Search This Blog

Showing posts with label Cin zabe. Show all posts
Showing posts with label Cin zabe. Show all posts

Wednesday, 29 March 2023

Yanzu-Yanzu: Nasiru Gawuna Ya Taya Abba Gida-gida Murnar Lashe zaɓen Gwamnan Kano

Mataimakin Gwamnan Jihar Kano Kuma wanda ya yiwa jam’iyyar APC takarar gwamnan jihar kano a jam’iyyar APC Dr. Nasiru Yusuf Gawuna ya ce ya karɓi Kaddarar faɗuwa zaɓe tare da taya Abba Kabiru Yusuf Murnar lashe zaɓen gwamnan Kano.

Nasiru Gawuna ya bayyana hakan ne cikin wani sakon murya da yayi bayani na tsawon mintuna biyu, wanda Sakataren yada labaran sa Hassan Musa Fagge ya aikowa kadaura24.


” Mun tsammaci Hukumar Zabe INEC zata duba koken da mukai mata na samun kura-kurai a sakamakon zaben da ya gudana, amma a yau 29 ga watan maris ta sake tabbatar da matsayar ta ta hanyar mikawa Abba Kabiru Yusuf Shaidar lashe zabe , don haka mun dauki wannan a matsayin kaddara”. Inji Gawuna


 
Yace dama ya fada a baya cewa zai karɓi Kaddara idan ya fadi zaben don haka yayi kira ga magoya bayan sa da dukkanin al’ummar jihar kano da zu baiwa sabon zaɓaɓɓen gwamnan hadin kai don ya gudanar da mulkin sa cikin kwanciyar hankali da lumana.

 
Mataimakin Gwamnan ya kuma yi addu’ar Allah ya kamawa Sabon zababben gwamnan, sannan yayin addu’ar Allah ya bashi ikon yiwa al’ummar jihar kano adalci a Shugabanci sa.
KADAURA24 


Tuesday, 3 January 2023

Tinubu ba zai ci amanar ’yan Arewa ba, ya dace ya yi mulki – Gwamna Badaru




Gwamnan Jihar Jigawa, Muhammadu Badaru Abubakar, ya karyata rade-radin da ake yi na cewa dan takarar Shugaban kasa na APC, Ahmad Bola Tinubu zai yi butulci ga Yan arewa idan ya ci zabe


Ya yi ikirarin cewa makusantan dan takarar shugaban kasa sun nuna shi ba maciya amana ba ne. Kuma sun tabbatar da shi a matsayin wanda ba mai kabilanci ba ne kuma mai kishin addini.”

Gwamnan jihar Jigawa ya kara da cewa duk abin da Bola Tinubu ya yi a burinsa na zama shugaban kasa, ya yi tare da cikakken masaniyarsa d Ganduje da Nuhu Ribadu, mutanen da suka yi fice wajen kishin kasa.


Muhammadu Badaru wanda ya  tuno kan yadda Malamai suka tursasa shi ya janye aniyarsa ta tsayawa takarar shugaban kasa a Kudu, ya ce zabin Bola Tinubu an yi shi ne da duk wani mai ruwa da tsaki a harkar Nijeriya.

“Magana game da lafiyar kwakwalwarsa da lafiyarsa, ziyarar da muka yi a Makka kwanan nan a Ummara inda Tinubu ya yi tafiya mai nisa ba tare da shiga mota ba da kuma yadda ya yi dawafi  da Sa'ayi ya nuna cewa ba shi da wata matsala ta rashin lafiya 

"Ya kamata 'yan Najeriya su sani cewa zamanin amfani da ra'ayi, kabilanci, da kishin addini ya kare, duk tattaunawa da zarge-zarge marasa tushe. ”
(Daily Post) 

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

FG Urges KOICA, FAO to Align Agricultural Intervention with Nigeria’s Development Priorities, Ward-Based Strategy

The Federal Government has called for stronger alignment between development partners’ interventions and Nigeria’s national deve...