Posts

Showing posts with the label Saudia

Gwamna Abba Kabir Ya Yi Bankwana Da Tagwayen Da suka hade Da Za Ayi Tiyatar Rabasu A Saudiyya

Image
....Ya yabawa Masarautar Saudiya bisa kara kaimin agaji ga Kano Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya yabawa masarautar Saudiyya karkashin jagorancin Sarki Salman Bin Abdul'aziz kan daukar nauyin yi wa jarirai tagwaye a Kano tiyata a wani asibiti da ke kasar Saudiyya a birnin Riyadh. Da yake jawabi a lokacin da yake bankwana da iyayen tagwayen jarirai a filin jirgin sama na Aminu Kano, gwamnan ya bayyana irin alherin da Sarki Salman ya yi a matsayin wani aiki da Allah ya saka masa da ya dace a yi koyi da shi. Gwamna Yusuf wanda ya yi addu’ar Allah ya dore da dankon zumuncin da ke tsakanin Kano da Masarautar Saudiyya, ya bayyana cewa gwamnati ba za ta yi kasa a gwiwa ba a kokarinta na dawo da martabar da aka rasa a bangaren kiwon lafiya na jihar. A sanarwar da babban sakataren yada labaran Gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa ya sanyawa hannu, yace Gwamnan ya tuna cewa ba da dadewa ba Likitocin Saudiyya suna Asibitin Koyarwa na Aminu Kano, domin kula da marasa la

Hukumar Kula da Yanayi ta Kasar Saudiyya ta ce, yanayin zafi a gobe Juma’a, zai kai daraja Hamsin na tsananin Zafi.

Image
Saboda wannan zafin yanayin, Gwamnatin Saudiyya na bada shawarar cewa Alhazai da suyi Sallar Jumma’ah a Masallatan da suka fi kusa da gidajensu don kaucewa shiga tsananin rana.  Don haka Ma’aikatar Aikin Hajji ta Kasar Najeriya na kara jaddada ayi anfani da wannan nasihar ta yin Salla a Masallatai Mafiya kusa da Masaukan Alhazanmu. Sanarwar wacce babban jami'in hukumar NAHCON dake Makkah, Dr Ibrahim Muhammad Sodangi ya sanyawa hannu, ta yi fatan Alhazan zasu yi amfani da wannan shawara ta kwararru da aka domin kaucewa shiga babbar matsala