai

Image
Mataimakin shugaban kasa, Sanata Kashim Shetima ya bukaci hukumar alhazai ta Najeriya NAHCON da ta yi kira ga mahukuntan kasar Saudiyya da su janye matakin da suka dauka na samar da abinci ga alhazan Najeriya a cikin kwanaki 5 na aikin a kasar Saudiyya. A sanarwar da Mataimakin daraktan yada labarai na Hukumar, Mousa Ubandawaki ya sanyawa hannu, Mataimakin shugaban kasar ya bayyana haka ne a lokacin da shugabannin gudanarwar hukumar suka gana da shi domin bayyana masa sakamakon aikin hajjin shekarar 2023 a fadar shugaban kasa da ke Abuja a yau. Ya ce bisa la'akari da sauyin yanayi da aka samu a duniya ya zama wajibi Masarautar ta baiwa hukumar jin dadin Alhazai ta Jiha damar ciyar da Alhazanta domin kaucewa rashin jin dadi na jiki ko na lafiya a lokacin aikin Hajji. "Yana da mahimmanci ga Masarautar ta sake nazarin tsarin jin daÉ—inta a cikin masha'ir tare da sauyin yanayi da sauyin yanayi. Da yawa daga cikin Alhazai idan ba a ciyar da su da kayan abinci na gida