Posts

Showing posts with the label Wike

Wike Yayi Alkawarin Kammala Gyaran Masallacin Kasa Da Cibiyar Yada Addinin Kirista Kan Lokaci

Image
Mista Nyesom Wike, Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), ya yi alkawarin tabbatar da kammala aikin gyaran Masallacin kasa da cibiyar Kiristoci ta kasa da ke Abuja kan lokaci. Wike ya ba da wannan tabbacin ne bayan ya duba aikin gyaran manyan gine-ginen kasa guda biyu a Abuja ranar Alhamis. Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya, NAN, ta tuno da cewa, shugabannin Masallacin kasa da Cibiyar Ibadar Kirista sun ziyarci Wike tare da rokon a kammala ayyukan gyara. Wike, bayan ya tabbatar musu da cikakken goyon bayansa, ya yi alkawarin ziyartar cibiyoyin biyu domin ganin al'amura da kansa kafin ya yanke shawara kan mataki na gaba. Ministan ya shaidawa manema labarai jim kadan bayan kammala rangadin aikin da aka gudanar a Masallacin kasa saboda karin aikin da ya kamata a yi. Ya nuna jin dadinsa da abin da aka yi ya zuwa yanzu, ya kuma ba da izinin a saki kudi ga dan kwangilar domin samun damar kammala aikin. A cibiyar kiristoci ta kasa, Wike ya ce zai duba kudin aikin gyaran ka

Kada Wanda Ya Kafa Allunan Taya Ni Murnar Zama Minista – Wike

Image
  Ministan Abuja, Nyesom Wike, ya hana karkafa duk wasu allunan talla da nufin taya shi murnar zama Minista. A cikin wata sanarwa da Daraktan Yada Labarai na ma’aikatar, Anthony Ogunleye, Wike ya ce ya yanke shawarar daukar matakin ne saboda nuna kishin kasa da kuma mayar da hankali wajen aikin da Tinubu ya sa shi. Sanarwar ta ce Ministan ya gode da fatan alherin, amma ya bukaci a dakatar da amfani da irin wadannan allunan tallan. Wike ya ce babban burinsa shi ne ya bunkasa Abuja ta yadda mazauna cikinta za su ji dadin zamanta a zamanin mulkinsa. Ya kuma ce ya yana matukar girmamawa da kuma mutunta bukatun mazauna birnin tare da jajircewa wajen ganin ya biya musu su. AMINIYA

Sunayen Unguwannin Da Wike Zai Yi Rusau A Abuja

Image
Ministan Abuja, Nyesom Wike ya amince a rusa gine-gine sama da 6,000 a yankunan Garki da Jabi da wasu unguwanni 28 da suka saÉ“a da tsarin birnin tarayyan ba. Hukumar kula da birnin tarayyar (FCTA) ta fitar da jerin sunayen unguwannin, inda ta bayyana cewa gine-ginen ta riga aka sanya wa alama ne rusau din zai shafa, a shirin gwamnati na kawar da gine-ginen da aka yi ba bisa Æ™a’ida ba a birnin. Ga jerin unguwannin da abin zai shafa: Apo Mechanic Village Byanzhin. Dawaki. Dai Dai. Durumi. Dutse. Garki. Garki Village. Gishiri. Gwagwalada. Idu. Jabi. Kauyen Kado. Karmo. Karshi. Karu. Katampe. Kauyen Ketti. Kpaduma. Kabusa. Kauyen Kpana. Kubwa. Lokogoma. Lugbe. Mabushi. Mpape. Nyanya. Piya Kasa. Jikwoyi Galadima Tun ranar Litinin da aka rantsar da tsohon gwamnan na jihar Ribas a matsayin Minista, ya sha alwashin dawo da birnin kan ainihin taswirarsa, ruguza gine-ginen aka yi ba bisa tsaru ba, da kuma kawo karshen badaÆ™alar filaye a babban birnin. Wike wanda ya ce ya zaga birnin

