Posts

Showing posts with the label Rabon kujeru

Yanzu-yanzu: NAHCON ta raba kujerun aikin Hajjin 2024 ga Jihohi, Abuja da bangaren rundunar soja

Image
Hukumar alhazai ta kasa NAHCON ta raba kujeru ga jihohi talatin da shida da babban birnin tarayya Abuja da kuma rundunonin soji domin gudanar da aikin Hajjin shekarar 2024. Takardar da Hajj Reporters suka gani a ranar Talata ta nuna cewa jihar Kaduna ce ta samu kaso mafi tsoka na kujeru 6004 sai jihar Kano da ta samu 5934. Sokoto ta samu 4996 a matsayi na uku yayin da jihohin Kebbi da Katsina suka samu 4752 da 4513. Duba cikakken jadawalin yadda rabon kujerun ya kasance (IHR)