Search This Blog

Showing posts with label Farfesa Mahmoud Yakubu. Show all posts
Showing posts with label Farfesa Mahmoud Yakubu. Show all posts

Tuesday, 17 January 2023

A shirye muke don zuwa zagaye na biyu a zaɓen shugaban ƙasa - Shugaban INEC

Shugaban Hukumar Zaɓe mai zaman ƙanta a Najeriya Farfesa Mahmood Yakubu ya ce hukumarsa a shirye take game da zuwa zaɓen zagaye na biyu na shugaban ƙasar idan har ba a samu wanda ya yi nasara a zagayen farko ba.

Farfesa Yakubu ya bayyana hakan ne a lokacin da yake jawabi kan shirye-shiryen hukumar na tunkarar babban zaɓen ƙasar da ke tafe a Chatham House da ke birnin Landan a Birtaniya.

Ya ƙara da cewa a INEC ta yi shirin yiyuwar zuwa zagaye na biyu a zaɓen shugaban ƙasar, kamar yadda take yi a zaɓuka uku da suka gabata.

Shugaban hukumar zaɓe ya kuma ce zaɓen ƙasar da za gudanar cikin wannan shekara zaɓe ne na matasan ƙasar.

Farfesa Yakubu ya kuma ce rajistar masu kaɗa ƙuri'a ta nuna cewa matasa ne suka mamaye adadi mafi yawa na masu rajistar zaɓen.

Shugaban Hukumar ya ce ya ji daɗin yadda mutane suka fito domin karɓar katinan zaɓensu, yana mai cewa fiye da mutum 600,000 sun karɓi katinansu a jihar Legas kaɗai cikin watan da ya gabata.

Ya ƙara da cewa a yanzu adadin masu rajistar zaɓe a Najeriya sun kai miliyan 93.4, kuma daga ciki miliyan 37 wato kashi 39 na rajistar zaɓen matasa ne 'yan tsakanin shekara 19 zuwa 34.

Ya kuma tunasar da maharta taron cewa hukumar za ta tsayar da rabar da katin zaɓen daga ranar 29 ga watan Janairun da muke ciki.
(BBC HAUSA) 


Friday, 6 January 2023

Bamu kai Karar Shugaban INEC Kotu ba - DSS

Hukumar Tsaro ta Farin Kaya (DSS) ta musanta labarin da ke yawo cewa tana cikin hukumomin tsaron da suka maka Shugaban Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) Farfesa Mahmood Yakubu a kotu.

Kakakin rundunar, Peter Afunanya ne ya bayyana hakan a ganawarsa da manema labarai, inda ya yi karin haske kan umarnin wata Babbar Kotun Abuja na hana hukumomin tsaro ciki har da DSS din kama Yakubu.

Boka ya mutu yana lalata da matar fasto
Mun gano wadannin macizai a dajin Ecuador —Masana
A ranar Laraba ce dai Alkalin Kotun, M. A. Hassan ya ki amincewa da bukatar tsige shugaban INEC din daga mukaminsa, saboda zargin kin bayyana ainihin kadarorin da ya mallaka.

Alkalin ya ce kadarorin da Yakubun ya bayyana haka suke, kuma sun yi daidai da tanadin dokokin Najeriya.

Hukuncin dai ya biyo bayan karar da Somadina Uzoabaka ta shigar da Babban Lauyan Gwamnatin da Farfesa Yakubu mai lamba FCT/HC/GAR/CV/47/2022 don tilasta wa shugaban hukumar ta INEC sauka daga matsayinsa, har sai an gudanar da binciken wasu zarge-zargen da hukumomin tsaro daban-daban ke yi masa.
Sai dai Afunanya ya ce kwata-kwata DSS ba ta cikin hukumomin tsaron da suka shigar da waccan karar.

“DSS na sane da yadda wasu miyagu ke son tayar da rikici a kasar nan, gami da haifar da cece-kuce game da babban zabe mai zuwa.

“Kuma wannan na daya daga cikin dabarun su na yin zagon kasa da lalata kokarinmu na tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a Najeriya.


“Don haka ina amfani da wannan dama, don wanke DSS da kuma fahimtar da al’umma cewa, ba gaskiya ba ne cewa mun kai karar shugaban INEC kotu”, in ji Kakakin.

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

FG Urges KOICA, FAO to Align Agricultural Intervention with Nigeria’s Development Priorities, Ward-Based Strategy

The Federal Government has called for stronger alignment between development partners’ interventions and Nigeria’s national deve...