Posts

Showing posts with the label Sabbin mukamai

Yanzu-yanzu: Gwamna Abba Kabir Yusuf ya yi sabbin nade-naden mukamai

Image
A kokarinsa na kara baiwa jihar Kano karfin gwiwa, Gwamna Abba Kabir Yusuf ya amince da nada karin masu ba da shawara na musamman da sauran shugabannin hukumomin gwamnati. A wata sanarwa da Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar, mai magana da yawun gwamnan ya yi ishara da wadanda aka nada kamar haka: 1. Farfesa Ibrahim Magaji Barde, mai ba da shawara na musamman kan harkokin tattara kudaden shiga (IGR). 2. Dr. Abdulhamid Danladi, mai ba da shawara na musamman kan harkokin kasashen waje II 3. Injiniya Bello Muhammad Kiru, mai ba da shawara na musamman kan albarkatun ruwa. 4. Yusuf Shuaibu Imam (Ogan Boye) ya sake nada shi a matsayin mai ba da shawara na musamman kan harkokin matasa da wasanni. 5. Dr. Nura Jafar Shanono an dauke shi daga mai ba da shawara na musamman kan albarkatun ruwa zuwa Manajan Darakta, Injiniyan Ruwa da Gine-gine (WRECA). 6. Hon. Haka kuma Baba Abubakar Umar an dauke shi ne daga mai ba shi shawara na musamman ga babban sakataren gudanarwa, hukumar kula da

Yanzu-yanzu: Gwamnan Kano ya yi sabbin nade-naden mukaman shugabannin ma'aikatun gwamnati

Image
A bisa kokarin sanya hannun da suka dace don inganta shugabanci na gari, Gwamna Abba Kabir Yusuf ya amince da nadin shugabannin hukumomin na jihar nan take. A sanarwar da babban sakataren yada labaran Gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya sanyawa hannu, yace Wadanda aka nada sune kamar haka. 1. Salisu A. Kabo, Darakta Janar na hukumar Kula da ci gaban matasa 2. Dr. Hamisu Sadi Ali, Darakta Janar na ofishin kula da basussuka 3. Abduljabbar Mohammed Umar, Darakta Janar na KAN-INVEST 4. Yusuf Kabir Gaya, Shugaban Hukumar SUBEB 5. Mustapha Adamu Indabawa, Manajan Daraktan Gidan Talabijin na Abubakar Rimi (ARTV) 6. Hamisu Dogon Nama, Manajan Daraktan Kasuwar Kantin Kwari 7. Abdulkadir B. Hussain, Manajan Daraktan Kasuwar Sabon Gari 8. Dr Kabiru Sani Magashi, Mukaddashin Manajin Darakta na KASCO 9. Aminu Aminu Mai-Famfo, Mataimakin Manajin Darakta na KASCO 10. Engr, Abubakar Sadiq J. Mataimakin Manajin Darakta Hukumar sufuri ta  Kano Line Gwamnan ya umarci wadanda aka nada da su