Search This Blog

Showing posts with label Rarara. Show all posts
Showing posts with label Rarara. Show all posts

Monday, 13 November 2023

Kotu Ta Dage Shari'ar Rarara Kan Sukar Buhari

Wata Kotun Majistiri da ke zamanta a Lafiya, babban birnin Jihar Nassarawa, ta dage sauraron kara da aka shigar da mawakin siyasa, Dauda Kahutu wanda aka fi sani da Rarara, kan zarginsa da neman tunzura al’umma da kuma tayar da hankali.

Karar wanda wani mazaunin garin Mararraba da ke makotaka da Abuja mai suna Muhammad Sani Zangina ya shigar, ya danganta shi ne da wani jawabin taron ’yan jarida da ya ce mawakin ya shirya a Abuja, inda ya bayyana nadamar goyon bayansa ga tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buhari, tare da zarginsa da wargaza kasar kafin mika ta ga Shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu.

An sa zare tsakanin Rarara da mutanen Buhari
Sabuwar wakar Rarara ta sake yamutsa hazo
A takardar karar wadda wakilinmu ya samu gani, lauyan mai shigar da karar, Barista Muhammad Barde Abdullahi ya gabatar, ya ce zargin da ake yi wa Rararan da aikatawa, ya saba da doka ta 114 a Kundin Shari’a na penal code.

Sai dai a yayin zaman fara sauraron shari’ar a ranar Litinin 13 ga watan Nuwamba, an sanar da kotun cewa wanda ake zargin bai halarci zaman kotun ba.


Jami’in kotun da aka baiwa takardar gayyata don mikata ga wanda ake zargi, ya shaida wa kotun cewa dogaran mawakin ba su ba shi damar kaiwa gare shi ba, a lokacin da ya yi yunkurin hakan a mazauninsa da ke Abuja, bisa zargin suna cika umarnin uban gidansu ne.

Mai shari’a Maryam Nadabo ta amince da bukatar lauyan mai shigar da karar ta a gabatar da takardar gayyatar ta hanyar likata a jikin gidan mawakin, sannan ta dage ranar fara sauraron shari’ar zuwa 4 ga watan Disamba da ke tafe.

(AMINIYA)

Thursday, 26 October 2023

MARTANI GA MAWAKI DAUDA RARARA - Bashir Ahmad

Na kalli wani bangare na videon da yake yawo na taron manema labarai da mawaki Dauda Kahutu Rarara ya gabatar a yau, musamman bangarorin da ya ci wa tsohon Shugaban Kasa, Muhammadu Buhari mutunci tare da zargin cewa sai da ya rusa kasar baki daya kafin ya bar mulki. 

Bayan kammala kallon video na yi yunkurin bawa Rarara amsa daya bayan daya ga duk wadannan zarge - zargen da yayi, sai dai daga bisani da na sake yin nazari a tsanake sai na ga babu bukatar hakan a halkance da kuma mutunce, saboda wasu dalilai kwarara guda biyu.

Na farko, cikin videon, Rarara yayi ikirarin cewa wai gudunmawar daya bayar a tafiyar Buhari ko shi Buharin bai bawa kan sa irin wannnan gudunmawa ba. IKON ALLAH. Don Allah akwai hankali a cikin wannan magana? 

Sai dalili na biyu, inda yake cewa a wannan gwamnatin ta Shugaba Tinubu idan har ba a bashi mukamin minista ba, to ya kamata a ce an kira shi an zauna da shi an zabi wadanda za a bawa mukaman na ministoci. TASHIN HANKALI. Ko akwai chemistry, balle technology a cikin wannan batu? 

To gaskiya wanda maganganu da suka fita daga bakin mawakin ya sa na ga cewa tsayawa a bashi amsa a matakin hankali ma bata lokaci ne, domin kuwa wadannan maganganun na sa sun saba da kowane irin hankali da tunani, idan dai ba akwai rashin lafiya ba, to lalle akwai tsantsar jahilci. Babu hikima a cikin maganganun nasa ko kadan.

A kuma maganar da Rararan yayi da cewa wai a cikin shekaru bakwai na Baba Buhari ba a iya bin hanyar Abuja zuwa Kaduna, a zahirin gaskiya ba zan ce ba a samu matsalolin tsaro a hanyar ba, sai dai zan dan yi masa tuni da ya tuna baya a lokacin da Baba Buharin ya karbi mulki, ba ma maganar kidnapping ake yi a hanyar ba, Saboda matsalar da Boko Haram ta jefa yankin Arewa daga Abuja zuwa Kaduna sai an ci karo da shingen jami’an tsaro sama da goma, ba ma maganar daga Kaduna zuwa Kano ba, balle uwa uba, daga Kano zuwa Maiduguri. Duk wanda yake da hankali zai godewa Allah akan wannan.

Game da wakokin da yayi wa Baba Buhari, tunda Rarara yake yi masa waka, bai taba yi masa waka kyauta ba tare da an biya shi hakkin sa ba. 

A karshen magana daya da Rarara ya manta bai fada ba ita ce bai fito ya bayyanawa jama’a cewa Baba Buhari bai taimakon sa ba a rayuwarsa.

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

Head of Service Urges Civil Servants to Uphold Ethical Conduct

The Head of Service, Kano State, has called on civil servants to strictly adhere to the Civil Service ethical code and show grea...