Wike Ya Ziyarci Ganduje A Ofishin APC

Image
Tsohon Gwamnan Jihar Ribas, wanda aka tantance domin zama minista, Nyeson Wike, ya ziyarci Shugaban Jam’iyyar APC mai mulki, Abdullahi Umar Ganduje a ofishin jam’iyyar. Ganduja ya karbi bakuncin Wike a ofishinsa ne yayin da ake rade-radin yana shirin sauya sheka daga jam’iyyarsa ta PDP zuwa APC. Sai dai ya sha musanta shirin komawa jam’iyyar mai mulki. Wike wanda Shugaba Bola Ahmed Tinubu na APC ya mika sunansa a cikin jerin ministocin da zai nada ya fito karara ya yaki dan takarar shugaban kasan PDP a zaben 2023, Atiku Abubakar. A yayin wani bikin da aka shirya masa bayan ya mika mulki ga zababben gwaman jiharsa, Simi Fubara, an ji gwamnan na rokon Wike kada ya yi watsi da shi idan ya dawo jam’iyya mai mulki. Rade-radin komawar Wike jam’iyyar APC sun kara karfi ne bayan Shugaba Tinubu ya mika sunansa a jerin ministocinsa. Shugabannin PDP dai sun bayyana rashin jin dadinsu, tare da kurarin daukar mataki a kan tsohon gwamnan na Ribas. (AMINIYA)

Wike Ya Bawa Ma'aikata Hutu Domin Tarbar Tinibu A Ribas

Image
Gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Wike, ya ayyana Larabar nan a matsayin ranar hutu domin tarbar zaben shugaban kasa, Bola Tinudu a ziyarar da zai kai jihar. Wike, wanda dan jam’iyyar adawa ta PDP ne da ke takun saka da dan takarar shguaban kasa na jam’iyyarsa, Atiku Abubakar, ya ce yayin ziyarar aikin ta kwana biyu, Tinubu zai kaddamar da gadar sama da ginin zamani da ya gina wa kottun Majistare a birnin Fatakwal, hedikwatar jihar. DAGA LARABA: Yadda Iyaye Ke Kashewa ’Ya’yansu Aure A Arewa La Liga: Barcelona ta yi wa Osasuna gida da waje a bana Wike wanda ya juya wa Atiku baya a zaben da Tinubu ya lashe, ya ce, “Ina kira ga daukacin al’ummar jihar su fito kwansu da kwarkwato su yi wa zabebban shugaban kasarmu kuma abin alfaharimu, Mai Girma Sanata Bola Ahmed Tinubu gagarumar tarba, tare da bayyana abin da aka san su da shi na karamci yayin a ziyarar da zai kaddamar da muhimman ayyukan ci gaba da za su zama tarihi. “Saboda haka na ayyana ranar Laraba, 3 ga Mayu 2023, a matsayin r

Almundahanar N96bn: Wike Ya Sake Maka Amaechi A Kotu

Image
Gwamnatin Ribas ta shigar da sabuwar kara kan tsohon gwamnan jihar kuma tsohon Ministan Sufuri, Rotimi Amaechi, kan zargin yin sama da fadi da Naira biliyan 96. An maka Amaechi tare da Tonye Cole, dan takarar gwamna na Jam’iyyar APC a jihar bisa zargin sayar da kadarorin jihar. HOTUNA: Masaukin Ronaldo da burwarsa a Saudiyya DAGA LARABA: Dalilin Da Maza Ke Tsoron Auren Mata ’Yan Boko  Zacchaeus Adangor, babban lauyan Gwamnatin Jihar Ribas, ya tabbatar da shigar da karar. Nyesom Wike, gwamnan Ribas, ya kafa wani kwamitin mutum bakwai don bincikar Amaechi kan zargin cirar Naira biliyan 96 daga asusun gwamnatin jihar a lokacin da yake gwamna. Kwamitin ya kuma binciki batutuwan da suka shafi sayar da kadarorin da tsohon gwamnan ya yi. Kwamitin ya gabatar da rahotonsa a 2015 kan binciken, amma Amaechi ya musanta aikata laifin da ake tuhumar sa. A ranar 27 ga Mayu, 2022, wata babbar kotu ta yi watsi da bukatar Amaechi na hana kwamitin gudanar da bincike a kansa. Sakamakon haka ne