Posts

Showing posts with the label Ta'aziyya

Gwamna Abba Kabir Yayi Ta'aziyyar Rasuwar Marigayi Dr. Faizu Baffa Yola

Image
Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir ya bayyana kaduwarsa bisa rasuwar Dakta Faizu Baffa Yola wanda ya rasu a yau (Alhamis) sakamakon rashin lafiya da ya yi yana da shekaru 74 a duniya. Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya rabawa manema labarai. Gwamna Abba Kabir Yusuf ya bayyana a cikin wani yanayi na alhini game da gudunmawar da Marigayi Dokta Faizu Baffa Yola ya bayar wajen ci gaban harkokin kiwon lafiya a jihar da kuma wajensa da kuma yadda yake taimakawa bil’adama a kowane lokaci. “Mun samu matukar kaduwa da labarin rasuwar Dr. Faizu Baffa Yola, wani kwararren likita wanda ya shafe tsawon rayuwarsa yana hidima ga al'uma a fannin kula da lafiya da sauran ayyukan jin kai. “Abubuwan alkhairin da ya yi ba zai gushe ba saboda gudunmuwar da ya bayar a ci gaban jihar da kasa baki daya ba za a iya mantawa da shi cikin sauki ba kuma zai zama jagora ga masu son bin tafarki madaidaici. “A madadin gwamnati da na

Alhajin Kano Dake Jinya A Makkah Ya Rasu

Image
Daraktan Janar na Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kano Alh Laminu Rabi’u Danbappa ne ya bayyana hakan ne a karamar hukumar Gaya yayin da ya jagoranci tawagar shugabannin hukumar domin sanarwa iyalansa tare da yi musu ta'aziyya  A sanarwar da Jami'in hulda da jama'a na hukumar, Sulaiman Abdullahi Dederi ya sanyawa hannu, Laminu Rabi'u Danbappa, ya kara da cewa, cike da bakin ciki muke sanar da rasuwar Alh Umar Hamza daya daga cikin alhazan mu da ya rage a Asibitin Saudiyya. Umar Hamza, mai shekaru 75 ya rasu ne a Asibitin Saudiyya a jiya bayan gajeruwar jinya, kamar yadda Hukumar Kula da Asibitin Saudiyya ta tabbatar. Laminu Danbappa, wanda ya bayyana alhinin rasuwar Alh Umar Hamza, ya bayyana marigayin a matsayin malamin islamiyya, yana jajantawa 'yan uwa akan wannan rashi. Daraktan Janar din a madadin gudanarwar hukumar, ya mika ta’aziyyarsa ga Jafar Umar Hamza, dan marigayin, da sauran ‘yan uwa da suka rasu, da kuma daukacin al’ummar Musulmi. Laminu

Darakta Janar Na Hukumar Alhazai Ta Kano Yayi Ta'aziyya Ga Jami'in Alhazai Na Karamar Hukumar Bichi

Image
Daga Faruk Musa Sani Galadanchi Darakta Janar na Hukumar kula da jin dadin Alhazai ta Jahar Kano, Alhaji Laminu Rabi'u Danbaffa, ya bayyana rasuwar Maddassir Habib Idris a matsayin babban rashi. Alhaji Laminu Rabi'u Danbaffa ya bayyana hakan ne lokacin da ya jagoranci tawaga domin yin ta'aziyya ga mahaifin mamacin wanda kuma ya kasance jami''in Alhazai na Karamar Hukumar Bichi, Malam Habib Idris Bichi Laminu ya bayyana marigayi Mudassir a matsayin matashin Jami''in Hukumar tsaro ta farin kaya mai da'a wanda yake jajircewa da aiki tukuru wajen gudanar da aikinsa wanda ya rasa rayuwarsa sakamakon harin da yan bindiga suka kai musu suna tsakiyar gudanar da aikinsu a Jahar Kaduna Darakta janar din yace rasuwar Maddassir ta bar Babban gibi ga iyalan Malam Habib Idris Bichi da ma daukacin al'umar jahar Kano baki daya Don haka Alhaji Laminu Rabi'u a madadin Shugaban Hukumar da ma'aikata yayi addu'ar Allah ya g

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yi ta'aziyya ga iyalan marigayi Sheikh Giro

Image
Shugaban kasa, Bola Tinubu ya yi ta’aziyya ga iyalai, mabiya, da kuma makusantan fitaccen malamin addinin Islama, Sheikh Abubakar Giro Argungu, wanda ya rasu a ranar Laraba. A wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Ajuri Ngelale ya fitar a ranar Alhamis, shugaban ya bayyana rasuwar shugaban addinin a matsayin rashi da ya wuce sauran al’ummar marigayi wa’azi da kuma abin da ya shafi kasar baki daya, duba da irin gudunmawar da ya bayar ga kundin tsarin mulkin kasar. Karatun Musulunci da shahararriyarsa yana kira zuwa ga gyara tarbiyya. “Za a dade ana tunawa da Muryar Sheikh Giro Argungu a tsawon shekarun da ya yi na yada addinin Musulunci da kuma fafutukar tabbatar da adalci. “Ayyukan da malamin ya yi ta hanyar kungiyar Musulunci, JIBWIS, inda ya taba rike mukamin Shugaban Kwamitin Ayyuka, ya ba da gudunmawa matuka wajen jagorantar dimbin matasan Musulmi a tsawon shekaru,” in ji shi. Mista Tinubu ya kara da cewa, za a yi kewar marigayi malamin saboda rashin tsoro da jajircewa

LABARI CIKIN HOTUNA : Abdulmumin Jibrin Kofa ya kai ziyarar ta'ziyya ga al'umomi daban-daban

Image
Dan takakarar majalisar tarayya na mazabar Kiru da Bebeji a jam’iyyar #NNPP, Abdulmumin Jibrin Kofa, ya kai ziyarar ta'ziyya da dubiyar marasa lafiya ga Unguwanni da garuruwa daban-daban dake yankin Kiru da Bebeji