Search This Blog
Monday, 14 August 2023
Sojojin Nijar Za Su Gurfanar Da Bazoum Kan Zargin Cin Amanar Ƙasa
Welcome to Alheekmah News Alheekmah News is a Nigerian digital news platform committed to delivering timely, accurate, and credible news to readers across Nigeria and beyond. We provide comprehensive coverage of national affairs, politics, governance, Hajj and Umrah, religion, education, business, security, health, and other issues that shape our society. Our mission is to inform, educate, and inspire through responsible journalism founded on accuracy, fairness, and integrity. We strive to provide factual reporting while promoting public awareness and constructive engagement. At Alheekmah News, we believe that reliable information empowers individuals and strengthens communities. We are dedicated to bringing you breaking news, in-depth reports, exclusive interviews, and insightful analysis you can trust. Stay informed. Stay connected. Stay ahead with Alheekmah News.
Wednesday, 12 April 2023
Majalisar Najeriya ta gayyaci ministoci kan bacewar gangunan danyen mai
Kwamitin Majalisar Wakilan Najeriya da ke bincike kan zargin batar gangar danyen mai miliyan 48 a kasar ya gayyaci Ministocin Kudi da na Shari'a da wasu manyan shugabannin hukumomin kasar domin bayar da bahasi a game da wannan badakalar.
Da yake magana kan rashin girmama gayyatar da kwamitin ta ya yi wa Ministocin Kudi da na Shari'a da wasu jami'an hukumomin gwamnatin kasar, Shugaban Kwamitin Binciken Hon. Mark Gbillah, ya ce ana zargin Ministar Kudi Zainab Ahmed da karya dokar gwamnati ta tsarin fallasa masu yi wa gwamnati zagon kasa ta hanyar kin biyan masu fallasawar adadin kudin da ya dace a ba su.
Tun a watan Disamban shekarar da ta gabata ne Majalisar ta yanke shawarar fara bincike kan bantan miliyoyin gangar man, wadanda ake zargin wasu manyan jami'an gwamnatin kasar da karkatarwa zuwa China.
Ya ce a daya bangaren kuma, ana zargin Ministan Shari'a na kasar da karbar kudade daga ketare ba tare da sanyawa cikin asusun gwamnati ba.
Ya kuma bayyana cewa, kwamitin na da bayanan sirri na wasu ma’aikatu da hukumomin gwamnati da ba su bin ka'idar amfani da tsarin asusun ajiyar kudi na bai-daya.
Sai dai bai bayyana ranar da jami'an gwamnatin za su bayyana a gaban kwamitin domin amsa tambayoyi ba.
RFI
Welcome to Alheekmah News Alheekmah News is a Nigerian digital news platform committed to delivering timely, accurate, and credible news to readers across Nigeria and beyond. We provide comprehensive coverage of national affairs, politics, governance, Hajj and Umrah, religion, education, business, security, health, and other issues that shape our society. Our mission is to inform, educate, and inspire through responsible journalism founded on accuracy, fairness, and integrity. We strive to provide factual reporting while promoting public awareness and constructive engagement. At Alheekmah News, we believe that reliable information empowers individuals and strengthens communities. We are dedicated to bringing you breaking news, in-depth reports, exclusive interviews, and insightful analysis you can trust. Stay informed. Stay connected. Stay ahead with Alheekmah News.
Thursday, 16 March 2023
DSS ta kama mutum biyu a Kano kan zargin tayar da rikici
Hukumar tsaro ta farin kaya DSS ta ce ta kama wasu mutane biyu da take zargi da tunzura mutane domin tayar da hankali a jihar Kano gabanin zaɓen gwamna da na ‘yan majalisun jiha da za a yi a ranar Asabar.
Cikin wata sanarwa da ta
wallafa a shafinta na Twitter hukumar ta DSS ta ce mutanen sun naɗi hoton
bidiyo ne da suke bayanan tunzura jama’a a cikinsu, sannan suka riƙa wallafa
shi a shafukan sada zumunta.
Ta kuma wallafa sunayen
Sharu Abubakar Taɓule mai shekara 37 a duniya, da kuma Isma’il Iliyasu Mnagu
mai shekara 51 a matsayin waɗanda ta kama.
“Cikin waɗannan saƙonnin
masu haɗari, sun nuna jam’iyyar siyasar da suke goyon baya kuma suka yi kira ga
magoya bayansu su kai wa abokan hamayyarsu hari duk inda suka gansu.
“Wata jam’iyyar siyasa a Kano na barazanar shirya zanga-zanga a sakamakon shirin kai hare-haren,” in ji hukumar ta DSS.
Sanarwar ta ƙara da cewa jam’iyyar siyasar ta shirya kutsawa ofisoshin wasu hukumomin tsaro a ranar 16 ga watan Maris a matsayin nuna goyon baya ga waɗanda ake zargin.“Yayin da hukumar ke sanar da mutane kan wannan haramtaccen mataki, ta kuma yi kira ga jam’iyyar da ta dakatar da wannan lamari, ko kuma ta shirya yaba wa aya zaƙinta.
“DSS ba za ta zuba ido tana kallon mutane suna tunzura al’umma ba su tayar da hankali da rashin tsaro a jiha ba.”
Sanarwar DSS ta ce za ta haɗa hannu da sauran hukumomin tsaro domin tabbatar da an samar da cikakken tsaron da zai bayar da damar da gudanar da zaɓe mai inganci a jihar.
Baya ga Kano hukumar tsaron ta kama wasu mutane da ke irin wannan kiraye-kiraye a wasu jihohi a faɗin ƙasar.
Hukumar ta shawarci jam’iyyun siyasa a fadin Najeriya da su gargadi mabiyansu su zama masu bin doka da oda, domin tabbatar da dimokuraɗiyya ta samu wurin zama yadda ya kamata
BBC
Welcome to Alheekmah News Alheekmah News is a Nigerian digital news platform committed to delivering timely, accurate, and credible news to readers across Nigeria and beyond. We provide comprehensive coverage of national affairs, politics, governance, Hajj and Umrah, religion, education, business, security, health, and other issues that shape our society. Our mission is to inform, educate, and inspire through responsible journalism founded on accuracy, fairness, and integrity. We strive to provide factual reporting while promoting public awareness and constructive engagement. At Alheekmah News, we believe that reliable information empowers individuals and strengthens communities. We are dedicated to bringing you breaking news, in-depth reports, exclusive interviews, and insightful analysis you can trust. Stay informed. Stay connected. Stay ahead with Alheekmah News.
Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa
FG Urges KOICA, FAO to Align Agricultural Intervention with Nigeria’s Development Priorities, Ward-Based Strategy
The Federal Government has called for stronger alignment between development partners’ interventions and Nigeria’s national deve...
-
Gwamnan Babban Bankin Najeriya, Godwin Emefiele, ya ce Bankuna za su ci gaba da karbar tsoffin takardun kudi na Naira ko da baya...
-
Matar hamshakin dan kasuwa na Kano, Alhaji Aminu Alasan Dantata, Hajiya Rabi ta rasu Jaridar SOLACEBASE ta rawaito cewa, Hajiya ...
-
Zababben Gwamnan Jihar Kano Ya Sanar Da Kwamitin Karbar Mulki …… Dr. Baffa Bichi, Abdullahi Musa ya nada a matsayin Shugaba da Sakatare Baya...

