Search This Blog

Showing posts with label Kebbi. Show all posts
Showing posts with label Kebbi. Show all posts

Wednesday, 6 March 2024

Gwamnatin Kebbi Za Ta Raba Man Fetur Kyauta Ga Manoma

Gwamnatin Kebbi ta bullo da shiri na musamman domin raba man fetur kyauta ga manoman rani da nufin saukaka musu yin wahalar noma a jihar.

Kwamishinan Noma na jihar, Shehu Mu’azu ya ce gwamnatin ta samar da haujin noma, inda aka farrfado da aikin noma domin jihar ta cigaba da rike kambunta a bangaren noman shinkafa a Nijeriya.


Saboda haka ne ta gina karamin wurin noma na zamani a kananan hukumomin Argungu da Fakai a garin Mahuta.

Wannnan a cewarsa, kari ne a kan tallafin noman rani da manoman shinkafa 30,000 da masu noma masara 7,500 da kuma masu noman rogo 2,000 suka samu daga gwamnatin.
(AMINIYA)


Tuesday, 7 November 2023

Hajjin 2024: Wajibi ne ga maniyyata su biya kuɗin Hajji nan da makonni 2- Shugaban hukumar alhazan Kebbi

Shugaban Hukumar Alhazai ta Jihar Kebbi, Alh Faruku Aliyu Yaro Enabo ya ja hankalin maniyyata a jihar da su hanzarta biyan kuɗin aikin Hajjin 2014 kafin nan da makonni biyu.

Jaridar Hajj Reporters Hausa, ta rawaito cewa Enabo ya bayyana hakan ne a wata ganawa da yayi a yau Talata da Shuwagabannin Ƙananan Hukumomi 21 dake Jahar Kebbi a Babban Birnin Jahar, Birnin Kebbi.

A cewar shi , biyan kudin kafin wa’adin makonni biyun shi zai tabbatar da cewa maniyyatan sun ɗauki ƙuduri na aikin Hajji.

Ya ƙara da cewa Hukumar Alhazzai ta Ƙasar Saudiyya itace ta zo da sabbin tsare-tsare ta yadda dukkanin maniyyata za su samu biza kamin wata uku da tashi zuwa Ƙasa mai tsarki.

Bayan gabatar da shuwagabannin Hukumar, Daraktoti da Masu Bawa Gwamna Shawara, Alh Faruku Enabo ya ja hankalinsu da su bawa maraɗa kunya, ya ƙara da cewa duk wanda aka samu da laifi babu makawa za’a ɗauki matakin ladabtarwa.

(Hajj Reporters Hausa)

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

FG Urges KOICA, FAO to Align Agricultural Intervention with Nigeria’s Development Priorities, Ward-Based Strategy

The Federal Government has called for stronger alignment between development partners’ interventions and Nigeria’s national deve...