Posts

Showing posts with the label Zangon Karatu Na 2024/2024/2025

Zangon Karatu Na 2024/2025: Gwamnatin Kano Ta Sauya Ranar Komawa Makaranta

Image
Gwamnatin jihar Kano ta mayar da ranar da za a ci gaba da bude makarantun firamare da na gaba da firamare na gwamnati zuwa ranar Talata 17 ga Satumba, 2024. Yayin da dalibai na makarantun kwana a fadin jihar za su koma ranar Litinin 16 ga Satumba, 2024.  Wata sanarwa da daraktan wayar da kan jama’a na ma’aikatar ilimi ta jihar, Balarabe Abdullahi Kiru ya sanya wa hannu, ta ruwaito kwamishinan ilimi na jihar Alhaji Umar Haruna Doguwa yana bayyana cewa hakan ya biyo bayan ayyana ranar 16 ga watan Satumba, 2024 a matsayin ranar hutu domin bikin Mauludi. “Saboda haka an yi gyara ne domin baiwa dalibai damar gudanar da bukukuwan wannan rana mai alfarma da ke nuna maulidin fiyayyen halitta Annabi Muhammad (SAW). “A yayin da nake taya al’ummar musulmi murna, ina kira gare su da su rungumi dabi’ar hakuri, sadaukarwa, da kishin kasa, su ci gaba da yi wa kasa  addu’a ga kasa baki daya,” inji shi. Don haka sanarwar ta bukaci iyaye/masu kula da daliban da su lura da sabuwar ranar da za