Posts

Showing posts with the label Mamaye

Hukumar DSS Ta Musunta Mamaye ofishin Gwaman Babban Bankin Najeriya

Image
Hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) ta musanta mamaye harabar babban bankin Najeriya, a ranar Litinin, kamar yadda ake yada labarin a yanar gizo. Rundunar ‘yan sandan sirrin a cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na hukumar tsaron ta farin kaya, Peter Afunanya ya fitar ta ce labarin karya ne. Idan dai za a iya tunawa a ranar Litinin din da ta gabata ne aka ga motocin a harabar babban bankin da ke Abuja. Hukumar ta DSS a cikin sanarwar ta ce jami’anta ba su yi yunkurin kama gwamnan na CBN ba.

LABARI DA DUMIDUMINSA! Jami’an Hukumar I DSS Sun Mamaye ofishin Gwaman Babban Bankin Najeriya

Image
Jami’an hukumar tsaro ta farin kaya, SSS, sun mamaye hedikwatar babban bankin Najeriya CBN, inda suka karbe ofishin gwamnan babban bankin, Godwin Emefiele. Jaridar DAILY NIGERIAN ta rawaito cewa an yi artabu tsakanin jami’an SSS da Mista Emefiele kan zargin bada tallafin yaki da ta’addanci. A baya dai hukumar leken asirin ta nemi kotu ta kama Mista Emefiele amma ya fita kasar domin hutun shekara da zai kare a gobe 17 ga watan Janairu. Sai dai a watan Disamba ne babbar kotun birnin tarayya ta haramtawa SSS kama, gayyata, ko kuma tsare Mista Emefiele. Jami’an SSS da suka isa hedikwatar CBN a ranar Litinin da ta gabata, sun shigo da motoci kusan 20 dauke da jami’an tsaro. Jami’an sun kuma hana duk ma’aikatan bankin shiga ofishin Mista Emefiele. Peter Afunanya, mai magana da yawun SSS, har yanzu bai amsa tambayar da dan jaridan ya aike masa ba. Cikakkun bayanai daga baya…