Search This Blog

Showing posts with label Hukumar Zabe Mai zaman kanta. Show all posts
Showing posts with label Hukumar Zabe Mai zaman kanta. Show all posts

Tuesday, 18 April 2023

INEC Ta Bayyana Gwamna Ahmadu Fintiri A Matsayin Wanda Ya Lashe Zaben Gwamnan Jahar Adamawa

Hukumar zaɓe a Najeriya ta sanar da Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri a matsayin wanda ya lashe zaɓen jihar Adamawa, wanda ya ƙare cikin taƙaddama.

Jami'in sanar da sakamakon zaɓen gwamna na Adamawa, Farfesa Mohammed Mele ya ce Ahmadu Fintiri ya yi nasarar lashe zaɓen ne da ƙuri'a, 430, 861.

Gwamnan mai ci ya samu nasara a kan babbar abokiyar fafatawarsa Aisha Ɗahiru Binani wadda ta samu ƙuri'a, 398, 788.

Wannan nasara ta bai wa Fintiri ikon ci gaba da mulkin jihar Adamawa a wa'adi na biyu.

Da yammacin Talata ne, jami'in sanar da sakamako, Farfesa Mohammed Mele cikin rakiyar wasu manyan jami'an INEC na ƙasa, ya isa zauren karɓar sakamako da ke Yola, inda ya ci gaba da aikin tattara sakamakon ƙananan hukumomin da suka rage.

A ranar 15 ga watan Afrilu ne, hukumar zaɓe ta gudanar da cikon zaɓen cikin wasu rumfuna da ke faɗin ƙananan hukumomin jihar 20.

An sake kaɗa ƙuri'u ne a tashoshin zaɓe 69.

Sakamakon zaɓen da aka ƙarasa ya nuna cewa 'yar takarar jam'iyyar APC, Aisha Binani ta samu ƙuri'a 6,513, yayin da Gwamna Fintiri na PDP ya samu 9,337.

Zaɓen dai ya gamu da taƙaddama bayan kwamishinan zaɓe na jihar Adamawa Hudu Ari ya sanar da Aisha Binani a matsayin wadda ta lashe zaɓen ba tare da ya fayyace sakamakon kowacce jam'iyya dalla-dalla ba.


ne a Yola tare da rakiyar 'yan sanda da safiyar Lahadi, inda ya ayyana Sanata Aishatu Binani ta APC a matsayin wadda ta lashe zaɓen.

Bai dai yi bayani filla-filla na sakamakon da kowacce jam'iyya ta samu, da kuma yadda aka yi Aisha Binani ta ci zaɓen ba.

Sai dai cikin wata sanarwa da babban jami'inta kan yaɗa labarai da wayar da kan masu zaɓe na ƙasa, Barista Festus Okoye ya fitar, INEC ta ce matakin da kwamishinan zaɓe na jihar Adamawa - REC ya ɗauka na sanar da wanda ya lashe zaɓe haramtacce ne, don haka ta ce ba za a yi amfani da shi ba.

INEC ta kuma ce Hudu Ari ya sanar da sakamakon ne a lokacin da ba a riga an kammala aikin tattara sakamakon zaɓen ba.

Lamarin dai ya janyo ruɗani a Najeriya, inda a Adamawa 'ya'yan jam'iyyar PDP suka shiga gudanar da zanga-zanga don matsa lamba ga hukumar zaɓe ta kammala aikin sanar da sakamako.

A zaɓen ranar 18 ga watan Maris, INEC ta bayyana gwamna mai ci Ahmadu Umar Fintiri da cewa ya samu ƙuri'a 421,524.

Sai babbar abokiyar fafatawarsa ta jam'iyyar APC, Sanata Aisha Dahiru Binani wadda ta samu ƙuri'a 390,275.

Ita ce mace ta farko da ta taɓa zuwa wannan mataki na zaɓen da aka ƙarasa a takarar gwamna, tun bayan komawar Najeriya mulkin dimokraɗiyya a 1999.


Tuni dai aka ga wasu magoya bayan gwamnan a kan tituna suna shagulgulan nasarar da Gwamna Ahmadu Fintiri ya samu.
BBC 

Wednesday, 8 March 2023

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) za ta gudanar da zabe karo Na Biyu A mazabar Doguwa Da Tudun Wada

Jami’in zaben mazabar tarayya da aka gudanar a ranar 25 ga watan Fabrairu, Farfesa Ibrahim Adamu Yakasai, a ranar Laraba ya sanar da sakamakon sake duba sakamakon zaben da aka gudanar a mazabar Doguwa/Tudun Wada na tarayya ya ce hukumar ta sake duba sakamakon farko da ake zargin sa ya bayyana a karkashinsa. tilastawa.
Ya kara da cewa INEC bisa ga tanade-tanaden dokar zabe ta sake duba sakamakon.

Da yake sanar da sakamakon da aka sake duba, Farfesa Ibrahim ya bayyana cewa sakamakon zaben da aka duba ya zo kamar haka, APC 39,732, NNPP 34, 798, PDP 7,091.
A cewarsa, an soke sakamakon zabe a rumfunan zabe 13.

Ya ce jimillar kuri’un mazabar da aka soke a rumfunan zabe da aka soke sun yi wa jam’iyyar APC da NNPP tazarar kuri’u.

Ya bayyana cewa adadin kuri’u da aka tattara a rumfunan zabe 13 da aka soke sun kai 6,917 sabanin kuri’u sama da 4000 da ke tsakanin APC da NNPP.

Ya ce INEC za ta gudanar da karin zabuka a sassan da abin ya shafa domin tantance wanda ya lashe zaben mazabar tarayya na Doguwa/Tudun Wada a ranar 25 ga watan Fabrairu.

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

FG Urges KOICA, FAO to Align Agricultural Intervention with Nigeria’s Development Priorities, Ward-Based Strategy

The Federal Government has called for stronger alignment between development partners’ interventions and Nigeria’s national deve...