Search This Blog

Showing posts with label Dantata. Show all posts
Showing posts with label Dantata. Show all posts

Saturday, 8 April 2023

Yanzu-Yanzu : Matar Alhaji Aminu Dantata, Ta Rasu

Matar hamshakin dan kasuwa na Kano, Alhaji Aminu Alasan Dantata, Hajiya Rabi ta rasu

Jaridar SOLACEBASE ta rawaito cewa, Hajiya Rabi, mahaifiya ga Tajuddeen Aminu Dantata, ta rasu ne a ranar Asabar. ta bar "yaya biyar 
Ta rasu ne sakamakon jinya da ta yi fama da ita 

Cikakken labarin zai zo muku nan gaba 

Tuesday, 27 December 2022

Na Daina Jin Dadin Rayuwa, Burina In Cika Da Imani Kawai – Aminu Dantata

 


Hamshakin  attajirin nan na Jihar Kano, Aminu Alhassan Dantata, ya ce daina jin dadin rayuwa, kuma ba shi da wani buri sama da cikawa da imani.

Attajirin ya bayyana haka ne a lokacin da ya karbi bakuncin Mataimakin Dan Takarar Shugaban Kasa a jam’iyyar APC, Kashim Shettima.

Ya ce ton tasowarsa, ya samu damar haduwa da mutane da dama, kuma ya kulla abota da jama’a a duka jihohin kasar nan.

Sai dai, ya ce a halin yanzu da walan gaske ya samu mutum 10 daga cikin abokan nasa da ke raye.

“Gaskiya a yadda nake yanzu, lokaci kawai nake jira. Ina fata in bar wannan duniya da imani.

“Ina fata ban saba wa kowa ba a rayuwa, idan kuwa hakan ta faru, ina fata za a yi mini afuwa, ni ma na yafe wa duk wani da ya saba mini.

“A zuri’armu n i kadai na rage, inda nake rayuwa a tsakanin jikoki,” inji Dantata.

Daga nan, ya yaba da ziyarar da aka kai masa, kana ya yi addu’ar samun dauwamammen zaman lafiya ga Nijeriya da al’ummarta.

Tun da farko, Sanata Kashim Shettima ya ce ya je Kano ne ziyarar tuntuba tare da ziyarar dattijon don neman tabarraki a wani bangare na yakin neman zabensu a 2023.

A cikin tawagar dai har da Gwamnan Kano, Abdullahi Umar Ganduje, kuma sun ziyarci dattawan jihar kamar su Alhaji Musa Gwadabe da Janar Lawal Jafaru Isah (mai ritaya) da Alhaji Tanko Yakasai a gidajen su.

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

FG Urges KOICA, FAO to Align Agricultural Intervention with Nigeria’s Development Priorities, Ward-Based Strategy

The Federal Government has called for stronger alignment between development partners’ interventions and Nigeria’s national deve...