Posts

Showing posts with the label Tsaro

Mun himmatu wajen kare rayuka da dukiyoyin al’ummar Kano – Gwamna Abba Kabir Yusuf

Image
Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya bayyana kudurinsa na kare rayuka da dukiyoyin al’ummar jihar. Gwamna Yusuf ya bayyana haka ne a lokacin da ya karbi bakuncin shugabannin tsaron Kano a wani taron buda baki a gidan gwamnati da ke Kano. Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa ya fitar a ranar Litinin. A cikin sanarwar, gwamnan ya yabawa jami’an tsaro bisa rawar da suke takawa wajen tabbatar da tsaro da walwalar ‘yan kasa, tare da sanin irin gudunmawar da suke bayarwa. Gwamna Yusuf ya nanata jajircewar gwamnatin sa wajen karfafa tsarin tsaro domin isar da muhimman ayyukan da gwamnati da al’ummar Kano ke sa ran yadda ya kamata. Ya kuma bayyana cewa gwamnatin sa ta fara siyan kayan abinci domin rabawa, inda jami’an tsaro na cikin wadanda suka ci gajiyar shirin. Bugu da kari, ya yabawa gwamnatin tarayya musamman shugaban kasa Ahmed Bola Tinubu bisa amincewa da rabon kayan abinci da za a raba ga marasa galihu a

Dokar Najeriya Ta Haramta Biyan Kuɗin Fansa — Ministan Tsaro

Image
  Ministan Tsaro Mohammed Badaru Abubakar ya ce Dokar Najeriya ta haramta biyan masu garkuwa da mutane kuɗin fansa. Ministan wanda ya bayyana haka ne a taron Majalisar Zartarwa da aka gudanar a wannan Larabar, ya ce lokaci ya yi da za a daina biyan kuɗin fansar saboda haka ne kaɗai hanyar kawo ƙarshen masu garkuwa da mutane. Ya ce Shugaban Kasa ya bai wa dukkan hafsoshin tsaro goyon bayan da ya kamata don ganin an kawo karshen garkuwa da mutane da ya yi ƙamari a ƙasar. Tsohon Gwamnan na Jihar Jigawa, ya ce kasancewar dokar Najeriya ta haramta bayar da kuɗin fansa ya sanya bai kamata mutane su riƙa biyan kuɗin ba saboda ba shi da amfani. “Babbar matsalar ita ce yadda mutane ke fitowa a kafafen yaɗa labarai suna neman taimako, har a zo a tara musu kuɗi domin biyan fansa. Hakan bai dace ba. “Idan muka daina biyan kuɗin fansa, sannu a hankali ayyukan masu garkuwa da mutane zai zama tarihi,” in ji Badaru. Dangane da yadda rashin tsaro ke ƙara ta’azzara a Abuja, babban birnin ƙasar da kuma g

Zamu mayar da hankali kan zuba jari a tsarinmu na tattalin arziki - Badaru

Image
Ministan tsaro, Alhaji Mohammed Badaru, ya bayyana a ranar Laraba cewa, gwamnatin tarayya ta mayar da hankali wajen sanya hannun jari wajen sabunta kayan aikin soja domin tabbatar da tsaron lafiyar ‘yan kasa da na kasashen waje. Badaru ya bayyana haka ne a wata sanarwa da Misis Victoria Agba-Attah, Darakta, hulda da manema labarai na ma’aikatar tsaro ta fitar, a cikin sakon fatan alheri da ya gabatar a taron kungiyar lauyoyin Najeriya na shekara ta 2023. Taron ya kasance takensa: "Sarrafa Dabarun Tsare-tsare don Tsaro da Ci Gaba". Ya ce yayin da ake saka hannun jari a zamanantar da kayan aikin soji, gwamnati za ta kuma mai da hankali kan tattalin arzikin shudi, wuraren da ba sa tuka mutum da kuma sauyin yanayi. Badaru wanda ya samu wakilcin babban sakatare a ma’aikatar, Dr Ibrahim Kana, ya ce gwamnatin Najeriya ta hannun ma’aikatar ta kashe kudade da dama wajen samar da kayan aiki da hanyoyin magance matsalar satar fasaha. Ya kara da cewa hukumar kula da harkokin

Buhari Ya Je Wurin Fareti Sanye Da Kakin Soja

Image
Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya fito sanye da kakin sojoji a dandalin Eagles Square inda sojoji ke fareti a safiyar Alhamis.  Buhari ya isa dandalin, inda sojoji 1,000 ke gabatar da fareti inda ya samu rakiyar Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Kasa, Ibrahim Gambari. Babban Hafsan Taron Najeriya, Janar Lukcy Irabor da Babban Hafsan Sojin Kasa, Laftanar-Janar Faruk Yahaya da kuma Shugaban ’Yan Sandan Najeriya, Usman Baba na daga cikin mahalarta faretin. Sauran hafsoshin tsaro da Shugaban Majalisar Dattawa, Ahmad Lawan na daga cikin mahalarta faretin sojojin. AMINIYA

Buhari Zai Sayo Motocin Sulke 400 Don Tsaron Su Abuja

Image
Shugaba Buhari ya amince da sayo motocin sulke guda 400 don amfani da su wajen tabbatar da tsaro a babban birnin tarayya da jihohin Nasarawa da kuma Neja. Sabon Kwamandan Rundunar Tsar Birgediya, Manjo-Janar Mohammed Usman ne ya bayyana hakan a ranar Laraba a jawabin godiyarsa a bikin nada masa anininsa bayan karin girma da ya samu. Shugaban kasa tare da Babban Hafsan Sojin Kasa, Laftanar-Janar Faruk Yahaya da uwargidan kwamandan, Dokta Rekiya Usman, ne suka nada masa aninin. Jim kadan bayan kammala bikin a Fadar Shugaban Kasa da ke Abuja, shugaban kasa ya bayyana shi a matsayin fitaccen jami’in da yake yi wa kasa hidima. Ya yaba wa Janar Usman bisa jajircewarsa da rikon amana da hakuri da kuma kwazo. Buhari, a cikin wata sanarwa da hadiminsa, Garba Shehu ya fitar, ya yaba wa iyalan kwamandan bisa hakurin da suka yi na jure kalubalen da ya fuskanta wajen gudanar da aikinsa. A nasa jawabin, Manjo-Janar Usman, ya gode wa shugaban kasa bisa irin gagarumin goyon bayan da ya bai wa Rundunar